Romawa 2 – HCB & KJV

Hausa Contemporary Bible

Romawa 2:1-29

Shari’ar adalcin Allah

1Saboda haka, kai da kake ba wa wani laifi, ba ka da wata hujja, gama a duk lokacin da kake ba wa wani laifi, kana hukunta kanka ne, domin kai da kake ba wa wani laifi kai ma kana aikata waɗannan abubuwa. 2Yanzu mun san cewa hukuncin Allah a kan masu aikata waɗannan abubuwa daidai ne. 3Saboda haka sa’ad da kai mutum kurum, kana ba su laifi, duk da haka kana aikata abubuwan nan, kana tsammani za ka tsere wa hukuncin Allah ne? 4Ko kuma kana rena wadatar alherinsa, haƙurinsa, da kuma jimrewarsa ne ba tare da sanin cewa alherin Allah yana kai ka ga tuba ba ne?

5Amma saboda taurinkanka da zuciyarka marar tuba, kana tara wa kanka fushi a ranar fushin Allah, sa’ad da za a bayyana hukuncinsa mai adalci. 6Allah, “Zai sāka wa kowane mutum gwargwadon aikin da ya yi.”2.6 Zab 62.12; K Mag 24.12 7Ga waɗanda ta wurin naciya suna yin nagarta suna neman ɗaukaka, girma da rashin mutuwa, su za a ba su rai madawwami. 8Amma ga waɗanda suke sonkai waɗanda suke ƙin gaskiya suke kuma bin mugunta, akwai fushi da haushi dominsu. 9Akwai wahala da baƙin ciki ga duk mutumin da yake aikata mugunta, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai, 10amma akwai ɗaukaka, girma da salama ga duk mutumin da yake aikata alheri, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai. 11Gama Allah ba ya nuna bambanci.

12Duk waɗanda suka yi zunubi a rashi sanin doka, a rashin doka za su hallaka, waɗanda kuma suka yi zunubi ƙarƙashin doka, a ƙarƙashin doka za a hukunta su. 13Gama ba masu jin dokar ne suke da adalci a gaban Allah ba, amma waɗanda suke yin biyayya da dokar, su za a ce da su masu adalci. 14Tabbatacce, sa’ad da Al’ummai, waɗanda ba su da dokar, suka aikata abubuwan da dokar take bukata, abubuwan sun zama doka ke nan gare su, ko da yake ba su da dokar. 15To, da yake sun nuna cewa abubuwan da dokar take bukata suna a rubuce a zukatansu, lamirinsu yana kuma ba da shaida, tunaninsu kuwa yanzu yana zarginsu ko kuma yana kāre su. 16Wannan zai faru a ranar da Allah ta wurin Yesu Kiristi zai shari’anta ɓoyayyun abubuwan da mutane suka yi, yadda bisharata ta furta.

Yahudawa da doka

17To, kai, da kake kiran kanka mutumin Yahuda; in kana dogara ga doka kana kuma taƙama da dangantakarka da Allah; 18in ka san nufinsa ka kuma amince da abin da yake mafifici domin an koyar da kai bisa ga doka; 19in ka tabbata cewa kai jagora ne ga makafi, haske ga waɗanda suke cikin duhu, 20mai koyar da masu wauta, malamin jarirai, domin a cikin dokar ce akwai sani da gaskiya 21to, kai mai koya wa waɗansu, ba kanka kake koya wa ba? Kai da kake wa’azi kada a yi sata, kana sata? 22Kai da kake cewa wa mutane kada su yi zina, kana yin zina? Kai da kake ƙyamar gumaka, kana wa haikali fashi? 23Kai da kake taƙama da doka, kana nuna rashin bangirma ga Allah ta wurin karya dokar? 24Kamar yadda yake a rubuce, “Ana saɓon sunan Allah a cikin Al’ummai saboda ku.”2.24 Ish 52.5; Ezk 36.22

25Kaciya tana da amfani in kana kiyaye dokar, amma in kana karya dokar, ka zama kamar ba a yi maka kaciya ba. 26In marasa kaciya suna kiyaye dokar, ashe, ba za a ɗauke su kamar an yi musu kaciya ba? 27Wanda ba shi da kaciya ta jiki duk da haka yana biyayya da dokar zai iya hukunta ka, kai da kake karya dokar, ko da yake kana da rubutaccen tsarin dokar an kuma yi maka kaciya.

28Mutum ba mutumin Yahuda ba ne in shi mutumin Yahuda ne kawai a jiki, haka kuma kaciya ba a waje ko a jiki kawai ba. 29A’a, mutum mutumin Yahuda ne in shi mutumin Yahuda ne a zuci; kuma kaciya ita ce kaciya ta zuci, ta wurin Ruhu, ba ta wurin rubutaccen doka ba. Irin wannan mutum yana samun yabo daga Allah ne, ba ɗan adam ba.

King James Version

Romans 2:1-29

1Therefore thou art inexcusable, O man, whosoever thou art that judgest: for wherein thou judgest another, thou condemnest thyself; for thou that judgest doest the same things. 2But we are sure that the judgment of God is according to truth against them which commit such things. 3And thinkest thou this, O man, that judgest them which do such things, and doest the same, that thou shalt escape the judgment of God? 4Or despisest thou the riches of his goodness and forbearance and longsuffering; not knowing that the goodness of God leadeth thee to repentance? 5But after thy hardness and impenitent heart treasurest up unto thyself wrath against the day of wrath and revelation of the righteous judgment of God; 6Who will render to every man according to his deeds: 7To them who by patient continuance in well doing seek for glory and honour and immortality, eternal life: 8But unto them that are contentious, and do not obey the truth, but obey unrighteousness, indignation and wrath, 9Tribulation and anguish, upon every soul of man that doeth evil, of the Jew first, and also of the Gentile; 10But glory, honour, and peace, to every man that worketh good, to the Jew first, and also to the Gentile: 11For there is no respect of persons with God. 12For as many as have sinned without law shall also perish without law: and as many as have sinned in the law shall be judged by the law; 13(For not the hearers of the law are just before God, but the doers of the law shall be justified. 14For when the Gentiles, which have not the law, do by nature the things contained in the law, these, having not the law, are a law unto themselves: 15Which shew the work of the law written in their hearts, their conscience also bearing witness, and their thoughts the mean while accusing or else excusing one another;) 16In the day when God shall judge the secrets of men by Jesus Christ according to my gospel.

17Behold, thou art called a Jew, and restest in the law, and makest thy boast of God, 18And knowest his will, and approvest the things that are more excellent, being instructed out of the law; 19And art confident that thou thyself art a guide of the blind, a light of them which are in darkness, 20An instructor of the foolish, a teacher of babes, which hast the form of knowledge and of the truth in the law. 21Thou therefore which teachest another, teachest thou not thyself? thou that preachest a man should not steal, dost thou steal? 22Thou that sayest a man should not commit adultery, dost thou commit adultery? thou that abhorrest idols, dost thou commit sacrilege? 23Thou that makest thy boast of the law, through breaking the law dishonourest thou God? 24For the name of God is blasphemed among the Gentiles through you, as it is written. 25For circumcision verily profiteth, if thou keep the law: but if thou be a breaker of the law, thy circumcision is made uncircumcision. 26Therefore if the uncircumcision keep the righteousness of the law, shall not his uncircumcision be counted for circumcision? 27And shall not uncircumcision which is by nature, if it fulfil the law, judge thee, who by the letter and circumcision dost transgress the law? 28For he is not a Jew, which is one outwardly; neither is that circumcision, which is outward in the flesh: 29But he is a Jew, which is one inwardly; and circumcision is that of the heart, in the spirit, and not in the letter; whose praise is not of men, but of God.