2 Bitrus 1 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

2 Bitrus 1:1-21

1Siman Bitrus, bawa da kuma manzon Yesu Kiristi,

Zuwa ga waɗanda ta wurin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi sun sami bangaskiya mai daraja irin tamu.

2Alheri da salama su zama naku a yalwace ta wurin sanin Allah da Yesu Ubangijinmu.

Mai da kira da kuma zaɓen da aka wa mutum yă zama tabbatacce

3Ikonsa na Allahntaka ya ba mu kome da muke bukata don rayuwa da kuma tsoron Allah ta wurin sanin wanda ya kira mu ta wurin ɗaukakarsa da nagartarsa. 4Ta wurin waɗannan ya ba mu alkawaransa masu girma da kuma masu daraja, domin ta wurinsu ku iya yin tarayya cikin Allahntakarsa, ku kuma kuɓuta daga lalatar da take cikin duniya wadda mugayen sha’awace-sha’awace suke jawowa.

5Saboda haka, ku yi iyakar ƙoƙari ku ƙara wa bangaskiyarku nagarta; ga nagarta kuwa, ku ƙara mata sani; 6ga sani kuma ku ƙara masa kamunkai; ga kamunkai kuma ku ƙara da daurewa; ga daurewa kuwa ku ƙara da tsoron Allah; 7ga tsoron Allah kuma ku ƙara da nuna alheri ga ’yan’uwa; ga nuna alheri ga ’yan’uwa kuma ku ƙara da ƙauna. 8Domin in kuna ƙaruwa a waɗannan halaye, za su kāre ku daga rashin tasiri da rayuwa na rashin amfani cikin saninku na Ubangijinmu Yesu Kiristi. 9Amma in wani ba shi da su, ba shi da hangen nesa ke nan kuma makaho ne, ya kuma manta cewa an tsarkake shi daga zunubansa na dā.

10Saboda haka ’yan’uwana, ku ƙara aniya wajen tabbatar da kiranku da zaɓenku da aka yi. Gama in kuka yi waɗannan abubuwa, ba za ku taɓa fāɗuwa ba, 11za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi.

Annabcin nassi

12Saboda haka kullum zan tuna muku da waɗannan, ko da yake kun sansu kun kuma kahu ƙwarai cikin gaskiyar da kuke da ita yanzu. 13A ganina ya dace in tunashe ku muddin ina raye cikin tentin wannan jiki, 14domin na sani na kusa in ajiye shi a gefe, yadda Ubangijinmu Yesu Kiristi ya nuna mini a sarari. 15Zan kuwa yi iyakacin ƙoƙari in ga cewa bayan rabuwata kullum za ku iya tuna da waɗannan abubuwa.

16Ba mu bi tatsuniyoyin da aka ƙaga da wayo sa’ad da muka gaya muku game da ikon Ubangijinmu Yesu Kiristi da zuwansa ba, sai dai mu shaidu ne na ɗaukakarsa mai girma da muka gani da ido. 17Gama ya sami girma da ɗaukaka daga Allah Uba sa’ad da murya ta zo masa daga Mafificiyar Ɗaukaka cewa, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; da shi nake jin daɗi ƙwarai.”1.17 Mat 17.5; Mar 9.7; Luk 9.35 18Mu kanmu mun ji wannan muryar da ta zo daga sama sa’ad da muke tare da shi a kan dutse mai tsarki.

19Muna kuwa da maganar annabawa da aka ƙara tabbatar mana, zai fi kyau in kuka lura da ita, kamar hasken da yake haskakawa a wuri mai duhu, har yă zuwa wayewar gari da kuma haskakawar tauraron asubahi a zukatanku. 20Gaba da kome dai, dole ku gane cewa babu annabcin Nassin da ya fito daga fassarar annabi da kansa. 21Gama annabci bai taɓa samo tushensa daga nufin mutum ba, sai dai mutane sun yi magana daga Allah yayinda Ruhu Mai Tsarki ya bishe su.

New International Reader’s Version

2 Peter 1:1-21

1I, Simon Peter, am writing this letter. I serve Jesus Christ. I am his apostle.

I am sending this letter to you. You are those who have received a faith as valuable as ours. You received it because our God and Savior Jesus Christ does what is right.

2May more and more grace and peace be given to you. May they come to you as you learn more about God and about Jesus our Lord.

Showing That God Has Chosen You

3God’s power has given us everything we need to lead a godly life. All of this has come to us because we know the God who chose us. He chose us because of his own glory and goodness. 4He has also given us his very great and valuable promises. He did it so you could share in his nature. You can share in it because you’ve escaped from the evil in the world. This evil is caused by sinful desires.

5So you should try very hard to add goodness to your faith. To goodness, add knowledge. 6To knowledge, add the ability to control yourselves. To the ability to control yourselves, add the strength to keep going. To the strength to keep going, add godliness. 7To godliness, add kindness for one another. And to kindness for one another, add love. 8All these things should describe you more and more. They will make you useful and fruitful as you know our Lord Jesus Christ better. 9But what if these things don’t describe someone at all? Then that person can’t see very well. In fact, they are blind. They have forgotten that their past sins have been washed away.

10My brothers and sisters, try very hard to show that God has appointed you to be saved. Try hard to show that he has chosen you. If you do everything I have just said, you will never trip and fall. 11You will receive a rich welcome into the kingdom that lasts forever. It is the kingdom of our Lord and Savior Jesus Christ.

Prophecy of Scripture Comes From God

12So I will always remind you of these things. I’ll do it even though you know them. I’ll do it even though you now have deep roots in the truth. 13I think it is right for me to remind you. It is right as long as I live in this tent. I’m talking about my body. 14I know my tent will soon be removed. Our Lord Jesus Christ has made that clear to me. 15I hope that you will always be able to remember these things after I’m gone. I will try very hard to see that you do.

16We told you about the time our Lord Jesus Christ came with power. But we didn’t make up clever stories when we told you about it. With our own eyes we saw him in all his majesty. 17God the Father gave him honor and glory. The voice of the Majestic Glory came to him. It said, “This is my Son, and I love him. I am very pleased with him.” (Matthew 17:5; Mark 9:7; Luke 9:35) 18We ourselves heard this voice that came from heaven. We were with him on the sacred mountain.

19We also have the message of the prophets. This message can be trusted completely. You must pay attention to it. The message is like a light shining in a dark place. It will shine until the day Jesus comes. Then the Morning Star will rise in your hearts. 20Above all, here is what you must understand. No prophecy in Scripture ever came from a prophet’s own understanding of things. 21Prophecy never came simply because a prophet wanted it to. Instead, the Holy Spirit guided the prophets as they spoke. So, although prophets are human, prophecy comes from God.