Mattiyu 2 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 2:1-23

Ziyarar Masana

1Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana,2.1 A al’adance Masu Hikima daga gabas suka zo Urushalima 2suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas2.2 Ko kuwa a tauraro sa’ad da ya taso mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”

3Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima. 4Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi. 5Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.

6“ ‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda,

ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba,

gama daga cikinki mai mulki zai zo,

wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’2.6 Mik 5.2

7Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana. 8Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”

9Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake. 10Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai. 11Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur. 12Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.

Tserewa zuwa Masar

13Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”

14Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar, 15inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”2.15 Hos 11.1

16Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan ’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan. 17Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,

18“An ji murya a Rama,

tana kuka da makoki mai tsanani,

Rahila ce take kuka domin ’ya’yanta,

an kāsa ta’azantar da ita,

don ba su.”2.18 Irm 31.15

Komowa zuwa Nazaret

19Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar, 20ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”

21Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila. 22Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili, 23ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”

New International Reader’s Version

Matthew 2:1-23

The Wise Men Visit Jesus

1Jesus was born in Bethlehem in Judea. This happened while Herod was king of Judea. After Jesus’ birth, Wise Men from the east came to Jerusalem. 2They asked, “Where is the child who has been born to be king of the Jews? We saw his star when it rose. Now we have come to worship him.”

3When King Herod heard about it, he was very upset. Everyone in Jerusalem was troubled too. 4So Herod called together all the chief priests of the people. He also called the teachers of the law. He asked them where the Messiah was going to be born. 5“In Bethlehem in Judea,” they replied. “This is what the prophet has written. He said,

6“ ‘But you, Bethlehem, in the land of Judah,

are certainly not the least important among the towns of Judah.

A ruler will come out of you.

He will rule my people Israel like a shepherd.’ ” (Micah 5:2)

7Then Herod secretly called for the Wise Men. He found out from them exactly when the star had appeared. 8He sent them to Bethlehem. He said, “Go and search carefully for the child. As soon as you find him, report it to me. Then I can go and worship him too.”

9After the Wise Men had listened to the king, they went on their way. The star they had seen when it rose went ahead of them. It finally stopped over the place where the child was. 10When they saw the star, they were filled with joy. 11The Wise Men went to the house. There they saw the child with his mother Mary. They bowed down and worshiped him. Then they opened their treasures. They gave him gold, frankincense and myrrh. 12But God warned them in a dream not to go back to Herod. So they returned to their country on a different road.

Jesus’ Family Escapes to Egypt

13When the Wise Men had left, Joseph had a dream. In the dream an angel of the Lord appeared to Joseph. “Get up!” the angel said. “Take the child and his mother and escape to Egypt. Stay there until I tell you to come back. Herod is going to search for the child. He wants to kill him.”

14So Joseph got up. During the night, he left for Egypt with the child and his mother Mary. 15They stayed there until King Herod died. So the words the Lord had spoken through the prophet came true. He had said, “I brought my son out of Egypt.” (Hosea 11:1)

16Herod realized that the Wise Men had tricked him. So he became very angry. He gave orders about Bethlehem and the area around it. He ordered all the boys two years old and under to be killed. This agreed with the time when the Wise Men had seen the star. 17In this way, the words Jeremiah the prophet spoke came true. He had said,

18“A voice is heard in Ramah.

It’s the sound of crying and deep sadness.

Rachel is crying over her children.

She refuses to be comforted,

because they are gone.” (Jeremiah 31:15)

Jesus’ Family Returns to Nazareth

19After Herod died, Joseph had a dream while he was still in Egypt. In the dream an angel of the Lord appeared to him. 20The angel said, “Get up! Take the child and his mother. Go to the land of Israel. The people who were trying to kill the child are dead.”

21So Joseph got up. He took the child and his mother Mary back to the land of Israel. 22But then he heard that Archelaus was king of Judea. Archelaus was ruling in place of his father Herod. This made Joseph afraid to go there. Joseph had been warned in a dream. So he went back to the land of Galilee instead. 23There he lived in a town called Nazareth. So what the prophets had said about Jesus came true. They had said that he would be called a Nazarene.