Yohanna 2 – HCB & KJV

Hausa Contemporary Bible

Yohanna 2:1-25

Yesu ya mai da ruwa ya zama ruwan inabi

1A rana ta uku sai aka yi bikin aure a Kana ta Galili. Mahaifiyar Yesu kuwa tana can, 2aka gayyaci Yesu da almajiransa su ma a auren. 3Da ruwan inabi ya ƙare, sai mahaifiyar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.”

4Yesu ya ce, “Mace, me ya sa kike haɗa ni a wannan? Lokacina bai yi ba tukuna.”

5Sai mahaifiyarsa ta ce wa bayin, “Ku yi duk abin da ya faɗa.”

6Nan kusa kuwa akwai tulunan ruwa shida na dutse a ajiye, irin da Yahudawa suke amfani da su don tsarkakewa bisa ga al’ada, kowace kan ci gallon kusan ashirin zuwa talatin.

7Sai Yesu ya ce wa bayin, “Ku ciccika tulunan da ruwa.” Suka kuwa ciccika su fal.

8Sa’an nan ya ce musu, “Yanzu ku ɗiba ku kai wa uban bikin.”

Suka yi haka. 9Uban bikin kuwa ya ɗanɗana ruwan da aka juya ya zama ruwan inabi. Bai san daga ina ya fito ba, ko da yake bayin da suka ɗiba ruwan sun sani. Sai ya kira angon waje ɗaya 10ya ce, “Kowa yakan kawo ruwan inabi mafi kyau da fari, sa’an nan marar kyan bayan baƙin sun sha da yawa; amma ka ajiye ruwan inabi mafi kyau sai yanzu.”

11Wannan shi ne na fari cikin abubuwan banmamakin da Yesu ya yi a Kana ta Galili. Ta haka ya bayyana ɗaukakarsa, almajiransa kuwa suka ba da gaskiya gare shi.

Yesu ya tsabtacce haikali

12Bayan wannan sai ya tafi Kafarnahum tare da mahaifiyarsa da ’yan’uwansa da kuma almajiransa. A can suka zauna ’yan kwanaki.

(Mattiyu 21.12,13; Markus 11.15-17; Luka 19.45,46)

13Da lokacin Bikin Ƙetarewa na Yahudawa ya yi kusa, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima. 14A filin haikali ya sami mutane suna sayar da shanu, tumaki da tattabaru, waɗansu kuma zaune a tebur suna canjin kuɗi. 15Saboda haka ya tuƙa bulala ta igiyoyi, ya kori duka daga filin haikali, har da tumaki da shanu; ya watsar da kuɗin masu canjin, ya birkice teburansu. 16Ga masu sayar da tattabaru kuwa ya ce, “Ku kwashe waɗannan daga nan! Don me za ku mai da gidan Ubana kasuwa!” 17Sai almajiransa suka tuna cewa a rubuce yake, “Himma saboda gidanka zai cinye ni.”2.17 Zab 69.9

18Sai Yahudawa suka tambaye shi, “Wace abar banmamaki za ka nuna mana ka tabbatar mana ikonka na yin duk waɗannan?”

19Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku rushe wannan haikali, zan kuwa sāke tā da shi cikin kwana uku.”

20Yahudawa suka ce, “Sai fa da aka shekara arba’in da shida ana ginin haikalin nan, kai kuwa a cikin kwana uku za ka tā da shi?” 21Amma haikalin da ya yi magana jikinsa ne. 22Bayan da ya tashi daga matattu, sai almajiransa suka tuna da abin da ya faɗa. Sa’an nan suka gaskata Nassi da kuma kalmomin da Yesu ya yi.

23To, yayinda yake a Urushalima a Bikin Ƙetarewa, mutane da yawa suka ga abubuwan banmamakin da yake aikata suka kuma gaskata da sunansa. 24Sai dai Yesu bai amince da su ba, don ya san dukan mutane. 25Ba ya bukatar shaidar mutum game da mutum, don yă san abin da yake cikin zuciyar mutum.

King James Version

John 2:1-25

1And the third day there was a marriage in Cana of Galilee; and the mother of Jesus was there: 2And both Jesus was called, and his disciples, to the marriage. 3And when they wanted wine, the mother of Jesus saith unto him, They have no wine. 4Jesus saith unto her, Woman, what have I to do with thee? mine hour is not yet come. 5His mother saith unto the servants, Whatsoever he saith unto you, do it. 6And there were set there six waterpots of stone, after the manner of the purifying of the Jews, containing two or three firkins apiece. 7Jesus saith unto them, Fill the waterpots with water. And they filled them up to the brim. 8And he saith unto them, Draw out now, and bear unto the governor of the feast. And they bare it. 9When the ruler of the feast had tasted the water that was made wine, and knew not whence it was: (but the servants which drew the water knew;) the governor of the feast called the bridegroom, 10And saith unto him, Every man at the beginning doth set forth good wine; and when men have well drunk, then that which is worse: but thou hast kept the good wine until now. 11This beginning of miracles did Jesus in Cana of Galilee, and manifested forth his glory; and his disciples believed on him.

12¶ After this he went down to Capernaum, he, and his mother, and his brethren, and his disciples: and they continued there not many days.

13¶ And the Jews’ passover was at hand, and Jesus went up to Jerusalem, 14And found in the temple those that sold oxen and sheep and doves, and the changers of money sitting: 15And when he had made a scourge of small cords, he drove them all out of the temple, and the sheep, and the oxen; and poured out the changers’ money, and overthrew the tables; 16And said unto them that sold doves, Take these things hence; make not my Father’s house an house of merchandise. 17And his disciples remembered that it was written, The zeal of thine house hath eaten me up.

18¶ Then answered the Jews and said unto him, What sign shewest thou unto us, seeing that thou doest these things? 19Jesus answered and said unto them, Destroy this temple, and in three days I will raise it up. 20Then said the Jews, Forty and six years was this temple in building, and wilt thou rear it up in three days? 21But he spake of the temple of his body. 22When therefore he was risen from the dead, his disciples remembered that he had said this unto them; and they believed the scripture, and the word which Jesus had said.

23¶ Now when he was in Jerusalem at the passover, in the feast day, many believed in his name, when they saw the miracles which he did. 24But Jesus did not commit himself unto them, because he knew all men, 25And needed not that any should testify of man: for he knew what was in man.