Ibraniyawa 13 – HCB & BPH

Hausa Contemporary Bible

Ibraniyawa 13:1-25

Gargaɗin ƙarshe

1Ku ci gaba da ƙaunar juna kamar ’yan’uwa. 2Kada ku manta da yin alheri ga baƙi, gama ta yin haka ne waɗansu suka yi wa mala’iku hidima, ba da saninsu ba. 3Ku riƙa tunawa da waɗanda suke a kurkuku kamar tare kuke a kurkuku, da kuma waɗanda ake gwada musu azaba, kamar ku ake yi wa.

4Aure yă zama abin girmamawa ga kowa, a kuma kiyaye gadon aure da tsabta, gama Allah zai hukunta masu zina da kuma dukan masu fasikanci. 5Ku kiyaye kanku daga yawan son kuɗi, ku kuma gamsu da abin da kuke da shi, gama Allah ya ce,

“Ba zan taɓa bar ka ba;

ba zan taɓa yashe ka ba.”13.5 M Sh 31.6

6Saboda haka muna iya fitowa gabagadi, mu ce,

“Ubangiji ne mai taimakona; ba zan ji tsoro ba.

Me mutum zai iya yi mini?”13.6 Zab 118.6,7

7Ku tuna da shugabanninku, waɗanda suka faɗa muku maganar Allah. Ku dubi irin rayuwar da suka yi ku kuma yi koyi da bangaskiyarsu. 8Yesu Kiristi ba ya sākewa, shi ne a jiya, shi ne a yau, shi ne kuma har abada.

9Kada a ɗauke muku hankali da sababbin koyarwa dabam-dabam. Yana da kyau zukatanmu su ƙarfafa ta wurin alheri, ba ta wurin abinci waɗanda ba su da amfani ga waɗanda suke cinsu. 10Muna da bagade inda firistocin da suka yi hidima a tabanakul ba su da izini su ci.

11Babban firist yakan ɗauki jinin dabbobi yă shiga cikin Wuri Mafi Tsarki a matsayin hadaya ta zunubi, amma jikunan dabbobin akan ƙone su a bayan sansani. 12Haka ma Yesu ya sha wahala a bayan gari don yă tsarkake mutane ta wurin jininsa. 13Saboda haka, sai mu fita mu je wajensa a bayan sansani, muna ɗaukar kunyar da ya sha. 14Gama a nan ba mu da dawwammamen birni, sai dai muna zuba ido a kan birnin nan mai zuwa.

15Saboda haka, ta wurin Yesu, bari mu ci gaba da miƙa hadaya ta yabo ga Allah, yabon leɓuna da yake shaidar sunansa. 16Kada kuma ku manta yin aikin nagari da kuma taimakon waɗansu, gama da irin waɗannan hadayu ne Allah yake jin daɗi.

17Ku yi wa shugabanninku biyayya ku kuma miƙa kanku ga ikonsu. Suna lura da ku kuma za su ba da lissafi a gaban Allah. Saboda haka kada ku sa su yi fushi saboda aikinsu, ku sa su yi farin ciki. In ba haka ba za su iya taimakonku ba ko kaɗan.

18Ku yi mana addu’a. Mun tabbata cewa muna da lamiri mai kyau, kuma muna da marmari mu yi rayuwa ta bangirma a ta kowace hanya. 19Ni musamman, ina roƙonku ku yi addu’a, don a komo da ni a gare ku ba da daɗewa ba.

Albarka da kuma gaisuwa ta ƙarshe

20Bari Allah na salama, wanda ta wurin jinin madawwamin alkawari ya tā da Ubangijinmu Yesu daga matattu, wannan Makiyayin tumaki mai girma, 21yă kintsa ku da kowane abu mai kyau domin aikata nufinsa, bari kuma yă aikata abin da zai gamshe shi cikinmu, ta wurin Yesu Kiristi, a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada. Amin.

22’Yan’uwa, ina roƙonku ku yi haƙuri da wannan gargaɗi, don ba wata doguwar wasiƙa ce na rubuta muku ba.

23Ina so ku san cewa an saki ɗan’uwanmu Timoti. In ya iso da wuri, zan zo tare da shi in gan ku.

24Ku gai da dukan shugabanninku da kuma dukan mutanen Allah.

Waɗanda suke Italiya suna gaishe ku.

25Alheri yă kasance da ku duka.

Bibelen på hverdagsdansk

Hebræerbrevet 13:1-25

Afsluttende formaninger og hilsener

1Hold fast ved den indbyrdes kærlighed. 2Forsøm ikke at byde de fremmede velkommen hos jer, for derved har nogle haft engle som gæster uden at vide af det. 3Husk på dem, der sidder i fængsel, og føl med dem, som var I selv i fængsel. Føl smerten hos dem, der mishandles, som var det jeres egen krop, det gik ud over.

4Alle bør respektere ægteskabet, og I skal være tro mod jeres ægtefælle, for Gud vil dømme dem, der er utro eller lever i seksuel synd. 5Hold jer fri af pengebegær og vær tilfredse med det, I har. Gud har jo sagt: „Jeg vil aldrig svigte dig eller forlade dig.”13,5 5.Mos. 31,6.

6Derfor kan vi med frimodighed sige:

„Herren er min hjælper, så jeg vil intet frygte.

Hvad kan mennesker gøre mig?”13,6 Sl. 118,6 (LXX).

7Tænk på jeres ledere, som har talt Guds ord til jer. Se på, hvad de har udrettet, og efterlign deres tro. 8Jesus Kristus er den samme i går og i dag, ja til evig tid. 9Lad jer ikke rive med af forskellige, fremmede lærdomme. Det er godt for det indre menneske at hente styrke i Guds nåde og ikke i religiøse spiseregler, som alligevel ikke hjælper dem, der prøver at overholde dem.

10Vi har et alter, som de præster, der gør tjeneste i templet, ikke har adgang til. 11Ypperstepræsten bragte på forsoningsdagen blodet fra syndofrene ind i åbenbaringsteltets allerhelligste rum, men dyrenes kroppe blev brændt uden for lejren.13,11 Jf. 3.Mos. 16,27. 12Jesus skabte forsoning mellem Gud og folket ved sit eget blod, da han blev dræbt uden for byen. 13Lad os derfor samles med ham uden for lejren, selvom vi bliver hånet for det. 14Der findes nemlig ikke noget sted i denne verden, som kan være vores blivende hjem. Vi ser i stedet frem til vores evige hjem i den himmelske verden.

15Lad os på grund af, hvad Jesus har gjort, altid bringe lovprisningsofre til Gud. Lad os prise og takke Gud med vores ord. 16Men forsøm heller ikke at gøre godt og at dele med andre, for sådanne ofre glæder Gud.

17Adlyd jeres åndelige ledere og ret jer efter dem. De våger over jer, fordi de har ansvar for jer og en dag skal aflægge regnskab for deres tjeneste over for Gud. Hvis I adlyder lederne, vil de kunne gøre deres arbejde med glæde, i stedet for at det bliver en byrde. Det sidste ville ikke være godt for jer.

18Bed for os, venner, for vi mener at have en god samvittighed, da vi altid søger at gøre det rigtige. 19Netop nu har jeg særligt brug for jeres forbøn, så jeg hurtigt kan få mulighed for at besøge jer.

20Jesus, vores Herre, er den store Hyrde for fårene, og han beseglede en evig pagt med sit eget blod. Jeg beder om, at Fredens Gud, som oprejste Jesus fra de døde, 21vil udruste jer med alt, hvad I har brug for for at kunne gøre hans vilje, og at han ved Kristi kraft vil fremelske alt det i os alle, som glæder ham. Æren tilhører Jesus Kristus i al evighed. Amen.

22Kære venner, tag godt imod mine formaninger, selvom jeg har skrevet i al korthed. 23I skal vide, at vores medarbejder Timoteus nu er blevet løsladt, og hvis han snart kommer hertil, vil jeg tage ham med, når jeg kommer til jer. 24Hils alle jeres ledere og de andre troende. De kristne fra Italien sender hilsen til jer. 25Guds nåde være med jer alle!