מעשי השליחים 20 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

מעשי השליחים 20:1-38

1לאחר ששככה הסערה אסף פולוס את התלמידים, ובדברי עידוד נפרד מהם לשלום ויצא בדרכו למקדוניה. 2בכל הערים שבהן עבר הוא לימד את המאמינים את דבר ה׳, ולבסוף הגיע ליוון. 3כעבור שלושה חודשים התכונן פולוס ללכת לסוריה, אולם משנודע לו שהיהודים תכננו להתנקש בחייו, החליט לסטות מדרכו ולנסוע קודם צפונה, למקדוניה.

4מספר אנשים ליוו את פולוס עד אסיה הקטנה: סופטרוס בן־פורוס מברואה; ארסטרכוס וסקונדוס מתסלוניקי; גיוס מדרבי; טימותיוס; וטוכיקוס וטרופימוס אשר חזרו לבתיהם באסיה הקטנה. 5כל אלה הלכו לפנינו וחיכו לנו בטרואס. 6בתום חג הפסח עלינו על ספינה בפיליפי, שבצפון יוון, וכעבור חמישה ימים הגענו לטרואס, שם נשארנו שבוע ימים.

7במוצאי שבת התאספנו יחד לבצוע לחם, ופולוס, שעמד לצאת לדרכו למחרת בבוקר, דרש דרשה שנמשכה עד חצות. 8חדר־העלייה שבו התאספנו היה מואר בנרות רבים. 9כל אותו זמן ישב אבטוכוס הצעיר על אדן החלון, ומכיוון שפולוס האריך בדבריו, נפלה עליו תרדמה. לפתע איבד אבטוכוס את שיווי משקלו ונפל ארצה מן הקומה השלישית ומת בו במקום. 10‏-12פולוס רץ למטה ולקח את הבחור בזרועותיו. ”אל תדאגו,“ הרגיע אותם, ”יש בו רוח חיים והוא יהיה בסדר!“ ואכן הכרתו שבה אליו. שמחה גדולה מילאה את כל הקהילה. כולם חזרו לעליית־הגג. פולוס אכל ולאחר מכן פתח בדרשה נוספת שנמשכה עד אור הבוקר, ואז ניפרד מהם לשלום.

13פולוס המשיך ברגל לאסוס, ואילו אנחנו הגענו לשם לפניו בספינה. 14כאשר הצטרף אלינו באסוס, הפלגנו יחד למיטוליני. 15למחרת הפלגנו דרך כיוס, ביום השלישי עגנו בסמוס (בלילה ישנו בטרוגוליון), וביום הרביעי הגענו למיליטוס.

16פולוס סרב להתעכב הפעם באפסוס, כי רצה להגיע לירושלים לקראת חג השבועות, אם יעלה הדבר בידו. 17אולם בהגיענו למיליטוס שלח פולוס הודעה לזקני הקהילה באפסוס, וביקש מהם לבוא לפגוש אותו שם.

18כשהגיעו, אמר להם: ”אתם יודעים היטב שמהיום הראשון שדרכתי על אדמת אסיה ועד היום הזה, 19עשיתי את עבודת האדון בענווה – ואפילו בדמעות – למרות הצרות שגרמו לי נוכלים מבין היהודים. 20ובכל זאת, מעולם לא פחדתי לומר לכם את האמת; לימדתי אתכם והטפתי לכם בציבור ובבתים פרטיים. 21בישרתי לכם בשורה אחת ליהודים ולגויים גם יחד, שעליהם להפסיק לחטוא, לחזור בתשובה, ולפנות לאלוהים באמצעות האמונה בישוע המשיח אדוננו.

22”עתה אני הולך לירושלים, כי עלי לציית לרוח הקודש המדריך אותי, אולם איני יודע מה מצפה לי שם. 23אני יודע רק דבר אחד: שבכל עיר רוח הקודש מזהיר אותי מפני העינויים והמאסר המצפים לי. 24אולם לחיי אין כל ערך אם לא אבצע את המשימה שהטיל עלי ישוע אדוננו: לספר לכולם על אהבת אלוהים ועל חסדו.

25”אני בטוח שאף אחד מכם – אשר שמעתם מפי את דבר ה׳ – לא ישוב לראותי, 26ומשום כך עלי לומר לכם: מצפוני נקי בנוגע לכל אחד ואחד מכם! 27כי מעולם לא היססתי לבשר לכם את דבר האלוהים.

28”השגיחו על עצמכם ועל הצאן שרוח הקודש הטיל עליכם את האחריות עליה – אשר הן קהילת אלוהים שקנה במחיר דמו. 29אני יודע היטב שלאחר לכתי מכאן יופיעו ביניכם מורי שקר, אשר יהיו כזאבים אכזריים ולא יחוסו על העדר. 30אפילו אחדים מכם יסלפו את האמת כדי למשוך אחריהם תלמידים. 31לכן היזהרו! זכרו שבמשך שלוש שנים לא חדלתי להשגיח עליכם יומם ולילה, ואף שפכתי דמעות רבות בגללכם.

32”עתה אני מפקיד אתכם בידי אלוהים ודברו הנפלא, אשר בכוחו לבנות את אמונתכם ולתת לכם את הנחלה השמורה לבניו.

33”מעולם לא השתוקקתי לכסף או לבגדים יקרים. 34כולכם יודעים שבמו ידי עבדתי ופרנסתי את עצמי ואת בני־לוויתי. 35אתם גם יודעים שתמיד שימשתי לכם דוגמה בהגישי עזרה לעניים, משום שזכרתי את דברי אדוננו ישוע המשיח: מוטב לתת מאשר לקבל!“

36כשסיים פולוס את דבריו, כרע על ברכיו והתפלל איתם. 37כולם בכו בעת שחיבקו אותו ונשקו לו נשיקת פרידה. 38יותר מכל הם הצטערו על שאמר להם שלא ישובו לראותו. לאחר מכן ליוו אותו כולם אל האונייה.

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 20:1-38

Bulus ya ratsa Makidoniya da Giris

1Sa’ad da hayaniyar ta kwanta, sai Bulus ya aika a kira almajiran, kuma bayan ya ƙarfafa su, sai ya yi bankwana ya tafi Makidoniya. 2Ya ratsa wurin yana ƙarfafa mutanen da kalmomi masu yawa, a ƙarshe kuma ya kai Giris, 3inda ya zauna wata uku. Da yake Yahudawa sun ƙulla masa makirci, a lokacin da yake shirin tashi cikin jirgin ruwa zuwa Suriya, sai ya yanka shawara yă koma ta Makidoniya. 4Sai Sofater ɗan Fairrus daga Bereya, Aristarkus da Sekundus daga Tessalonika, Gayus daga Derbe, Timoti ma, da Tikikus da Turofimus daga lardin Asiya suka tafi tare da shi. 5Waɗannan mutane suka sha gaba suka kuma jira mu a Toruwas. 6Amma muka tashi daga Filibbi a jirgin ruwa bayan Bikin Burodi Marar Yisti bayan kuma kwana biyar muka sadu da sauran a Toruwas, inda muka zauna kwana bakwai.

Ta da Yutikus daga matattu a Toruwas

7A ranar farko ta mako muka taru wuri ɗaya don gutsuttsura burodi. Bulus ya yi wa mutane magana, don yana niyyar tashi kashegari, sai ya yi ta yin magana har tsakar dare. 8Akwai fitilu da yawa a ɗakin gidan saman da muka taru. 9Akwai wani saurayi zaune a taga mai suna Yitikus, wanda barci mai nauyi ya ɗauke shi yayinda Bulus yake ta tsawaita magana. Sa’ad da yake barci, sai ya fāɗi daga gidan sama a hawa ta uku aka kuma ɗauke shi matacce. 10Sai Bulus ya sauka, ya miƙe a kan saurayin ya rungume shi ya ce, “Kada ku damu, yana da rai!” 11Sai ya koma ɗakin da yake a gidan sama, ya gutsuttsura burodi ya kuma ci. Bayan ya yi magana har gari ya waye, sai ya tafi. 12Mutanen suka ɗauki saurayin da rai zuwa gida suka kuma ta’azantu ƙwarai da gaske.

Bankwanan Bulus ga dattawan Afisa

13Mu kuwa muka ci gaba zuwa jirgin ruwan muka tashi muka nufi Assos inda za mu ɗauki Bulus. Ya yi wannan shirin don zai tafi can da ƙafa. 14Da ya same mu a Assos, sai muka ɗauke shi a jirgin ruwan muka zo Mitilen. 15Kashegari muka tashi cikin jirgin ruwa daga can muka zo gefen Kiyos. Kwana ɗaya bayan wannan, sai muka ƙetare zuwa Samos, kashegari kuma muka iso Miletus. 16Bulus ya yanke shawara yă wuce Afisa a jirgin ruwa don kada yă ɓata lokaci a lardin Asiya, gama yana sauri yă kai Urushalima, in ya yiwu ma, a ranar Fentekos.

17Daga Miletus, Bulus ya aika zuwa Afisa a kira dattawan ikkilisiya. 18Da suka iso, sai ya ce musu, “Kun san irin zaman da na yi tun lokacin da na zauna da ku, daga ranar farkon da na zo cikin lardin Asiya. 19Na bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali’u har da hawaye, da gwagwarmaya iri-irin da na sha game da makircin Yahudawa. 20Kun san cewa ban yi wata-wata yin muku wa’azi game da duk abin da zai amfane ku ba amma na koyar da ku a fili da kuma gida-gida. 21Na yi shela ga Yahudawa da Hellenawa cewa dole su juye ga Allah cikin tuba su kuma amince da Ubangijinmu Yesu.

22“Yanzu kuma Ruhu ya tilasta ni, za ni Urushalima, ba tare da sanin abin da zai faru da ni a can ba. 23Na dai san cewa a kowace birni Ruhu Mai Tsarki yakan gargaɗe ni cewa kurkuku da shan wuya suna jirana. 24Amma ni ban ɗauki raina a bakin kome ba, in dai zan iya gama tserena in kuma kammala aikin da Ubangiji Yesu ya ba ni aikin shaida bisharar alherin Allah.

25“Yanzu na san cewa ba ko ɗaya daga cikinku wanda na zazzaga ina muku wa’azin mulkin Allah da zai sāke ganina. 26Saboda haka, ina muku shela a yau cewa ba ni da alhakin kowa a kaina. 27Gama ban yi wata-wata a sanar muku dukan nufin Allah ba. 28Ku lura da kanku da dukan garken da Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu kula da shi. Ku zama masu kiwon ikkilisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa. 29Na san cewa bayan na tafi, mugayen kyarketai za su shigo cikinku ba za su kuwa ƙyale garken ba. 30Ko cikinku ma mutane za su taso su karkatar da gaskiya don su jawo wa kansu almajirai. 31Saboda haka ku zauna a faɗake! Ku tuna cewa shekara uku, dare da rana ban taɓa fasa yin wa kowannenku gargaɗi ba, har da hawaye.

32“To, yanzu na danƙa ku ga Allah da kuma ga maganar alherinsa, wadda za tă iya gina ku ta kuma ba ku gādo a cikin dukan waɗanda aka tsarkake. 33Ban yi ƙyashin azurfa ko zinariya ko tufafin kowa ba. 34Ku kanku kun san cewa hannuwan nan nawa sun biya mini bukatuna da kuma na abokan aikina. 35Cikin kowane abin da na yi, na nuna muku cewa da irin wannan aiki tuƙuru don mu taimaki marasa ƙarfi, muna tunawa da kalmomin da Ubangiji Yesu kansa ya ce, ‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.’ ”

36Da ya faɗi haka, ya durƙusa tare da dukansu ya yi addu’a. 37Sai dukansu suka yi kuka suka rungume shi, suka kuma yi masa sumba. 38Abin da ya fi sa su baƙin ciki shi ne maganarsa da ya ce, ba za su ƙara ganin fuskarsa ba. Sai suka raka shi zuwa wajen jirgin ruwa.