Mattiyu 3 – HCB & CCBT

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 3:1-17

Yohanna Mai Baftisma ya shirya hanya

(Markus 1.1-8; Luka 3.1-18; Yohanna 1.19-28)

1A waɗancan kwanaki, Yohanna Mai Baftisma ya zo, yana wa’azi a Hamadan Yahudiya 2yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.” 3Wannan shi ne wanda aka yi maganarsa ta wurin annabi Ishaya cewa,

“Ga murya mai kira a hamada tana cewa,

‘Ku shirya wa Ubangiji hanya,

ku miƙe hanyoyi dominsa.’ ”3.3 Ish 40.3

4Tufafin Yohanna kuwa an yi su da gashin raƙumi ne, yana kuma daure da ɗamara ta fata. Abincinsa kuwa fāri ne da zumar jeji. 5Mutane suka zo wurinsa daga Urushalima da dukan Yahudiya da kuma dukan yankin Urdun. 6Suna furta zunubansu, ya kuma yi musu baftisma a Kogin Urdun.

7Amma da Yohanna ya ga Farisiyawa da Sadukiyawa da yawa suna zuwa inda yake yin baftisma, sai ya ce musu, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku ku guje wa fushin nan mai zuwa? 8Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. 9Kada ma ku yi tunani a ranku cewa, ‘Ai, Ibrahim ne mahaifinmu.’ Ina gaya muku cewa Allah zai iya tā da ’ya’ya wa Ibrahim daga cikin duwatsun nan. 10An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da ’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.

11“Ina muku baftisma da3.11 Ko kuwa a cikin ruwa domin tuba. Amma wani yana zuwa a bayana wanda ya fi ni iko, wanda ko takalmansa ma ban isa in ɗauka ba. Zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta. 12Yana riƙe da matankaɗinsa, zai tankaɗe hatsinsa, yă kuma tattara alkamarsa a cikin rumbu, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”

Baftismar Yesu

(Markus 1.9-11; Luka 3.21,22)

13Sai Yesu ya zo daga Galili, ya je Urdun don Yohanna yă yi masa baftisma. 14Amma Yohanna ya so yă hana shi, yana cewa, “Ina bukata ka yi mini baftisma, yaya kake zuwa wurina?”

15Yesu ya amsa ya ce, “Bari yă zama haka yanzu; ya dace mu yi haka don mu cika dukan adalci.” Sa’an nan Yohanna ya yarda.

16Nan da nan da aka yi wa Yesu baftisma, sai ya fito daga ruwa. A wannan lokaci sama ya buɗe, sai ya ga Ruhun Allah yana saukowa kamar kurciya ya kuwa sauka a kansa. 17Sai murya daga sama ta ce, “Wannan shi ne Ɗana wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai.”

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

馬太福音 3:1-17

開路先鋒

1那時,施洗者約翰來到猶太的曠野傳道,說: 2「悔改吧,因為天國臨近了!」 3約翰就是以賽亞先知所說的那位,他說:「有人在曠野大聲呼喊,『預備主的道,修直祂的路。』」

4約翰身穿駱駝毛的衣服,腰束皮帶,吃的是蝗蟲、野蜜。 5那時,耶路撒冷猶太各地和約旦河一帶的人都來到約翰那裡, 6承認他們的罪,在約旦河裡接受他的洗禮。

7約翰看見很多法利賽人和撒都該人也來受洗,就對他們說:「你們這些毒蛇的後代!誰指示你們逃避那將臨的烈怒呢? 8你們要結出與悔改相稱的果子。 9不要心裡說,『我們是亞伯拉罕的子孫。』我告訴你們,上帝可以從這些石頭中興起亞伯拉罕的子孫。 10現在斧頭已經放在樹根上了,不結好果子的樹都要被砍下,丟在火裡。 11我用水為你們施洗,叫你們悔改。但在我之後,有位比我更有能力的要來,我連替祂提鞋都不配。祂要用聖靈和火為你們施洗。 12祂手拿簸箕,要把穀場清理乾淨,將麥子存入倉裡,用不滅的火把糠秕燒盡。」

耶穌受洗

13後來,耶穌從加利利來到約旦河要約翰為祂施洗。 14約翰想要攔住祂,就說:「應該是你為我施洗才對,你反倒來找我?」

15耶穌回答說:「你就這樣做吧!我們理當這樣遵行上帝一切的要求。」於是約翰答應了。

16耶穌受了洗,剛從水裡上來,天就開了。祂看見上帝的聖靈像鴿子一樣降到祂身上, 17又有聲音從天上傳來:「這是我的愛子,我甚喜悅祂。」