Mattiyu 1 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 1:1-25

Asalin Yesu Kiristi

(Luka 3.23-38)

1Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.

2Ibrahim ya haifi Ishaku,

Ishaku ya haifi Yaƙub,

Yaƙub ya haifi Yahuda da ’yan’uwansa,

3Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu;

Ferez ya haifi Hezron,

Hezron ya haifi Ram,

4Ram ya haifi Amminadab,

Amminadab ya haifi Nashon,

Nashon ya haifi Salmon,

5Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa,

Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa,

Obed ya haifi Yesse,

6Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda.

Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.

7Solomon ya haifi Rehobowam,

Rehobowam ya haifi Abiya,

Abiya ya haifi Asa,

8Asa ya haifi Yehoshafat,

Yehoshafat ya haifi Yehoram,

Yehoram ya haifi Azariya,

9Azariya ya haifi Yotam,

Yotam ya haifi Ahaz,

Ahaz ya haifi Hezekiya,

10Hezekiya ya haifi Manasse,

Manasse ya haifi Amon,

Amon ya haifi Yosiya,

11Yosiya kuma ya haifi Yekoniya1.11 Wato, Jehohiyachin; haka ma a aya 12 da ’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.

12Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon.

Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel,

Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,

13Zerubbabel ya haifi Abiyud,

Abiyud ya haifi Eliyakim,

Eliyakim ya haifi Azor,

14Azor ya haifi Zadok,

Zadok ya haifi Akim,

Akim kuma ya haifi Eliyud,

15Eliyud ya haifi Eleyazar,

Eleyazar ya haifi Mattan,

Mattan ya haifi Yaƙub,

16Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.

17Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.1.17 Ko kuwa Kiristi. Kiristi (Da Girik) Almasihu (Da Ibraniyanci) duk suna nufin “Shafaffe.”

Haihuwar Yesu Kiristi

(Luka 2.1-7)

18Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 19Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.

20Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne. 21Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu,1.21 Yesu da Girik shi ne Yoshuwa da Ibraniyanci, wanda yake nufin Ubangiji yana ceto. gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”

22Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa, 23“Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel”1.23 Ish 7.14 (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).

24Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa. 25Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.

New International Reader’s Version

Matthew 1:1-25

The Family Line of Jesus the Messiah

1This is the written story of the family line of Jesus the Messiah. He is the son of David. He is also the son of Abraham.

2Abraham was the father of Isaac.

Isaac was the father of Jacob.

Jacob was the father of Judah and his brothers.

3Judah was the father of Perez and Zerah. Tamar was their mother.

Perez was the father of Hezron.

Hezron was the father of Ram.

4Ram was the father of Amminadab.

Amminadab was the father of Nahshon.

Nahshon was the father of Salmon.

5Salmon was the father of Boaz. Rahab was Boaz’s mother.

Boaz was the father of Obed. Ruth was Obed’s mother.

Obed was the father of Jesse.

6And Jesse was the father of King David.

David was the father of Solomon. Solomon’s mother had been Uriah’s wife.

7Solomon was the father of Rehoboam.

Rehoboam was the father of Abijah.

Abijah was the father of Asa.

8Asa was the father of Jehoshaphat.

Jehoshaphat was the father of Jehoram.

Jehoram was the father of Uzziah.

9Uzziah was the father of Jotham.

Jotham was the father of Ahaz.

Ahaz was the father of Hezekiah.

10Hezekiah was the father of Manasseh.

Manasseh was the father of Amon.

Amon was the father of Josiah.

11And Josiah was the father of Jeconiah and his brothers. At that time, the Jewish people were forced to go away to Babylon.

12After this, the family line continued.

Jeconiah was the father of Shealtiel.

Shealtiel was the father of Zerubbabel.

13Zerubbabel was the father of Abihud.

Abihud was the father of Eliakim.

Eliakim was the father of Azor.

14Azor was the father of Zadok.

Zadok was the father of Akim.

Akim was the father of Elihud.

15Elihud was the father of Eleazar.

Eleazar was the father of Matthan.

Matthan was the father of Jacob.

16Jacob was the father of Joseph. Joseph was the husband of Mary. And Mary was the mother of Jesus, who is called the Messiah.

17So there were 14 generations from Abraham to David. There were 14 from David until the Jewish people were forced to go away to Babylon. And there were 14 from that time to the Messiah.

Joseph Accepts Jesus as His Son

18This is how the birth of Jesus the Messiah came about. His mother Mary and Joseph had promised to get married. But before they started to live together, it became clear that she was going to have a baby. She became pregnant by the power of the Holy Spirit. 19Her husband Joseph was faithful to the law. But he did not want to put her to shame in public. So he planned to divorce her quietly.

20But as Joseph was thinking about this, an angel of the Lord appeared to him in a dream. The angel said, “Joseph, son of David, don’t be afraid to take Mary home as your wife. The baby inside her is from the Holy Spirit. 21She is going to have a son. You must give him the name Jesus. That’s because he will save his people from their sins.”

22All this took place to bring about what the Lord had said would happen. He had said through the prophet, 23“The virgin is going to have a baby. She will give birth to a son. And he will be called Immanuel.” (Isaiah 7:14) The name Immanuel means “God with us.”

24Joseph woke up. He did what the angel of the Lord commanded him to do. He took Mary home as his wife. 25But he did not sleep with her until she gave birth to a son. And Joseph gave him the name Jesus.