An maido da Eden
1Sai mala’ikan ya nuna mini kogin ruwan rai, mai ƙyalli kamar madubi, yana gangarawa daga kursiyin Allah da na Ɗan Ragon, 2yana bin tsakiyar babban titi na birnin. A kowane gefen kogin akwai itacen rai mai ba da ’ya’ya goma sha biyu, yana ba da ’ya’yansa kowane wata. Ganyayen itacen kuwa saboda warkar da al’ummai ne. 3Ba za a ƙara samun la’ana ba. Kursiyin Allah da na Ɗan Ragon zai kasance a cikin birnin, bayinsa kuma za su yi masa hidima. 4Za su ga fuskarsa, sunansa kuma zai kasance a goshinsu. 5Ba za a ƙara yin dare ba. Ba za su bukaci hasken fitila ko hasken rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su. Za su kuwa yi mulki har abada abadin.
Yohanna da Mala’ikan
6Mala’ikan ya ce mini, “Waɗannan kalmomi amintattu ne gaskiya ne kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa, ya aiki mala’ikansa, don yă nuna wa bayinsa abubuwan da za su faru nan ba da daɗewa ba.”
7“Ga shi! Ina zuwa da wuri! Mai albarka ne wanda yake kiyaye kalmomin annabcin da suke cikin wannan littafi.”
8Ni, Yohanna, na ji, na kuma ga abubuwan nan. Kuma sa’ad da na ji, na kuma gan su, sai na fāɗi a ƙasa a gaban mala’ikan da yake nuna mini su, don in yi sujada. 9Amma ya ce mini, “Kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da ’yan’uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye kalmomin wannan littafi. Allah za ka yi wa sujada!”
10Sa’an nan ya gaya mini cewa, “Kada ka rufe kalmomin annabcin littafin nan, domin lokaci ya yi kusa. 11Duk mai yin laifi yă ci gaba da yin laifi; duk mai aikata ƙazanta yă ci gaba da aikata ƙazanta. Duk mai aikata abin da yake daidai, yă ci gaba da aikata abin da yake daidai. Kuma duk wanda yake mai tsarki, yă ci gaba da yin abin da yake da tsarki.”
Maganar ƙarshe. Gayyata da gargaɗi
12“Ga shi, ina zuwa da wuri! Ladan da zan bayar yana tare da ni, kuma zan ba wa kowa gwargwadon abin da ya yi. 13Ni ne Alfa da kuma Omega, na Fari da kuma na Baya, Farko da kuma Ƙarshe.
14“Masu albarka ne waɗanda suka wanke tufafinsu, don su sami izinin ci daga itacen rai su kuma shiga birnin ta ƙofofi. 15Waɗanda suke waje kuwa karnuka ne, masu sihiri, masu fasikanci, masu kisankai, masu bautar gumaka, da duk wanda yake ƙaunar ƙarya yake kuma aikata ta.
16“Ni, Yesu, na aiko mala’ikana ya ba ka wannan shaida saboda ikkilisiyoyi. Ni ne Tushe da kuma Zuriyar Dawuda, da kuma Tauraron Asubahi mai haske.”
17Ruhu da kuma amarya suna cewa, “Zo!” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo!” Duk mai jin ƙishirwa, yă zo; duk mai bukata kuma, yă ɗibi ruwan rai kyauta.
18Ina yin wa duk wanda ya ji kalmomin annabcin wannan littafi gargaɗi. Duk wanda ya ƙara wani abu a kansu, Allah zai ƙara masa annoban da aka bayyana a littafin nan. 19Duk wanda kuma ya yi ragi a kalmomi daga littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai da kuma na birnin nan mai tsarki, waɗanda aka bayyana a littafin nan.
20Shi da ya shaida waɗannan abubuwa ya ce, “I, ina zuwa da wuri.”
Amin. Zo, Ubangiji Yesu!
21Alherin Ubangiji Yesu yă kasance tare da mutanen Allah. Amin.
1آنگاه رودخانهٔ آب حيات را به من نشان داد كه مثل بلور، صاف و زلال بود. رودخانه از تخت خدا و «برّه» جاری میشد، 2و از وسط جادهٔ اصلی میگذشت. دو طرف رودخانه، درختان حيات قرار داشت كه سالی دوازده بار ميوه میدادند يعنی هر ماه يک نوع ميوهٔ تازه. برگهايش نيز شفابخش بود و برای درمان قومها به کار میرفت.
3در شهر چيزی بدی يافت نخواهد شد، چون تخت خدا و «برّه» در آنجاست. خدمتگزاران خدا، او را پرستش خواهند كرد، 4و رويش را خواهند ديد و نامش روی پيشانیشان نوشته خواهد بود. 5در آنجا ديگر شب نخواهد بود. احتياجی هم به چراغ و خورشيد نخواهد بود، چون خداوند بزرگ نور ايشان خواهد بود و ايشان تا ابد سلطنت خواهند كرد.
6آنگاه فرشته به من گفت: «اين سخنان راست و قابل اعتماد است. و خدايی كه وقايع آينده را از قبل به انبيا خود اطلاع میدهد، فرشتهٔ خود را فرستاده است تا آنچه را كه بزودی روی خواهد داد به شما اطلاع دهد.»
عيسی بزودی میآيد
7عيسی مسيح میفرمايد: «گوش كنيد! من بزودی میآيم. خوشا به حال كسانی كه آنچه را كه در اين كتاب پيشگويی شده، باور میكنند.»
8من، يوحنا، تمام اين چيزها را ديدم و شنيدم و زانو زدم تا فرشتهای را كه آنها را به من نشان داده بود، پرستش كنم. 9ولی او بار ديگر به من گفت: «نه، اين كار را نكن. من نيز مانند تو و برادرانت يعنی انبيا خدا، و تمام كسانی كه به حقايق اين كتاب اعتماد دارند، از خدمتگزاران عيسی میباشم. پس فقط خدا را پرستش كن.»
10سپس به من دستور داده، گفت: «پيشگويیهای اين كتاب را در دسترس همه بگذار، چون بزودی به وقوع خواهند پيوست. 11وقتی آن زمان فرا رسد، بدكاران باز هم به كارهای بد خود ادامه خواهند داد و فاسدان باز هم فاسدتر خواهند شد، ولی نیکان، نیکتر و پاكان، پاکتر میگردند.»
12عيسی مسيح میفرمايد: «چشم به راه باشيد، من به زودی میآيم و برای هر كس مطابق اعمالش پاداشی با خود خواهم آورد. 13من الف و يا، آغاز و پايان، اول و آخر هستم. 14خوشا به حال كسانی كه لباسهایشان را دائماً میشويند. آنها اجازهٔ ورود به شهر و خوردن ميوهٔ درخت حيات را خواهند داشت. 15اما فاسدان، جادوگران، زناكاران، قاتلان، بتپرستان، دروغگويان و متقلبان، به شهر راه نخواهند يافت.
16«من، عيسی، فرشتهٔ خود را نزد شما فرستادم تا همه چيز را با كليساها در ميان بگذارم. من از اصل و نسب داوود هستم. من ستارهٔ درخشندهٔ صبح میباشم.»
17روح و عروس میگويند: «بيا!» هر کس اين را میشنود، بگويد: «بيا!» هر كه تشنه است بيايد، و هر کس مايل است بيايد، و از آب حيات به رايگان بنوشد.
18به كسی كه پيشگويیهای اين كتاب را میشنود با صراحت میگويم كه اگر به نوشتههای اين كتاب چيزی اضافه كند، خدا بلاهای اين كتاب را بر سرش خواهد آورد. 19و اگر از اين پيشگويیها مطلبی كم كند، خداوند او را از درخت حيات و شهر مقدس كه آن را شرح دادم، بینصيب خواهد ساخت. 20كسی كه اين چيزها را گفته است، میفرمايد: «بله، من بزودی میآيم!»
«آمين! ای عيسای خداوند، بيا!»
21فيض خداوند ما عيسی مسيح بر همهٔ شما باد! آمين!