Romawa 2 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

Romawa 2:1-29

Shari’ar adalcin Allah

1Saboda haka, kai da kake ba wa wani laifi, ba ka da wata hujja, gama a duk lokacin da kake ba wa wani laifi, kana hukunta kanka ne, domin kai da kake ba wa wani laifi kai ma kana aikata waɗannan abubuwa. 2Yanzu mun san cewa hukuncin Allah a kan masu aikata waɗannan abubuwa daidai ne. 3Saboda haka sa’ad da kai mutum kurum, kana ba su laifi, duk da haka kana aikata abubuwan nan, kana tsammani za ka tsere wa hukuncin Allah ne? 4Ko kuma kana rena wadatar alherinsa, haƙurinsa, da kuma jimrewarsa ne ba tare da sanin cewa alherin Allah yana kai ka ga tuba ba ne?

5Amma saboda taurinkanka da zuciyarka marar tuba, kana tara wa kanka fushi a ranar fushin Allah, sa’ad da za a bayyana hukuncinsa mai adalci. 6Allah, “Zai sāka wa kowane mutum gwargwadon aikin da ya yi.”2.6 Zab 62.12; K Mag 24.12 7Ga waɗanda ta wurin naciya suna yin nagarta suna neman ɗaukaka, girma da rashin mutuwa, su za a ba su rai madawwami. 8Amma ga waɗanda suke sonkai waɗanda suke ƙin gaskiya suke kuma bin mugunta, akwai fushi da haushi dominsu. 9Akwai wahala da baƙin ciki ga duk mutumin da yake aikata mugunta, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai, 10amma akwai ɗaukaka, girma da salama ga duk mutumin da yake aikata alheri, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai. 11Gama Allah ba ya nuna bambanci.

12Duk waɗanda suka yi zunubi a rashi sanin doka, a rashin doka za su hallaka, waɗanda kuma suka yi zunubi ƙarƙashin doka, a ƙarƙashin doka za a hukunta su. 13Gama ba masu jin dokar ne suke da adalci a gaban Allah ba, amma waɗanda suke yin biyayya da dokar, su za a ce da su masu adalci. 14Tabbatacce, sa’ad da Al’ummai, waɗanda ba su da dokar, suka aikata abubuwan da dokar take bukata, abubuwan sun zama doka ke nan gare su, ko da yake ba su da dokar. 15To, da yake sun nuna cewa abubuwan da dokar take bukata suna a rubuce a zukatansu, lamirinsu yana kuma ba da shaida, tunaninsu kuwa yanzu yana zarginsu ko kuma yana kāre su. 16Wannan zai faru a ranar da Allah ta wurin Yesu Kiristi zai shari’anta ɓoyayyun abubuwan da mutane suka yi, yadda bisharata ta furta.

Yahudawa da doka

17To, kai, da kake kiran kanka mutumin Yahuda; in kana dogara ga doka kana kuma taƙama da dangantakarka da Allah; 18in ka san nufinsa ka kuma amince da abin da yake mafifici domin an koyar da kai bisa ga doka; 19in ka tabbata cewa kai jagora ne ga makafi, haske ga waɗanda suke cikin duhu, 20mai koyar da masu wauta, malamin jarirai, domin a cikin dokar ce akwai sani da gaskiya 21to, kai mai koya wa waɗansu, ba kanka kake koya wa ba? Kai da kake wa’azi kada a yi sata, kana sata? 22Kai da kake cewa wa mutane kada su yi zina, kana yin zina? Kai da kake ƙyamar gumaka, kana wa haikali fashi? 23Kai da kake taƙama da doka, kana nuna rashin bangirma ga Allah ta wurin karya dokar? 24Kamar yadda yake a rubuce, “Ana saɓon sunan Allah a cikin Al’ummai saboda ku.”2.24 Ish 52.5; Ezk 36.22

25Kaciya tana da amfani in kana kiyaye dokar, amma in kana karya dokar, ka zama kamar ba a yi maka kaciya ba. 26In marasa kaciya suna kiyaye dokar, ashe, ba za a ɗauke su kamar an yi musu kaciya ba? 27Wanda ba shi da kaciya ta jiki duk da haka yana biyayya da dokar zai iya hukunta ka, kai da kake karya dokar, ko da yake kana da rubutaccen tsarin dokar an kuma yi maka kaciya.

28Mutum ba mutumin Yahuda ba ne in shi mutumin Yahuda ne kawai a jiki, haka kuma kaciya ba a waje ko a jiki kawai ba. 29A’a, mutum mutumin Yahuda ne in shi mutumin Yahuda ne a zuci; kuma kaciya ita ce kaciya ta zuci, ta wurin Ruhu, ba ta wurin rubutaccen doka ba. Irin wannan mutum yana samun yabo daga Allah ne, ba ɗan adam ba.

New International Reader’s Version

Romans 2:1-29

God Judges Fairly

1If you judge someone else, you have no excuse for it. When you judge another person, you are judging yourself. You do the same things you blame others for doing. 2We know that when God judges those who do evil things, he judges fairly. 3Though you are only a human being, you judge others. But you yourself do the same things. So how do you think you will escape when God judges you? 4Do you disrespect God’s great kindness and favor? Do you disrespect God when he is patient with you? Don’t you realize that God’s kindness is meant to turn you away from your sins?

5But you are stubborn. In your heart you are not sorry for your sins. You are storing up anger against yourself. The day of God’s anger is coming. Then his way of judging fairly will be shown. 6God “will pay back each person in keeping with what they have done.” (Psalm 62:12; Proverbs 24:12) 7God will give eternal life to those who keep on doing good. They want glory, honor, and life that never ends. 8But there are others who only look out for themselves. They don’t accept the truth. They go astray. God will pour out his great anger on them. 9There will be trouble and suffering for everyone who does evil. That is meant first for the Jews. It is also meant for the Gentiles. 10But there will be glory, honor and peace for everyone who does good. That is meant first for the Jews. It is also meant for the Gentiles. 11God treats everyone the same.

12Some people do not know God’s law when they sin. They will not be judged by the law when they die. Others do know God’s law when they sin. They will be judged by the law. 13Hearing the law does not make a person right with God. People are considered to be right with God only when they obey the law. 14Gentiles do not have the law. Sometimes they just naturally do what the law requires. They are a law for themselves. This is true even though they don’t have the law. 15They show that what the law requires is written on their hearts. The way their minds judge them proves this fact. Sometimes their thoughts find them guilty. At other times their thoughts find them not guilty. 16This will happen on the day God appoints Jesus Christ to judge people’s secret thoughts. That’s part of my good news.

The Jews and the Law

17Suppose you call yourself a Jew. You trust in the law. You brag that you know God. 18You know what God wants. You agree with what is best because the law teaches you. 19You think you know so much more than the people you teach. You think you’re helping blind people. You think you are a light for those in the dark. 20You think you can make foolish people wise. You act like you’re teaching little children. You think that the law gives you all knowledge and truth. 21You claim to teach others, but you don’t even teach yourself! You preach against stealing. But you steal! 22You say that people should not commit adultery. But you commit adultery! You hate statues of gods. But you rob temples! 23You brag about the law. But when you break it, you rob God of his honor! 24It is written, “The Gentiles say evil things against God’s name because of you.” (Isaiah 52:5; Ezekiel 36:22)

25Circumcision has value if you obey the law. But if you break the law, it is just as if you hadn’t been circumcised. 26And sometimes those who aren’t circumcised do what the law requires. Won’t God accept them as if they had been circumcised? 27Many are not circumcised physically, but they obey the law. They will prove that you are guilty. You are breaking the law, even though you have the written law and are circumcised.

28A person is not a Jew if they are a Jew only on the outside. And circumcision is more than just something done to the outside of a man’s body. 29No, a person is a Jew only if they are a Jew on the inside. And true circumcision means that the heart has been circumcised by the Holy Spirit. The person whose heart has been circumcised does more than obey the written law. The praise that matters for that kind of person does not come from other people. It comes from God.