Romawa 1 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

Romawa 1:1-32

1Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah. 2Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki 3game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne. 4Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne. 5Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya. 6Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.

7Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka.

Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.

Bulus ya yi marmari yă ziyarci Roma

8Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya. 9Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku 10cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.

11Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi 12wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu. 13Ina so ku sani ’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.

14Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci. 15Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.

16Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai. 17Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”1.17 Hab 2.4

Fushin Allah a kan ’yan adam

18Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu, 19gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi. 20Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja.

21Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta. 22Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye, 23suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.

24Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya. 25Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin.

26Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da ’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba. 27Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.

28Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba. 29Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne, 30da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu; 31su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi. 32Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.

New International Reader’s Version

Romans 1:1-32

1I, Paul, am writing this letter. I serve Christ Jesus. I have been appointed to be an apostle. God set me apart to tell others his good news. 2He promised the good news long ago. He announced it through his prophets in the Holy Scriptures. 3The good news is about God’s Son. He was born into the family line of King David. 4By the Holy Spirit, he was appointed to be the mighty Son of God. God did this by raising him from the dead. He is Jesus Christ our Lord. 5We received grace because of what Jesus did. He made us apostles to the Gentiles. We must invite all of them to obey God by trusting in Jesus. We do this to bring glory to him. 6You also are among those Gentiles who are appointed to belong to Jesus Christ.

7I am sending this letter to all of you in Rome. You are loved by God and appointed to be his holy people.

May God our Father and the Lord Jesus Christ give you grace and peace.

Paul Longs to Visit Rome

8First, I thank my God through Jesus Christ for all of you. People all over the world are talking about your faith. 9I serve God with my whole heart. I preach the good news about his Son. God knows that I always remember you 10in my prayers. I pray that now at last it may be God’s plan to open the way for me to visit you.

11I long to see you. I want to make you strong by giving you a gift from the Holy Spirit. 12I want us to encourage one another in the faith we share. 13Brothers and sisters, I want you to know that I planned many times to visit you. But until now I have been kept from coming. My work has produced results among the other Gentiles. In the same way, I want to see results among you.

14I have a duty both to Greeks and to non-Greeks. I have a duty both to wise people and to foolish people. 15So I really want to preach the good news also to you who live in Rome.

16I want to preach it because I’m not ashamed of the good news. It is God’s power to save everyone who believes. It is meant first for the Jews. It is meant also for the Gentiles. 17The good news shows God’s power to make people right with himself. God’s power to be made right with him is given to the person who has faith. It happens by faith from beginning to end. It is written, “The one who is right with God will live by faith.” (Habakkuk 2:4)

God’s Anger Against Sinners

18God shows his anger from heaven. It is against all the godless and evil things people do. They are so evil that they say no to the truth. 19The truth about God is plain to them. God has made it plain. 20Ever since the world was created it has been possible to see the qualities of God that are not seen. I’m talking about his eternal power and about the fact that he is God. Those things can be seen in what he has made. So people have no excuse for what they do.

21They knew God. But they didn’t honor him as God. They didn’t thank him. Their thinking became worthless. Their foolish hearts became dark. 22They claimed to be wise. But they made fools of themselves. 23They would rather have statues of gods than the glorious God who lives forever. Their statues of gods are made to look like people, birds, animals and reptiles.

24So God let them go. He allowed them to do what their sinful hearts wanted to. He let them commit sexual sins. They made one another’s bodies impure by what they did. 25They chose a lie instead of the truth about God. They worshiped and served created things. They didn’t worship the Creator. But he is praised forever. Amen.

26So God let them continue to have their shameful desires. Their women committed sexual acts that were not natural. 27In the same way, the men turned away from their natural love for women. They burned with sexual desire for each other. Men did shameful things with other men. They suffered in their bodies for all the wrong things they did.

28They didn’t think it was important to know God. So God let them continue to have evil thoughts. They did things they shouldn’t do. 29They are full of every kind of sin, evil and ungodliness. They want more than they need. They commit murder. They want what belongs to other people. They fight and cheat. They hate others. They say mean things about other people. 30They tell lies about them. They hate God. They are rude and proud. They brag. They think of new ways to do evil. They don’t obey their parents. 31They do not understand. They can’t be trusted. They are not loving and kind. 32They know that God’s commands are right. They know that those who do evil things should die. But they continue to do those very things. They also approve of others who do them.