הבשורה על-פי יוחנן 17 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי יוחנן 17:1-26

1בסיימו לדבר נשא ישוע את עיניו השמימה ואמר: ”אבי, הגיעה השעה; פאר את בנך כדי שבנך יפאר אותך. 2הרי נתת לו סמכות וכוח על כל בני־האדם, כדי שיעניק חיי עולם לכל מי שנתת לו. 3חיי עולם פירושם להכיר אותך, אלוהי האמת לבדו, ואת ישוע המשיח אשר שלחת. 4סיימתי את המשימה שהטלת עלי, וכך פארתי אותך על־פני הארץ. 5עתה, אבי, פאר אותי בכבוד שהיה לי איתך עוד לפני בריאת העולם.

6”סיפרתי על אודותיך לכל האנשים שנתת לי בעולם. למעשה הם היו שלך תמיד; אתה נתת לי אותם והם שמעו בקולך. 7עתה הם יודעים שכל מה שנתת לי ממך הוא, 8כי מסרתי להם את המצוות שמסרת לי. הם קיבלו אותן, והם יודעים בבטחון שבאתי לעולם מעמך ושאתה שלחת אותי.

9”איני מתפלל בעד העולם כולו, אלא בעד אלה שנתת לי, כי הם שייכים לך. 10אלה שהם שלי הם שלך, ושלך הם שלי, ולכן הם תפארתי. 11כעת אני עוזב את העולם ומשאיר אותם כאן. אבי הקדוש, אני בא אליך ומבקש ממך: שמור על כל אלה שנתת לי, כדי שיתאחדו ויהיו לאחד – כמונו. 12בהיותי כאן בעולם שמרתי על אלה שנתת לי אך אחד מהם לא אבד, מלבד בן־הגיהינום שבו נתקיימה הנבואה שבכתבי־הקודש.

13”עכשיו אני בא אליך. סיפרתי להם דברים רבים בהיותי עמם, כדי שיימלאו בשמחתי, 14ומסרתי להם את מצוותיך. העולם שונא אותם, כי אינם שייכים לו, כשם שאני איני שייך לעולם. 15אני לא מבקש ממך להוציא אותם מהעולם, אלא לשמרם מהרע. 16הם אינם שייכים לעולם הזה, כשם שאני איני שייך לעולם הזה. 17למד אותם את דבר האמת, כדי שיהיו קדושים וטהורים. 18כשם ששלחת אותי אל העולם כך גם אני שולח אותם אל העולם. 19אני מוסר את עצמי למענם, כדי שיגדלו באמת ובקדושה.

20”אינני מתפלל רק בעד אלה כאן, אלא גם בעד אלה שיאמינו בי בעתיד, לאחר שישמעו את עדויות המאמינים. 21אני מתפלל שהם יהיו מאוחדים כמונו; שהם יהיו בנו כשם שאתה בי ואני בך, כדי שהעולם יאמין שאתה שלחת אותי.

22”נתתי להם את הכבוד שנתת לי, כדי שיהיו מאוחדים כשם שאנחנו מאוחדים – 23אני בהם ואתה בי, כדי שאחדותם תהיה שלמה, וכדי שהעולם ידע שאתה שלחתני ושאתה אוהב אותם כמו שאתה אוהב אותי. 24אבי, אני רוצה שאלה אשר נתת לי יהיו במקום שבו אהיה, כדי שיוכלו לראות את התפארת והכבוד שהענקת לי על שום שאהבת אותי עוד לפני בריאת העולם.

25”הו, אבי הצדיק, העולם אינו מכיר אותך, אבל אני מכיר אותך, והתלמידים שנתת לי יודעים שאתה שלחתני. 26אני הודעתי להם את שמך, ואוסיף להודיע, כדי שהם יאהבו אותי כשם שאתה אוהב אותי וכדי שגם אני אהיה בהם.“

Hausa Contemporary Bible

Yohanna 17:1-26

Yesu ya yi addu’a

1Bayan da Yesu ya faɗi wannan, sai ya dubi sama ya yi addu’a ya ce,

“Uba, lokaci ya yi. Ka ɗaukaka Ɗanka, don Ɗanka yă ɗaukaka ka. 2Gama ka ba shi iko bisa dukan mutane domin yă ba da rai madawwami ga duk waɗanda ka ba shi. 3Rai madawwami kuwa shi ne, su san ka, Allah makaɗaici mai gaskiya, da kuma Yesu Kiristi, wanda ka aiko. 4Na ɗaukaka ka a duniya ta wurin gama aikin da ka ba ni. 5Yanzu ya Uba, ka ɗaukaka ni a gabanka da ɗaukakar da dā nake da ita tun kafin a kafa duniya.

Yesu ya yi addu’a saboda almajiransa

6“Na bayyana ka ga waɗanda ka ba ni a duniya. Su naka ne; kai ka ba ni su sun kuma yi biyayya da maganarka. 7Yanzu sun san cewa duk abin da ka ba ni daga gare ka ya fito. 8Na ba su kalmomin da ka ba ni sun kuwa karɓa. Sun san tabbatacce daga wurinka na fito. Sun kuma gaskata kai ka aiko ni. 9Ina addu’a dominsu. Ba domin duniya nake addu’a ba, amma domin waɗanda ka ba ni, gama su naka ne. 10Duk abin da nake da shi naka ne, kuma duk abin da kake da shi nawa ne. Na kuwa sami ɗaukaka ta wurinsu. 11Ba sauran zamana a duniya, amma waɗannan a duniya suke, ni kuwa ina zuwa wurinka. Ya Uba Mai Tsarki, ka kiyaye su ta wurin ikon sunanka, sunan da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya. 12Yayinda nake tare da su, na kāre su na kuma kiyaye su ta wurin sunan nan da ka ba ni. Ba ko ɗayan da ya ɓace, sai dai wannan da aka ƙaddara zuwa ga hallaka don Nassi yă cika.

13“Yanzu ina zuwa wurinka, sai dai na faɗi waɗannan abubuwa ne tun ina a duniya domin farin ciki yă zama cikakke a cikinsu. 14Na gaya musu maganarka duniya kuwa ta ƙi su, don su ba na duniya ba ne yadda ni ma ba na duniya ba ne. 15Ba addu’ata ba ce ka ɗauke su daga duniya ba, sai dai ka kāre su daga mugun nan. 16Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ma ba na duniya ba ne. 17Ka tsarkake su ta wurin gaskiya; maganarka ce gaskiya. 18Kamar yadda ka aiko ni cikin duniya, haka ni ma na aike su cikin duniya. 19Saboda su ne na tsarkake kaina, domin su ma a tsarkake su da gaske.

Yesu ya yi addu’a saboda dukan masu bi

20“Addu’ata ba saboda masu bina kaɗai ba ne. Ina addu’a kuma saboda waɗanda za su gaskata da ni ta wurin maganarsu. 21Ina so dukansu su zama ɗaya, ya Uba, kamar yadda kake a cikina, ni kuwa a cikinka. Haka su ma bari su zauna cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa kai ka aiko ni. 22Na ba su ɗaukakar da ka ba ni, don su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya. 23Ni a cikinsu kai kuma a cikina. Bari su kasance da cikakken haɗinkai, domin duniya ta san cewa kai ka aiko ni. Ka kuwa ƙaunace su yadda ka ƙaunace ni.

24“Uba, ina so waɗanda ka ba ni su kasance tare da ni a inda nake, su kuma ga ɗaukakata, ɗaukakar da ka ba ni domin kana ƙaunata kafin halittar duniya.

25“Ya Uba Mai Adalci, ko da yake duniya ba tă san ka ba, ni na san ka, sun kuma san kai ka aiko ni. 26Na bayyana ka a gare su, zan kuma ci gaba da bayyana ka domin ƙaunar da ka yi mini ta kasance a cikinsu ni ma in kasance a cikinsu.”