אגרתו הראשונה של יוחנן השליח 2 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

אגרתו הראשונה של יוחנן השליח 2:1-29

1בני היקרים, אני כותב לכם דברים אלה כדי שלא תחטאו. אך אם תחטאו, דעו לכם שיש לנו סנגור לפני אלוהים – ישוע המשיח הצדיק! 2ישוע המשיח הוא כפרה על חטאינו ועל חטאי העולם כולו; הוא נשא על עצמו את עונשו של ה׳ על החטאים שלנו.

3אם אנחנו משתדלים מאוד לעשות כל מה שהוא אומר לנו, אנחנו יודעים שאנו באמת שייכים לו.

4אם מישהו טוען: ”אני מאמין בישוע המשיח!“ אך אינו שומע בקולו, הוא שקרן. 5מי שבאמת מאמין במשיח ושומע בקולו, ילמד לאהוב את אלוהים יותר ויותר. 6אם מישהו טוען שהוא מאמין במשיח, עליו לחיות כמוהו.

7אחים יקרים, איני כותב לכם מצווה חדשה; אני מזכיר לכם מצווה ישנה שציווה לכם אלוהים מבראשית. אף כי שמעתם אותה פעמים רבות 8היא תמיד חדשה ורעננה, ואף הוכיחה את אמיתותה במשיח ובנו. כשאנו מקיימים את המצווה לאהוב איש את רעהו, החטא והחשכה נעלמים מחיינו, ובמקומם זורח אורו של ישוע המשיח.

9האומר שהוא חי באור המשיח, אך שונא את חברו, הוא עדיין בחשכה. 10האוהב את חברו חי באור המשיח, אשר מאיר את דרכו ושומר עליו שלא ייכשל. 11ואילו השונא את חברו הוא בְחשכה רוחנית המעוורת את עיניו, ומשום כך אינו יודע לאן הוא הולך.

12בני היקרים, אני כותב לכם דברים אלה מפני שחטאיכם נסלחו לכם בשם ישוע המשיח מושיענו ולמענו.

13אני כותב לכם, האבות בָאמונה, כי אתם באמת יודעים ומכירים את המשיח אשר חי מבראשית.

אני כותב לכם, הצעירים באמונה, מפני שהתגברתם על פיתויי השטן.

14ילדי היקרים, כתבתי לכם מפני שאתם יודעים ומכירים את האלוהים אבינו.

כתבתי לכם, האבות, מפני שאתם מכירים את אלוהי הנצח.

כתבתי לכם, הצעירים, מפני שאתם חזקים, דבר־אלוהים שוכן בכם ואף התגברתם על פיתויי השטן.

15אל תאהבו את העולם הנתעב הזה ואת כל מה שהוא מציע. אם אתם אוהבים את העולם הרי שאינכם אוהבים באמת את אלוהים. 16מה כבר מסוגל העולם להציע לכם? תאוות הבשר, תאוות העיניים וגאוות החיים! דברים אלה אינם מאלוהים; מקורם בעולם המרושע הזה. 17דעו לכם, יבוא יום שכל העולם הזה יחלוף על חטאיו, אך כל השומע בקול ה׳ יחיה לנצח. 18ילדים יקרים, שמעתם כי שונא־המשיח2‏.18 ב 18 הכוונה לצורר המשיח – משיח שקר. עומד לבוא. היודעים אתם שבכל מקום כבר הופיעו שונאים רבים למשיח? עובדה זאת מאשרת שקץ העולם קרב. 19שונאי המשיח היו בעבר גם בין חברי קהילתנו, אך אין ספק שמעולם לא היו חלק מאיתנו, אחרת היו נשארים. עזיבתם הוציאה לאור את האמת.

20אבל אתם שונים מהם, כי רוח הקודש שוכן בקרבכם ואתם יודעים את האמת.

21כתבתי לכם כל זאת לא משום שאינכם יודעים את האמת, אלא להיפך: כתבתי לכם משום שאתם יודעים את האמת, ויודעים להבחין בין שקר לאמת.

22היודעים אתם מיהו השקרן הגדול ביותר? האומר שישוע אינו המשיח. אדם כזה שונא המשיח הוא, שכן אינו מאמין באלוהים האב ובבנו. 23הרי אדם המתכחש למשיח בן־האלוהים, מתכחש בהכרח גם לאלוהים עצמו, בעוד שאדם שמאמין בישוע המשיח, מאמין גם באלוהים אביו.

24המשיכו להאמין ולעשות את אשר למדתם בהתחלה, כדי שתמיד תהיה לכם התחברות אמיתית ואיתנה עם אלוהים האב ועם בנו ישוע המשיח.

25זכרו, אלוהים עצמו הבטיח לנו חיי נצח.

26כתבתי לכם דברים אלה כדי להזהירכם מפני שונאי המשיח. הם יעשו הכול כדי לסנוור את עיניכם, לסלף את האמת ולהוליך אתכם שולל. 27אולם אלוהים השכין בכם את רוח הקודש שמלמד אתכם את האמת בלבד, ומשום כך אין לכם צורך מחייב במורה אחר כדי להראות לכם שאלה מורי שקר. על כן שמעו בקולו, התקרבו למשיח ואל תיפרדו ממנו לעולם.

28בני היקרים, היו נאמנים למשיח, כדי שלא תתביישו לפגוש אותו בבואו, אלא להיפך: תשמחו מאוד. 29מאחר שאנחנו יודעים כי אלוהים צדיק גמור, וכי הוא עושה רק את הנכון והצודק, נוכל להניח כי כל העושה את הנכון והצודק הוא ילדו.

Hausa Contemporary Bible

1 Yohanna 2:1-29

1’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci. 2Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.

3Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa. 4Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa. 5Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa. 6Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.

7Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji. 8Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.

9Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu. 10Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe. 11Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.

12Ina rubuta muku, ’ya’yana ƙaunatattu,

domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.

13Ina rubuta muku, ubanni,

domin kun san shi wanda yake tun farko.

Ina rubuta muku, samari,

domin kun ci nasara a kan mugun nan.

14Ina rubuta muku, ’ya’yana ƙaunatattu,

domin kun san Uba.

Ina rubuta muku, ubanni,

domin kun san shi wanda yake tun farko.

Ina rubuta muku, samari,

domin kuna da ƙarfi,

maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku,

kun kuma ci nasara a kan mugun nan.

Kada ku ƙaunaci duniya

15Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa. 16Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya. 17Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada.

Gargaɗi a kan magabcin Kiristi

18’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso. 19Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.

20Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya. 21Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya. 22Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan. 23Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.

24Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban. 25Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami.

26Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce. 27Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.

’Ya’yan Allah

28Yanzu fa, ya ku ’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.

29In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.