Mattiyu 4 – HCB & CCBT

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 4:1-25

Gwajin Yesu

(Markus 1.12,13; Luka 4.1-13)

1Sa’an nan Ruhu ya kai Yesu cikin hamada don Iblis yă gwada shi. 2Bayan ya yi azumi yini arba’in da kuma dare arba’in, sai ya ji yunwa. 3Sai mai gwajin ya zo wurinsa ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka ce wa duwatsun nan su zama burodi.”

4Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, sai dai da kowace kalmar da take fitowa daga bakin Allah.’4.4 M Sh 8.3

5Sai Iblis ya kai shi birni mai tsarki, ya kai shi can wuri mafi tsayi duka na haikali. 6Ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, yi tsalle ka sauka ƙasa. Gama a rubuce yake,

“ ‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai,

za su tallafe ka da hannuwansu,

don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’4.6 Zab 91.11,12

7Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake kuma cewa, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’4.7 M Sh 6.16

8Har wa yau, Iblis ya kai shi bisa wani dutse mai tsawo sosai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu. 9Ya ce, “Zan ba ka dukan wannan, in za ka durƙusa ka yi mini sujada.”

10Sai Yesu ya ce masa, “Rabu da ni, Shaiɗan! Gama a rubuce yake, ‘Yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai kuma za ka bauta wa.’4.10 M Sh 6.13

11Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.

Yesu ya fara wa’azi

(Markus 1.14,15; Luka 4.14,15)

12Da Yesu ya ji labari cewa an kulle Yohanna a kurkuku, sai ya koma zuwa Galili. 13Ya bar Nazaret, ya je ya zauna a Kafarnahum, wadda take a bakin tafki wajen Zebulun da Naftali 14don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,

15“Ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali,

da kuke a hanyar zuwa tekun Galili, a ƙetaren Urdun,

wannan yankin Galili ta Al’ummai,

16mutanen da suke zama cikin duhu

sun ga babban haske;

haske kuma ya haskaka

a kan waɗanda suke zama a inuwar mutuwa.”4.16 Ish 9.1,2f

17Tun daga wannan lokaci, Yesu ya fara wa’azi yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”

Kiran almajirai na farko

(Markus 1.16-20; Luka 5.1-11)

18Da Yesu yana kan tafiya a bakin Tekun Galili, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Siman wanda ake kira Bitrus da ɗan’uwansa Andarawus. Suna jefa abin kamun kifi a tafki, gama su masunta ne. 19Sai Yesu ya ce, “Zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masu jan mutane zuwa wurina.” 20Nan da nan suka bar abin kamun kifinsu suka bi shi.

21Da ya ci gaba daga nan, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna. Suna cikin jirgin ruwa tare da mahaifinsu Zebedi, suna shirya abin kamun kifinsu. Yesu ya kira su, 22nan take suka bar jirgin ruwan da mahaifinsu suka kuwa bi Yesu.

Yesu ya warkar da marasa lafiya

(Luka 6.17-19)

23Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane. 24Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su. 25Taron mutane mai yawa daga Galili, Dekafolis,4.25 Wato, Birane Goma Urushalima, Yahudiya da kuma yankin hayin Urdun suka bi shi.

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

馬太福音 4:1-25

耶穌受試探

1後來,耶穌被聖靈帶到曠野,去受魔鬼的試探。 2耶穌禁食了四十晝夜後,很饑餓。 3試探者前來對祂說:「如果你是上帝的兒子,可以叫這些石頭變成食物。」

4耶穌回答說:「聖經上說,『人活著不是單靠食物,乃是靠上帝口中的每一句話。』」

5魔鬼又帶祂進聖城,讓祂站在聖殿的最高處, 6說:「如果你是上帝的兒子,就跳下去吧!因為聖經上說,『上帝會差遣祂的天使用手托住你,不讓你的腳碰在石頭上。』」

7耶穌回答說:「聖經上也說,『不可試探主——你的上帝。』」

8魔鬼再帶耶穌到一座極高的山上,把世上萬國及其榮華富貴展示給祂看, 9說:「如果你俯伏敬拜我,我就把這一切都給你。」

10耶穌說:「撒旦,走開!聖經上說,『要敬拜主——你的上帝,單單事奉祂。』」

11於是魔鬼離開了耶穌,這時有天使前來伺候祂。

開始傳道

12耶穌聽見約翰被捕入獄,就回到加利利13後來,祂離開拿撒勒迦百農住。迦百農靠近湖邊,在西布倫拿弗他利地區。 14這就應驗了以賽亞先知的話:

15西布倫拿弗他利

沿海一帶及約旦河東、外族人居住的加利利啊!

16你們住在黑暗中的人看見了大光,

活在死亡陰影下的人被光照亮了!」

17從那時起,耶穌開始傳道:「悔改吧,因爲天國臨近了!」

呼召門徒

18耶穌沿著加利利湖邊行走的時候,看見被稱為彼得西門安得烈兩兄弟正在撒網打魚,他們是漁夫。 19耶穌對他們說:「來跟從我!我要使你們成為得人的漁夫。」 20他們立刻撇下漁網,跟從了耶穌。 21耶穌再往前走,又看見雅各約翰兩兄弟正和父親西庇太一起在船上補漁網。耶穌呼召他們, 22他們馬上離開漁船,辭別父親,跟從了耶穌。

教導和醫治

23耶穌走遍加利利,在各個會堂裡教導人,宣講天國的福音,醫治人們各樣的疾病。 24祂的名聲傳遍了整個敘利亞。人們把一切患病的,就是患各種疾病的、疼痛的、癲癇的、癱瘓的,以及被鬼附身的都帶到祂面前,祂都醫治了他們。 25因此,有大群的人跟從了祂,他們來自加利利低加坡里耶路撒冷猶太約旦河東。