אגרתו הראשונה של יוחנן השליח 3 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

אגרתו הראשונה של יוחנן השליח 3:1-24

1ראו מה רבה אהבת אלוהים אלינו – הוא אף קרא לנו ”בני אלוהים“! ואין זה כינוי בלבד, אלא עובדה. לצערי, אנשים רבים אינם מאמינים באלוהים, ועל כן אינם מבינים כיצד אנו יכולים להיות בניו. 2אחי היקרים, עכשיו אנחנו בני אלוהים; איננו יודעים עדיין מה נהיה בעתיד, אנחנו רק יודעים שבבוא המשיח נהיה כמוהו, כי נראהו פנים אל פנים. 3כל המחזיק בתקווה זאת צריך להישאר טהור ונקי מחטא, כי המשיח עצמו טהור ונקי.

4מי שחוטא, חוטא נגד אלוהים, כי כל חטא נָעָשָה נגד תורת אלוהים. 5אתם הרי יודעים שהוא בא אלינו בדמות אדם, כדי לקחת על עצמו את העונש על חטאינו, למרות שבו לא היה חטא. 6אם נתמיד באמונתנו, נשמע בקולו ונעשה את הטוב בעיניו, לא נחטא. הממשיכים לחטוא חוטאים מסיבה פשוטה: הם מעולם לא האמינו במשיח ולא אהבו אותו.

7בני היקרים, אל תניחו לאיש לרמותכם. העושה מעשים טובים עושה אותם משום שהוא עצמו טוב – כמו המשיח ובזכותו. 8והעושה מעשים רעים מוכיח שהוא שייך לשטן – החוטא הראשון בעולם, שממשיך עדיין במעשיו הרעים – שכן בן־האלוהים בא לבטל את פעולות השטן. 9בני־אלוהים אינם חוטאים יותר מתוך הרגל, מכיוון שאלוהים האב נתן להם חיים וטבע חדש; הם אינם יכולים להמשיך בהרגל החטא.

10כיצד יכולים אנו להבדיל בין ילדי אלוהים לבין ילדי השטן? כל מי שחי חיי חטא ואינו אוהב את אחיו, אינו שייך למשפחת אלוהים. 11שהרי כבר מבראשית מסר לנו אלוהים את המצוה: אהבו איש את רעהו.

12אל לנו להידמות לקין, הורג אחיו, אשר השתייך לשטן. מדוע הרג את אחיו? מפני שקין עשה מעשים רעים, וידע היטב שחיי הבל אחיו היו טובים משלו. 13לכן, אחים יקרים, אל תתפלאו אם העולם שונא אתכם.

14אם אנחנו אוהבים את אחינו המאמינים, אנו יודעים שעברנו ממוות לחיים. בעוד שאדם אשר אין בו אהבה עדיין מת. 15כל השונא את אחיו רוצח אותו בלבו, ואתם יודעים שלרוצחים אין חיי נצח! 16מהי אהבה אמיתית? קורבנו של המשיח! כשם שהקריב את חייו למעננו, כך עלינו להקריב את חיינו למען אחינו.

17אדם הנקרא מאמין משיחי, ויש לו מספיק כסף, אך אין הוא עוזר לאחיו העני הנתון במצוקה, אהבת אלוהים אינה שוכנת בו. 18בני היקרים, הבה נפסיק לדבר על אהבת איש את רעהו; הבה נאהב באמת ונוכיח את אהבתנו במעשים. 19כך נדע בוודאות שאנו שייכים לאלוהים, וכאשר נעמוד לפניו יהיה מצפוננו נקי ושקט. 20אך אם חטאנו ומצפוננו מציק לנו, אלוהים יודע בדיוק מה עשינו וכיצד אנו מרגישים.

21ידידי היקרים, אם מצפוננו נקי אנו יכולים לבוא לפני אלוהים בביטחון מלא, 22והוא ייתן לנו כל מה שנבקש ממנו, שכן אנו שומעים בקולו ועושים את הטוב בעיניו. 23הזוכרים אתם מה ציווה עלינו אלוהים? להאמין בשם ישוע המשיח בנו ולאהוב איש את רעהו. 24כל השומע בקול אלוהים ומקיים את מצוותיו, חי באלוהים ואלוהים חי בו. כיצד אנו יודעים זאת? רוח הקודש השוכן בקרבנו מאשר את הדבר.

Hausa Contemporary Bible

1 Yohanna 3:1-24

1Dubi irin ƙaunar da Uba ya ƙaunace mu da ita mana, har ana ce da mu ’ya’yan Allah! Haka kuwa muke! Dalilin da ya sa duniya ba tă san mu ba shi ne, don ba tă san shi ba. 2Abokaina ƙaunatattu, yanzu, mu ’ya’yan Allah ne, kuma abin da za mu zama nan gaba ba a riga an bayyana ba. Sai dai mun san cewa sa’ad da Kiristi ya bayyana, za mu zama kamar sa, domin za mu gan shi kamar yadda yake. 3Duk mai wannan bege a cikinsa yakan tsarkake kansa, kamar yadda shi Kiristi yake da tsabta.

4Duk mai yin zunubi yana karya doka ne; tabbatacce, zunubi, karya doka ne. 5Sai dai kun san cewa Kiristi ya bayyana ne domin yă ɗauke zunubanmu. A cikinsa kuwa babu zunubi. 6Ba mai rayuwa a cikinsa da yake cin gaba da yin zunubi. Kowa da yake aikata zunubi, bai taɓa ganinsa ba, bai ma san shi ba.

7’Ya’yana ƙaunatattu, kada ku yarda wani yă ruɗe ku. Duk mai yin abin da yake daidai mai adalci ne, yadda Kiristi yake mai adalci. 8Duk mai aikata abin da yake zunubi shi na Iblis ne, domin Iblis mai aikata zunubi ne tun farko. Dalilin da ya sa Ɗan Allah ya bayyana kuwa shi ne don yă rushe aikin Iblis. 9Babu haifaffe na Allah da zai ci gaba da yin zunubi, domin iri na Allah yana a cikinsa; ba zai iya ci gaba da yin zunubi ba, domin haifaffe ne na Allah. 10Ta haka muka san waɗanda suke ’ya’yan Allah da kuma waɗanda suke ’ya’yan Iblis. Duk wanda ba ya yin abin da yake daidai, ba ɗan Allah ba ne; haka ma wanda ba ya ƙaunar ɗan’uwansa.

Ku ƙaunaci juna

11Wannan shi ne saƙon da kuka ji tun farko. Ya kamata mu ƙaunaci juna. 12Kada ku zama kamar Kayinu, wanda ya zama na mugun nan, ya kuma kashe ɗan’uwansa. Me ya sa ya kashe shi? Domin ayyukansa mugaye ne, na ɗan’uwansa kuma na adalci ne. 13Kada ku yi mamaki ’yan’uwana, in duniya ta ƙi ku. 14Mun san cewa mun riga mun ratsa daga mutuwa zuwa rai, domin muna ƙaunar ’yan’uwanmu. Duk wanda ba ya ƙauna matacce ne har yanzu. 15Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa.

16Yadda muka san ƙauna ke nan, wato, Yesu Kiristi ya ba da ransa dominmu. Ya kamata mu ma mu ba da rayukanmu domin ’yan’uwanmu. 17In wani yana da arziki, ya kuma ga ɗan’uwansa cikin rashi, bai kuwa taimake shi ba, anya, ƙaunar Allah tana a cikinsa kuwa? 18’Ya’yana ƙaunatattu, kada mu yi ƙauna da fatar baki kawai, sai dai mu nuna ta ta wurin aikatawa da kuma gaskiya.

19Ta haka muka san cewa mu na gaskiya ne, kuma za mu iya tsaya a gaban Allah ba tare da rawar jiki ba. 20Idan zuciyarmu ta nuna mana muna da laifi, mun san cewa Allah ya fi zuciyarmu, ya kuma san dukan kome. 21Abokaina ƙaunatattu, in zukatanmu ba su ba mu laifi ba, muna da ƙarfin halin tsayawa a gaban Allah ke nan. 22Muna kuma samun dukan abin da muka roƙa daga gare shi, domin muna biyayya da umarnansa, muna kuma yin abin da ya gamshe shi. 23Umarninsa kuwa shi ne, mu gaskata da sunan Ɗansa, Yesu Kiristi, mu kuma ƙaunaci juna kamar yadda ya umarce mu. 24Waɗanda suke biyayya da umarnansa kuwa suna rayuwa a cikinsa, shi kuma a cikinsu. Ta haka muka san cewa yana raye a cikinmu. Mun san haka ta wurin Ruhun da ya ba mu.