מעשי השליחים 19 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

מעשי השליחים 19:1-41

1בזמן שאפולוס היה בקורינתוס עבר פולוס בכל רחבי אסיה הקטנה, וכשהגיע לאפסוס פגש תלמידים אחדים. 2”האם קיבלתם את רוח הקודש כשהאמנתם?“ שאל אותם.

”לא“, ענו. ”למה אתה מתכוון? מהו רוח הקודש?“

3”אם כן, באיזו טבילה נטבלתם?“ שאל פולוס. ”על עיקרי האמונה שלימד יוחנן המטביל“, השיבו התלמידים.

4”טבילתו של יוחנן באה רק להוכיח את הרצון לשוב מן החטא ולהאמין באלוהים,“ הסביר להם פולוס, ”ומי שנטבל חייב להאמין בישוע המשיח, שעל בואו ניבא יוחנן.“

5לשמע דברים אלה מיהרו התלמידים להיטבל בשם האדון ישוע המשיח. 6כשסמך פולוס את ידיו עליהם, צלח עליהם רוח הקודש והם החלו להתנבא ולדבר בשפות בלתי־מובנות. 7שנים־עשר איש נכחו באותו מעמד.

8במשך שלושת החודשים הבאים הלך פולוס מדי שבת לבית־הכנסת, הטיף באומץ לב על אמונתו, ושכנע אנשים רבים להאמין בישוע המשיח. 9אולם היו אנשים שדחו את בשורתו ודיברו בפומבי נגד ישוע. משום כך עזב פולוס את המקום וסרב לשוב ולדבר אליהם. הוא הוציא מתוכם את המאמינים המשיחיים, ולימד אותם מדי יום בבית־המדרש ”טורנוס“. 10הדבר נמשך כשנתיים, עד שכל אדם באסיה הקטנה – יהודי וגוי – שמע את בשורת ה׳. 11מה נפלאים היו הניסים שחולל אלוהים באמצעות פולוס! 12כאשר הונחו ממחטותיו או חולצותיו על החולים, נעלמו מיד המחלות, והרוחות הרעות עזבו אותם.

13מספר נוודים יהודים, אשר נדדו ממקום למקום וגירשו שדים ורוחות רעות, החליטו לנסות לגרש את השדים והרוחות בשם האדון ישוע. הם החליטו להשתמש בלחש הבא: ”בשם אותו ישוע שעליו מבשר פולוס, אני מצווה עליך לצאת!“ 14בין המלחשים האלה היו שבעת בניו של סקווה, שהיה אחד מראשי הכוהנים. 15אולם כשניסו להשתמש בלחש זה כדי לגרש שד מאדם אחד, השיב להם השד: ”אני מכיר את ישוע ואני מכיר את פולוס, אבל מי אתם?“ 16השד התנפל על שניים מהם והכה אותם נמרצות, עד שברחו מן הבית ההוא עירומים ופצועים.

17סיפור המעשה התפשט במהירות רבה בין היהודים והגויים בכל אפסוס. פחד גדול שרר בעיר, ושם ישוע המשיח זכה לכבוד ולהערצה. 18‏-19מאמינים רבים שעסקו לפנים במעשי כישוף למיניהם התוודו על מעשיהם בפומבי. הם הביאו את ספרי הכישופים ואת הקמעות שלהם, ושרפו אותם באש לעיני כולם (מישהו העריך את שווי הספרים האלה בכ־100,000 שקלים). 20מעשה זה של המאמינים הוכיח שדבר ה׳ חדר עמוק ללב האנשים באזור כולו.

21לאחר מאורעות אלה החליט פולוס לחצות את יוון בדרכו לירושלים. ”אחרי כן,“ אמר, ”עלי ללכת לרומא.“ 22הוא שלח לפניו ליוון את שני עוזריו, טימותיוס ואריסטוס, והוא עצמו נשאר בינתיים באסיה הקטנה.

23באותו זמן התפתחה באפסוס מהומה גדולה הקשורה במאמינים המשיחיים. 24המהומה החלה בגלל צורף בשם דמטריוס, אשר היה בעל מפעל לייצור דגמי כסף של מקדש האלילה היוונית ארטמיס. הוא העסיק פועלים רבים ושילם להם משכורת גבוהה. 25דמטריוס כינס את פועליו ופועלים אחרים שעסקו באותו מקצוע, ופנה אליהם:

”רבותי, מלאכה זאת היא כל פרנסתנו. 26אתם רואים ושומעים בעצמכם מה עושה פולוס זה. הוא הצליח לפתות אנשים רבים להאמין שאלילים מעשה ידי־אדם אינם אלוהים כלל, וכתוצאה מכך יורד היקף המכירות שלנו! הוא פיתה את האנשים לא רק באפסוס, כי אם בכל הארץ! 27אינני מדבר אך ורק על הצד העסקי של העניין, על אבדן הכנסתנו וקיפוח פרנסתנו; חשבו לרגע על הסכנה שבאבדן יוקרתה של האלה הגדולה ארטמיס! תוך זמן קצר לא יהיה כל ערך למקדשה של ארטמיס, אשר שמה יצא לתהילה לא רק בארצנו, אלא בעולם כולו!“

28דברים אלה עוררו את זעמם של הפועלים, והם החלו לצרוח: ”גדולה היא ארטמיס של האפסים!“

29עד מהרה הייתה מהומה ברחבי העיר. ההמונים תפסו את גיוס ואריסטרכוס ממקדוניה, שהיו מלוויו של פולוס, וגררו אותם אל האמפיתיאטרון כדי להעמידם לדין. 30פולוס רצה ללכת ולדבר אל ההמון, אולם התלמידים לא הניחו לו. 31אפילו מספר קצינים רומאים מהאזור, שהיו אוהדיו של פולוס, הזהירו אותו; הם הודיעו לו שלא יסכן את חייו ושלא יעז ללכת לאמפיתיאטרון.

32בתוך האמפיתיאטרון הייתה מהומה; זה צועק דבר אחד, וזה צועק דבר אחר; איש לא שמע את דברי רעהו. למעשה רוב האנשים לא ידעו כלל מדוע התאספו שם!

33אחדים הגיעו למסקנה שאלכסנדר היה אשם בכל, מפני שהיהודים דחפו אותו קדימה. אלכסנדר הניף את ידו וביקש שקט, כדי שיוכל לדבר. 34אולם משנוכח הקהל לדעת שהוא יהודי, החלו כולם לצעוק: ”גדולה היא ארטמיס של האפסים! גדולה היא ארטמיס של האפסים!“ צעקותיהם נמשכו שעתיים שלמות.

35בסופו של דבר הצליח מזכיר העיר להשתיק את ההמון הזועם. ”אנשי אפסוס,“ פתח ואמר, ”הרי כל אחד יודע שאפסוס היא המרכז הדתי של פולחן האלה הגדולה ארטמיס, אשר הפסל שלה ירד אלינו מהשמים. 36הואיל ואיש אינו חולק על עובדה זאת, עליכם להירגע ולא לנהוג בפזיזות ובקלות ראש! 37אתם הבאתם הנה אנשים אשר לא שדדו דבר ממקדשה של ארטמיס, ואף לא חיללו את כבודה. 38אם לדמטריוס ולפועליו יש טענות נגדם, שיתבעו אותם לדין! הרי בתי־הדין שלנו פתוחים לקהל בשעות הרגילות, והשופטים יכולים לדון בעניין ללא דיחוי. 39אם יש לכם תלונות בעניינים אחרים, עליכם לנהוג לפי המקובל ולהביא אותן לפני מועצת העיר. 40כולנו נמצאים עתה בסכנה, כי הממשל הרומאי עלול לדרוש מאיתנו דין וחשבון על ההתפרעות הזאת, שאין לה שום הצדקה. ואם הממשל ידרוש הסבר, לא יהיה לנו מה לומר!“ 41כשסיים לדבר, שלח את ההמונים לבתיהם.

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 19:1-41

Bulus a Afisa

1Lokacin da Afollos yake a Korint, Bulus ya bi hanyar da ta ratsa ta Asiya ya zo Afisa. A can ya sadu da waɗansu almajirai, 2sai ya tambaye, su ya ce, “Kun karɓi Ruhu Mai Tsarki sa’ad da kuka gaskata?”

Suka amsa suka ce, “A’a, ba mu ma san akwai Ruhu Mai Tsarki ba.”

3Saboda haka Bulus ya yi tambaya ya ce, “To, wace baftisma aka yi muku?”

Suka ce, “Baftismar Yohanna.”

4Bulus ya ce, “Ai, baftismar Yohanna, baftisma ce ta tuba. Ya ce wa mutane su gaskata a wani wanda yake zuwa bayansa, wato, Yesu.” 5Da ji wannan, sai aka yi musu baftisma a cikin sunan Ubangiji Yesu. 6Da Bulus ya ɗibiya musu hannuwansa, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauka musu, suka kuwa yi magana da harsuna, suka kuma yi annabci. 7Mutane kuwa su wajen mutum goma sha biyu ne.

8Bulus ya shiga majami’a ya yi magana gabagadi a can na watanni uku, yana muhawwara yana kuma rinjayarsu game da mulkin Allah. 9Amma waɗansunsu suka taurara; suka ƙi su gaskata kuma a gaban jama’a suka yi baƙar magana game da Hanyar. Bulus kuwa ya bar su. Ya tafi tare da almajirai ya dinga tattaunawa da su kullum a babban ɗakin jawabi na Tirannus. 10Wannan ya ci gaba har shekara biyu, sai da ya sa dukan Yahudawa da Hellenawa da suke zaune a lardin Asiya suka ji maganar Ubangiji.

11Allah ya yi ayyukan banmamakin da suka wuce misali ta hannu Bulus, 12har ma ana kai hankicif da adikan da suka taɓa jikinsa wa marasa lafiya, suka kuwa warke daga cututtukansu mugayen ruhohi kuma suka rabu da su.

13Waɗansu Yahudawa masu yawo gari-gari suna fitar da mugayen ruhohi suka yi ƙoƙari su yi amfani da sunan Ubangiji Yesu a kan waɗanda suke da aljanu. Suna cewa, “A cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa’azi, na umarce ku, ku fito.” 14’Ya’ya bakwai maza na Sikeba, wani babban firist na Yahudawa, suna yin haka. 15Wata rana mugun ruhu ya amsa musu ya ce, “Yesu kam na sani, Bulus kuma na sani, amma ku kuma su wane ne?” 16Sai mutumin da yake da mugun ruhun ya fāɗa musu ya sha ƙarfinsu duka. Ya yi musu dūkan tsiya har suka fita a guje daga gidan tsirara jini yana zuba.

17Da Yahudawa da Hellenawan da suke zama a Afisa suka ji wannan labari sai duk tsoro ya kama su, aka kuwa darjanta sunan Ubangiji Yesu ƙwarai. 18Da yawa cikin waɗanda suka gaskata yanzu suka zo a fili suka furta mugayen ayyukansu. 19Waɗansu masu yin sihiri suka kawo naɗaɗɗun littattafansu wuri ɗaya suka kuwa ƙone su a gaban jama’a. Sa’ad da aka lissafta yawan kuɗin naɗaɗɗun littattafan nan, sai jimillar ta kai darik dubu hamsin. 20Ta haka maganar Ubangiji ta bazu ko’ina ta kuma yi ƙarfi.

21Bayan dukan wannan ya faru, sai Bulus ya yanke shawara ya ratsa Makidoniya da Akayya in za shi Urushalima. Ya kuma ce, “Bayan na tafi can, dole in ziyarci Roma ita ma.” 22Sai ya aiki biyu daga cikin masu taimakonsa, Timoti da Erastus, zuwa Makidoniya, yayinda shi kuwa ya ɗan dakata a lardin Asiya.

Hargitsi a Afisa

23Kusan wannan lokaci sai aka yi wani babban hargitsi game da wannan Hanyar. 24Wani maƙerin azurfa, mai suna Demetiriyus wanda yake ƙera siffar ɗakunan tsafin Artemis da azurfa, ba ƙaramin ciniki yake kawo wa mutane masu sana’an nan ba. 25Sai ya tara su wuri ɗaya, tare da masu irin wannan sana’ar ya ce, “Ku jama’a, kun san muna samun kuɗin shiga sosai daga wannan sana’a. 26Kuma kuna ji kuna gani yadda Bulus ɗin nan ya shawo kan mutane da yawa ya kuma sa suka bauɗe a nan a Afisa da dukan lardin Asiya. Yana cewa alloli da mutum ya ƙera ba alloli ba ne ko kaɗan. 27Akwai hatsari, ba kawai cewa sana’armu za tă rasa sunanta mai daraja ba, amma za a yi banza da ɗakin tsafin Artemis alliyarmu mai girma, alliyar kanta wadda ake bauta a ko’ina a yankin Asiya da kuma duniya, za a raba ta da darajarta.”

28Da suka ji haka, sai suka yi fushi ƙwarai suka fara ihu suna cewa, “Girma ta tabbata ga Artemis ta Afisawa!” 29Jim kaɗan sai hayaniya ta tashi a dukan birnin. Sai mutane suka cafke Gayus da Aristarkus, abokan tafiyar Bulus daga Makidoniya, suka ruga da zuwa fili da nufi ɗaya. 30Bulus ya so ya bayyana a gaban taron, amma almajirai ba su bar shi ba. 31Har waɗansu shugabannin lardin ma, abokan Bulus, suka aika masa suna roƙonsa kada yă kuskura ya shiga filin nan.

32Taron kuwa ya ruɗe. Waɗansu suna ihu suna ce abu kaza, waɗansu kuma wani abu dabam. Yawancin mutane kuma ba su ma san abin da ya sa suke a wurin ba. 33Yahudawa suka tura Alekzanda gaba, sai waɗansu a taron suka riƙa yin masa ihu. Sai ya ɗaga hannu don a yi shiru don yă kāre kansa a gaban mutane. 34Amma sa’ad da suka gane shi mutumin Yahuda ne, sai duk suka yi ihu gaba ɗaya na kusa sa’a biyu, suna cewa, “Girma ta tabbata ga Artemis ta Afisawa!”

35Sai magatakardar birnin ya sa taron su yi shiru, sa’an nan ya ce, “Mutanen Afisa, ashe duk duniya ba tă san cewa birnin Afisa ce mai lura da haikalin Artemis mai girma da kuma siffarta da ya fāɗi daga sama ba? 36Saboda haka, da yake ba dama a yi mūsun wannan gaskiya, ya kamata ku natsu kada ku yi kome da garaje. 37Kun kawo mutanen nan a nan, gashi kuwa ba su yi fashin haikali ba, ba su kuwa saɓa wa alliyarmu ba. 38To, in haka ne, in Demetiriyus da abokan sana’arsa suna da wata magana game da wani ai, kotuna suna nan a buɗe, akwai kuma muƙaddasai. Suna iya kai ƙara. 39In kuma akwai wani abu har yanzu da kuke so ku kawo, dole a daidaita shi a majalisa. 40Yadda yake a yanzu, muna a hatsarin amsa zargin ta da hargitsi saboda abin da ya faru yau. Da yake ba za mu iya ba da dalilin da ya sa aka yi wannan hargitsi ba.” 41Bayan da ya faɗi haka, sai ya sallami taron.