Ruʼuya ta Yohanna 21 – HCB & PCB

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 21:1-27

Sabuwar sama da sabuwar duniya

1Sa’an nan na ga sabon sama da sabuwar duniya, gama sama na farko da duniya ta farko sun shuɗe, babu kuma wani teku. 2Na ga Birni Mai Tsarki, sabuwar Urushalima tana saukowa daga sama, daga Allah, a shirye kamar amaryar da aka yi mata ado mai kyau saboda mijinta. 3Na kuma ji wata babbar murya daga kursiyin tana cewa, “Yanzu mazaunin Allah yana tare da mutane, zai kuma zauna tare da su. Za su zama mutanensa, Allah kansa kuwa zai kasance tare da su yă kuma zama Allahnsu. 4Zai share dukan hawaye daga idanunsu. Ba sauran mutuwa ko makoki ko kuka ko azaba, gama tsofaffin al’amura sun shuɗe.”

5Wannan da yake zaune a kursiyin ya ce. “Ina yin kome sabo!” Sai ya ce, “Rubuta wannan, domin waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma.”

6Ya ce mini, “An gama. Ni ne Alfa da kuma Omega, na Farko da kuma na Ƙarshe. Duk mai jin ƙishirwa zan ba shi abin sha kyauta daga maɓulɓular ruwan rai. 7Duk wanda ya ci nasara zai gāji dukan wannan, zan kuma zama Allahnsa, shi kuma zai zama ɗana. 8Amma matsorata, da marasa bangaskiya, masu ƙazanta, masu kisankai, masu fasikanci, masu sihiri, masu bautar gumaka da dukan maƙaryata, wurinsu zai kasance a cikin tafkin wutar da yake farar wuta mai ci. Wannan fa ita ce mutuwa ta biyu.”

9Ɗaya daga cikin mala’ikun nan bakwai masu kwanonin nan bakwai cike da annoban nan bakwai na ƙarshe, ya zo ya ce mini “Zo, zan nuna maka amaryar, matar Ɗan Ragon.” 10Ya kuwa ɗauke ni cikin Ruhu zuwa wani babban dutse mai tsayi, ya kuma nuna mini Birni Mai Tsarki, Urushalima, tana saukowa daga sama, daga Allah. 11Ya haskaka da ɗaukakar Allah, haskensa kuwa ya yi kamar lu’ulu’u mai daraja sosai, kamar yasfa, yana ƙyalƙyali kamar madubi. 12Yana da babbar katanga mai tsayi, mai ƙofofi goma sha biyu, da kuma mala’iku goma sha biyu a ƙofofin. A bisa ƙofofin an rubuta sunayen kabilu goma sha biyu na Isra’ila. 13Akwai ƙofofi uku a gabas, uku a arewa, uku a kudu, uku kuma a yamma. 14An gina katangar birnin a kan tushen gini goma sha biyu, a kansu kuwa akwai sunayen manzannin sha biyu na Ɗan Ragon.

15Mala’ikan da ya yi magana da ni yana da sandan awo na zinariya don awon birnin, ƙofofinsa, da kuma katangarsa. 16Birnin murabba’i ne, tsayinsa daidai ne da fāɗinsa. Ya auna birnin da sandarsa ya kuwa sami mil 1,400 (wajen kilomita 2,200) tsawonsa, fāɗinsa da kuma tsayinsa daidai suke. 17Ya auna katangarsa ya kuma sami ƙaurinta kamun 144, bisa ga ma’aunin mutum, wanda mala’ikan ya yi amfani da shi. 18An yi katangar da yasfa, birnin kuma da zinariya zalla, yana kuma ƙyalli kamar madubi. 19Tushen ginin katangar birnin kuwa an yi masa adon da kowane irin dutse mai daraja. Tushe na farko an yi shi yasfa, na biyu saffaya, na uku agat, na huɗu zumurrudu, 20na biyar onis, na shida yakutu, na bakwai kirisolit, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofuras, na goma sha ɗaya yasin, na goma sha biyu kuma ametis. 21Ƙofofi goma sha biyun nan lu’ulu’ai goma sha biyu ne, kowace ƙofa an yi ta da lu’ulu’u guda. Babban titin birnin kuwa an yi shi da zinariya zalla, yana kuma ƙyalli kamar madubi.

22Ban ga haikali a cikin birnin ba, domin Ubangiji Allah Maɗaukaki da kuma Ɗan Ragon ne haikalin birnin. 23Birnin ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi, gama ɗaukakar Allah tana ba shi haske, Ɗan Ragon kuwa shi ne fitilar birnin. 24Al’ummai za su yi tafiya cikin hasken birnin, sarakunan duniya kuma za su kawo darajarsu cikin birnin. 25Ba za a taɓa rufe ƙofofin birnin da rana ba, gama ba za a yi dare a can ba. 26Za a kawo ɗaukaka da girmar al’ummai a cikin birnin. 27Babu wani abu marar tsarkin da zai taɓa shiga cikin birnin, babu kuma wani mai aikata abin kunya ko ruɗi da zai shiga, sai dai waɗanda aka rubuta sunayensu a cikin littafin rai na Ɗan Ragon.

Persian Contemporary Bible

مکاشفه 21:1-27

اورشليم تازه

1سپس زمين و آسمان تازه‌ای را ديدم، چون آن زمين و آسمان اول ناپديد شده بود. از دريا هم ديگر خبری نبود. 2و من، يوحنا، شهر مقدسِ اورشليم را ديدم كه از آسمان از جانب خدا پايين می‌آمد. چه منظرهٔ باشكوهی بود! شهر اورشليم به زيبايی يک عروس بود كه خود را برای ملاقات داماد آماده كرده باشد!

3از تخت، صدايی بلند شنيدم كه می‌گفت: «خوب نگاه كن! خانهٔ خدا از اين پس در ميان انسانها خواهد بود. از اين پس خدا با ايشان زندگی خواهد كرد و ايشان خلق‌های خدا خواهند شد. بله، خود خدا با ايشان خواهد بود. 4خدا تمام اشكها را از چشمان آنها پاک خواهد ساخت. ديگر نه مرگی خواهد بود و نه غمی، نه ناله‌ای و نه دردی، زيرا تمام اينها متعلق به دنيای پيشين بود كه از بين رفت.»

5آنگاه او كه بر تخت نشسته بود، گفت: «ببين! الان همه چيز را نو می‌سازم!» و به من گفت: «اين را بنويس چون آنچه می‌گويم، راست و درست است. 6ديگر تمام شد! من الف و يا، و اول و آخر هستم. من به هر كه تشنه باشد از چشمهٔ آب حيات به رايگان خواهم داد تا بنوشد. 7هر كه پيروز شود تمام اين نعمتها را به ارث خواهد برد و من خدای او خواهم بود و او فرزند من. 8ولی ترسوها كه از پيروی من رو برمی‌گردانند و كسانی كه به من ايمان ندارند، فاسدان و قاتلان و زناكاران، جادوگران و دروغگويان، و كسانی كه به جای خدا، بت می‌پرستند، جای همه در درياچه‌ای است كه با آتش و گوگرد می‌سوزد. اين همان مرگ دوم است.»

9آنگاه يكی از آن هفت فرشته كه هفت جام بلای آخر را دارند، نزد من آمد و گفت: «همراه من بيا تا عروس را به تو نشان دهم. او همسر بره است.»

10سپس در يک رؤيا، مرا به قله كوه بلندی برد. از آنجا، شهر مقدس اورشليم را ديدم كه از جانب خدا از آسمان پايين می‌آمد. 11شهر غرق در جلال و شكوه خدا بود، و مثل يک تكه جواهر قيمتی كه بلورهای شفافش برق می‌زند، می‌درخشيد. 12ديوارهای شهر، پهن و بلند بود. شهر دوازده دروازه و دوازده فرشتهٔ دربان داشت. اسامی دوازده قبيلهٔ بنی‌اسرائيل روی دروازه‌ها نوشته شده بود. 13در هر طرف، يعنی در شمال، جنوب، شرق و غرب شهر، سه دروازه وجود داشت. 14ديوارهای شهر دوازده پايه داشت كه بر آنها اسامی رسولان «برّه» نوشته شده بود.

15در دست فرشته يک چوب طلا بود كه با آن در نظر داشت شهر و دروازه‌ها و ديوارهايش را اندازه بگيرد. 16وقتی شهر را اندازه گرفت، معلوم شد به شكل مربع است، يعنی طول و عرضش با هم مساوی است. در واقع، شهر به شكل مكعب بود، زيرا بلندی‌اش نيز به اندازهٔ طول و عرضش بود، يعنی هر ضلعش دوازده هزار تير پرتاب بود. 17سپس بلندی ديوار شهر را اندازه گرفت و معلوم شد در همه جا صد و چهل و چهار ذراع است. فرشته با استفاده از واحدهای مشخص، اين اندازه‌ها را به من گفت.

18‏-19خود شهر از طلای خالص مانند شيشه شفاف ساخته شده بود و ديوار آن از يَشم بود كه بر روی دوازده لايه از سنگهای زيربنای جواهرنشان ساخته شده بود: لايهٔ اول از يشم، دومی از سنگ لاجورد، سومی از عقيق سفيد، چهارمی از زمرد، 20پنجمی از عقيق سرخ، ششمی از عقيق، هفتمی از زبرجد، هشتمی از ياقوت كبود، نهمی از ياقوت زرد، دهمی از عقيق سبز، يازدهمی از فيروزه و دوازدهمی از ياقوت بود.

21جنس دوازده دروازهٔ شهر از مرواريد بود، هر دروازهٔ از يک قطعه مرواريد. خيابان اصلی شهر از طلای ناب بود كه مثل شيشه می‌درخشيد.

22در شهر هيچ عبادتگاهی ديده نمی‌شد، زيرا خدای توانا و «برّه» را همه جا بدون هيچ واسطه‌ای پرستش می‌كردند. 23اين شهر احتياجی به نور خورشيد و ماه نداشت، چون شكوه و جلال خدا و «بره» شهر را روشن می‌ساخت. 24نورش قومهای زمين را نيز نورانی می‌كرد، و پادشاهان دنيا می‌آمدند و جلال خود را نثار آن می‌كردند. 25دروازه‌های شهر هرگز بسته نمی‌شود، چون در آنجا هميشه روز است و شبی وجود ندارد! 26عزّت و جلال و افتخار تمام قومها به آن وارد می‌شود. 27هيچ بدی يا شخص نادرست و فاسد اجازه ورود به آنجا را ندارد. اين شهر فقط جای كسانی است كه نامشان در كتاب حيات «برّه» نوشته شده باشد.