Yaƙub 1 – HCB & BPH

Hausa Contemporary Bible

Yaƙub 1:1-27

1Yaƙub, bawan Allah da kuma na Ubangiji Yesu Kiristi,

Zuwa ga kabilan nan goma sha biyu, da suke warwartse a cikin al’ummai.

Gaisuwa mai yawa.

Gwaje-gwaje da jarrabobi

2Ku ɗauki wannan da farin ciki mai tsabta, ’yan’uwana, duk sa’ad da gwaje-gwaje na kowane iri suka zo muku, 3domin kun san cewa gwajin bangaskiyarku yakan haifi daurewa. 4Dole daurewa ta kammala aikinta don ku zama balagaggu da kuma cikakku, ba ku kuma rasa kome ba. 5In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi. 6Amma sa’ad da ya roƙa, dole yă gaskata, ba tare da shakka ba, domin shi mai shakka, yana kama da raƙumar ruwan tekun da iska take kori tana kuma ɓuɓɓugowa. 7Kada irin wannan mutum yă yi tsammani zai sami wani abu daga Ubangiji; 8shi mai zuciya biyu ne, marar tsai da zuciyarsa wuri ɗaya a cikin duk abin da yake yi.

9Bari ɗan’uwan da yake cikin halin ƙasƙanci yă yi taƙama a matsayinsa na ɗaukaka. 10Amma wanda yake mai arziki, ya kamata yă yi taƙama a matsayinsa na ƙasƙanci, gama ba zai daɗe ba kamar furen jeji. 11Gama in rana ta fito ta yi zafi mai tsanani sai ta sa tsiro yă yanƙwane tsiro; furensa yă kakkaɓe, kyansa kuma yă lalace. Haka ma mai arziki zai shuɗe yayinda yake cikin harkarsa.

12Mai albarka ne mutumin da yake daurewa cikin gwaji, gama bayan ya yi nasara da gwajin, zai sami rawanin rai wanda Allah ya yi alkawari ga waɗanda suke ƙaunarsa.

13Sa’ad da aka jarrabci mutum, kada yă ce, “Allah ne yake jarrabtarsa.” Gama ba ya yiwuwa a jarrabci Allah da mugunta, shi kuma ba ya jarrabtar kowa; 14amma akan jarrabce kowane mutum sa’ad da muguwar sha’awarsa ta janye shi ta kuma rinjaye shi. 15Sa’an nan, bayan da sha’awar ta yi ciki, takan haifi zunubi; zunubi kuwa, sa’ad da ya balaga yakan haifi mutuwa.

16Kada a ruɗe ku, ’yan’uwana ƙaunatattu. 17Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau. 18Ya zaɓa yă haife mu ta wurin kalmar gaskiya, domin mu zama ’ya’yan fari na dukan abin da ya halitta.

Saurarawa da kuma aikatawa

19’Yan’uwana ƙaunatattu, ku lura da wannan. Ya kamata kowa yă kasance mai saurin saurara, ba mai saurin magana ba, ba kuma mai saurin fushi ba, 20gama fushin mutum ba ya kawo rayuwar adalcin da Allah yake so. 21Saboda haka, ku rabu da ƙazamin hali da kuma kowace irin mugunta ku kuma yi na’am da maganar da aka shuka a cikinku da tawali’u, wadda za tă iya cetonku.

22Kada ku zama masu ji kawai, ku ruɗi kanku. A maimakon haka ku zama masu yin abin da ta ce. 23Duk wanda yake ji magana ne kawai, bai kuwa aikata abin da ta ce ba, yana kama da mutumin da ya kalli fuskarsa a madubi 24bayan ya kalli kansa, sa’ad da ya tashi daga wurin, nan da nan sai yă manta da kamanninsa. 25Amma duk mai duba cikakkiyar ƙa’idan nan ta ’yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai yă mance ba, sai dai mai yi ne yă zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake yi.

26In wani ya ɗauki kansa mai addini ne duk da haka bai ƙame harshensa ba, ruɗin kansa yake yi addininsa kuwa banza ne. 27Addinin da Allah Ubanmu ya yarda da shi a matsayin mai tsabta da kuma marar aibi shi ne, a kula da marayu da gwauraye cikin damuwoyinsu, a kuma kiyaye kai daga lalacin da duniya take sa wa.

Bibelen på hverdagsdansk

Jakobs Brev 1:1-27

Indledende hilsen

1Dette brev er fra Jakob, Guds og Herren Jesu Kristi tjener. Jeg skriver til de jødekristne fra de 12 stammer, der bor rundt omkring i verden. Guds fred!

Om prøvelser, udholdenhed og tro

2Kære venner, når I kommer ud for mange forskellige vanskeligheder og problemer, så glæd jer over det. 3I ved jo, at når jeres tro1,3 Eller: „trofasthed, troskab”. prøves, skærper det jeres udholdenhed. 4Og hvis I ellers holder ud gennem prøvelserne, vil I vokse i modenhed, så I ikke står tilbage på noget område.

5Hvis I mangler visdom, skal I bede om at få den fra Gud. Gud giver nemlig gerne til alle uden at komme med bebrejdelser. 6Men I skal bede i tro uden at tvivle. For hvis I vakler i jeres tillid til Gud, er I som havets bølger, der kastes frem og tilbage af stormen, 7-8eller som en, der står med et ben i hver lejr og går skiftevis i den ene og den anden retning. Beder I på den måde, kan I ikke regne med at få noget fra Herren.

Den himmelske rigdom er langt mere værd end den jordiske

9De kristne, der har en lav position i samfundet, kan glæde sig over at have en høj position i den åndelige verden. 10De, der før var rige, kan glæde sig over at være blevet ydmyget, for rigdom forgår som blomster, der visner. 11Når solen brænder i dagens hede, svides planterne. Blomsterne falmer, og deres pragt forsvinder. Sådan kan rigdom forsvinde, hurtigt og uden varsel.

Gud frister ingen, men lover evigt liv

12Velsignede er de, der holder ud, når der er modgang, for når de er kommet sejrende igennem, vil de få det evige liv som belønning. Det har Gud lovet alle dem, som elsker ham.

13Når du bliver fristet til at gøre noget forkert, skal du ikke sige: „Det er Gud, der frister mig.” Gud fristes aldrig til at gøre noget ondt, og han frister heller aldrig nogen til at gøre det. 14Når du bliver fristet, er det, fordi du bliver tiltrukket af noget, som du i virkeligheden har lyst til. 15Giver du efter for fristelsen, fører det til synd, og synden fører i sidste ende til død.

16Elskede venner, lad jer ikke bedrage. 17Det er udelukkende gode og fuldkomne gaver, der kommer til os fra vores himmelske Far, som har skabt lysene i himmelrummet. Hans lys er uforanderligt, og han skjules ikke af skygger. 18Han besluttede at give os nyt liv gennem sandhedens ord, så vi blev hans særlige ejendom blandt al skabningen.

Lyt, tag imod Guds ord og lev det ud i hverdagen

19Kære venner, husk, at det er godt at lytte, at tænke sig om, før man taler, og ikke være for hurtig til at blive vred, 20for et menneskes vrede kommer i vejen for Guds vilje. 21Derfor skal I lægge alle urene tanker og onde handlinger bag jer og koncentrere jer om at give vækstbetingelser til det ord, som er plantet i jer, og som er i stand til at føre jer frem til det evige liv.

22I bedrager jer selv, hvis I kun hører ordet uden at handle på det. 23Hvis I kun lytter til undervisningen, men ikke handler på det, I hører, er det, som når I betragter jeres ansigt i et spejl. 24Lige så snart I vender ryggen til spejlet, har I glemt, hvordan I så ud. 25Men hvis I fordyber jer i frihedens fuldkomne lov, og bliver ved med at holde den for øje, bliver I ikke som dem, der hører og glemmer, men som dem, der hører og handler. Det er jo dem, der handler på Guds ord, der oplever Guds velsignelse.

26De, der mener, at de tjener Gud, men ikke tøjler deres tunge, bedrager sig selv. Den måde at tjene Gud på er intet værd. 27Nej, en god og ægte måde at tjene Gud, vores Far, på er at tage sig af forældreløse børn og fattige enker og undgå at blive forurenet af verdslighed.