1 Yohanna 2 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

1 Yohanna 2:1-29

1’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci. 2Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.

3Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa. 4Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa. 5Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa. 6Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.

7Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji. 8Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.

9Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu. 10Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe. 11Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.

12Ina rubuta muku, ’ya’yana ƙaunatattu,

domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.

13Ina rubuta muku, ubanni,

domin kun san shi wanda yake tun farko.

Ina rubuta muku, samari,

domin kun ci nasara a kan mugun nan.

14Ina rubuta muku, ’ya’yana ƙaunatattu,

domin kun san Uba.

Ina rubuta muku, ubanni,

domin kun san shi wanda yake tun farko.

Ina rubuta muku, samari,

domin kuna da ƙarfi,

maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku,

kun kuma ci nasara a kan mugun nan.

Kada ku ƙaunaci duniya

15Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa. 16Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya. 17Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada.

Gargaɗi a kan magabcin Kiristi

18’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso. 19Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.

20Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya. 21Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya. 22Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan. 23Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.

24Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban. 25Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami.

26Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce. 27Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.

’Ya’yan Allah

28Yanzu fa, ya ku ’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.

29In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.

New International Reader’s Version

1 John 2:1-29

1My dear children, I’m writing this to you so that you will not sin. But suppose someone does sin. Then we have a friend who speaks to the Father for us. He is Jesus Christ, the Blameless One. 2He gave his life to pay for our sins. But he not only paid for our sins. He also paid for the sins of the whole world.

Instructions About Loving and Hating Other Believers

3We know that we have come to know God if we obey his commands. 4Suppose someone says, “I know him.” But suppose this person does not do what God commands. Then this person is a liar and is not telling the truth. 5But if anyone obeys God’s word, then that person truly loves God. Here is how we know we belong to him. 6Those who claim to belong to him must live just as Jesus did.

7Dear friends, I’m not writing you a new command. Instead, I’m writing one you have heard before. You have had it since the beginning. 8But I am writing what amounts to a new command. Its truth was shown in how Jesus lived. It is also shown in how you live. That’s because the darkness is passing away. And the true light is already shining.

9Suppose someone claims to be in the light but hates a brother or sister. Then they are still in the darkness. 10Anyone who loves their brother and sister lives in the light. There is nothing in them to make them fall into sin. 11But anyone who hates a brother or sister is in the darkness. They walk around in the darkness. They don’t know where they are going. The darkness has made them blind.

Reasons for Writing

12Dear children, I’m writing to you

because your sins have been forgiven.

They have been forgiven because of what Jesus has done.

13Fathers, I’m writing to you

because you know the one who is from the beginning.

Young men, I’m writing to you

because you have won the battle over the evil one.

14Dear children, I’m writing to you

because you know the Father.

Fathers, I’m writing to you

because you know the one who is from the beginning.

Young men, I’m writing to you

because you are strong.

God’s word lives in you.

You have won the battle over the evil one.

Do Not Love the World

15Do not love the world or anything in it. If anyone loves the world, love for the Father is not in them. 16Here is what people who belong to this world do. They try to satisfy what their sinful desires want to do. They long for what their sinful eyes look at. They take pride in what they have and what they do. All of this comes from the world. None of it comes from the Father. 17The world and its evil desires are passing away. But whoever does what God wants them to do lives forever.

Warnings About Saying No to the Son

18Dear children, we are living in the last days. You have heard that the great enemy of Christ is coming. But even now many enemies of Christ have already come. That’s how we know that these are the last days. 19These enemies left our community of believers. They didn’t really belong to us. If they had belonged to us, they would have remained with us. But by leaving they showed that none of them belonged to us.

20You have received the Spirit from the Holy One. And all of you know the truth. 21I’m not writing to you because you don’t know the truth. I’m writing because you do know it. I’m writing to you because no lie comes from the truth. 22Who is the liar? It is anyone who says that Jesus is not the Christ. The person who says this is the great enemy of Christ. They say no to the Father and the Son. 23The person who says no to the Son doesn’t belong to the Father. But anyone who says yes to the Son belongs to the Father also.

24Make sure that you don’t forget what you have heard from the beginning. Then you will remain joined to the Son and to the Father. 25And here is what God has promised us. He has promised us eternal life.

26I’m writing these things to warn you. I am warning you about people trying to lead you astray. 27But you have received the Holy Spirit from God. He continues to live in you. So you don’t need anyone to teach you. God’s Spirit teaches you about everything. What he says is true. He doesn’t lie. Remain joined to Christ, just as you have been taught by the Spirit.

God’s Children and Sin

28Dear children, remain joined to Christ. Then when he comes, we can be bold. We will not be ashamed to meet him when he comes.

29You know that God is right and always does what is right. And you know that everyone who does what is right is God’s child.