אגרת פולוס הראשונה אל-הקורנתים 8 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

אגרת פולוס הראשונה אל-הקורנתים 8:1-13

1שאלתכם הבאה הייתה בנוגע לאכילת מזון שהוקרב לאלילים. כל אחד מכם חושב שהוא לבדו יודע את התשובה לבעיה זו, אך דעו לכם שחשיבות עצמית רק מוסיפה לנו גאווה, ואילו כדי לבנות את הקהילה אנו זקוקים לאהבה ולא לגאווה. 2אדם שחושב שהוא יודע את כל התשובות רק מוכיח את בורותו. 3ואילו אדם האוהב את אלוהים באמת, מוכן תמיד לשמוע בקולו ולהקשיב לדבריו, ובכך ניכר בו חותם אלוהים.

4באשר לעצם השאלה אם מותר לנו לאכול מזון שהוקרב לאלילים, כולנו יודעים שאליל אינו אל אמיתי, וכי יש רק אל אחד ויחיד. 5יש אנשים המאמינים בקיומם של אלים רבים בשמים ובארץ. 6אבל אנחנו יודעים שיש רק אל אחד – הלא הוא אבינו שבשמים, אשר ברא את הכול ובחר בנו להיות ילדיו; ויש רק אדון אחד – הלא הוא ישוע המשיח, אשר עשה את הכול ואף העניק לנו את חיינו.

7מאמינים רבים עדיין אינם מבינים זאת. הם תמיד חשבו את האלילים ליצורים חיים, ומשום כך חשבו כי המזון שהוקרב לאלילים הוקרב לאל חי ואמיתי. מסיבה זאת מציק להם מצפונם בשעה שהם אוכלים מזון זה. 8לאלוהים אין זה משנה אם אנו אוכלים מזון שהוקרב לאלילים או לא; אכילתו אינה מוסיפה לנו ואינה גורעת מאיתנו. 9אך היזהרו שהרשות שיש לכם לאכול לא תהיה מכשול למאמין אחר שמצפונו חלש משלכם. 10כי אח החושב שאסור לאכול מזון כזה עלול לראותך סועד בבית־אלילים, וגם הוא יאזור אומץ ויאכל מזון זה, אך מצפונו יציק לו. 11וכך, מאחר שאתה יודע כי מותר לך לאכול מזון זה, תגרום נזק רוחני רב לאח בעל מצפון חלש, (שאינו יודע כי מותר לו לאכול) ואל תשכח שהמשיח מת גם בעדו. 12לפיכך, אם אתה מעודד את אחיך לעשות מעשה הנחשב בעיניו לחטא, אתה חוטא נגד ישוע המשיח. 13על כן אם אכילת מזון שהוקרב לאלילים נחשבת לחטא בעיני אחי, לא אוכל מזון זה כל חיי, כי איני רוצה להכשילו.

Hausa Contemporary Bible

1 Korintiyawa 8:1-13

Abincin da aka miƙa wa gumaka

1To, game da abincin da aka miƙa hadaya ga gumaka kuwa. Mun san cewa dukanmu muna da ilimi. Ilimi yakan kawo girman kai, amma ƙauna takan gina. 2Mutumin da yake tsammani ya san abu, sanin da yake da shi bai isa ba. 3Amma mutumin da yake ƙaunar Allah, Allah yana sane da shi.

4To, game da cin abincin da aka miƙa hadaya ga gumaka kuwa, mun san cewa “Gunki ba kome ba ne a duniya”, kuma “Babu wani Allah sai dai ɗaya.” 5Gama ko da akwai abubuwan da ake ce da su alloli, a sama ko a ƙasa (don kuwa akwai “alloli” da “iyayengiji” da yawa), 6duk da haka a gare mu dai akwai Allah ɗaya kaɗai, Uba, wanda dukan abubuwa suke daga gare shi, wanda kuma saboda shi ne muke rayuwa, kuma akwai Ubangiji ɗaya, Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa ne aka yi dukan abu, ta wurinsa ne kuma muke rayuwa.

7Amma ba kowa ne ya san wannan ba. Har yanzu, waɗansu mutane sun saba da tunani cewa gumaka ainihi ne, saboda haka sa’ad da suka ci irin abincin nan, sukan ɗauka cewa kamar an miƙa wa ga gunki ne, kuma da yake lamirinsu ba ƙarfi, yakan ƙazantu. 8Gaskiya ne cewa ba ma samun yardar Allah ta wurin abin da muke ci. Ba ma rasa wani abu idan ba mu ci ba, kuma ba ma ƙaru da wani abu in muka ci.

9Sai dai ku yi hankali, kada yin amfani da ’yancinku yă zama abin sa tuntuɓe ga marasa ƙarfi. 10Gama in wani wanda lamirinsa ba shi da ƙarfi ya gan ka, kai da kake da wannan sani, kana ci a haikalin gumaka, ashe, ba zai sami ƙarfin halin cin abin da aka miƙa wa gumaka ba? 11Saboda haka ta wurin sanin nan naka sai ka sa wannan ɗan’uwa marar ƙarfi wanda Kiristi ya mutu dominsa yă hallaka. 12Sa’ad da ka rushe lamiri mai bi marar ƙarfi, ka yi wa Kiristi zunubi ke nan. 13Saboda haka, in abin da nake ci zai sa ɗan’uwana yă yi zunubi, ba zan ƙara cin nama ba, don kada in sa shi yă yi tuntuɓe.