馬太福音 2 – CCBT & HCB

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

馬太福音 2:1-23

智者來朝拜

1希律王執政期間,耶穌降生在猶太伯利恆城。

當時有幾位智者2·1 智者」或譯「占星家」下同7節和16節。從東方來到耶路撒冷2問道:「那生來做猶太人之王的在哪裡呢?我們在東方看見祂的星,特來朝拜祂。」

3希律王聽後,心裡不安,全城的人都感到不安。 4希律王就召來祭司長和律法教師,問他們:「基督在哪裡降生呢?」

5他們回答說:「在猶太伯利恆,因為先知這樣記載,

6猶大地區的伯利恆啊!

你在猶大各城中並不是最小的,

因為有一位君王要從你那裡出來,

牧養我的以色列子民。』」

7於是,希律暗中召見那幾位智者,仔細查問那星出現的準確時間, 8然後派他們去伯利恆,並吩咐道:「你們去仔細尋訪那個小孩,找到了,就回來報信,我也好去朝拜祂。」

9他們聽了王的吩咐,就去了。忽然,那顆曾在東方出現的星又出現在他們前面,引領他們來到小孩耶穌所在的地方,便停下來。 10他們看見那顆星,喜出望外。

11他們進了屋子,看見孩子和祂母親瑪麗亞,就俯伏在地上拜祂,並打開盛寶物的盒子獻上黃金、乳香和沒藥作禮物。 12他們在夢中得到指示不可回希律那裡,便改道返回了家鄉。

逃往埃及

13他們離開之後,主的天使在夢中向約瑟顯現,說:「起來,帶著小孩子和祂母親逃往埃及,住在那裡等候我的通知,因為希律要尋找這孩子,殺害祂。」 14於是,約瑟起來帶著孩子和祂母親連夜逃往埃及15並在那裡一直住到希律死了。這就應驗了主藉著先知所說的話:「我把兒子從埃及召出來。」

16希律見自己被智者愚弄,大為惱怒,便照著智者所說的時間推算,下令把伯利恆附近兩歲以下的男孩殺光。 17這正應驗了耶利米先知的話:

18「在拉瑪有痛哭哀號的聲音,

拉結在為兒女哀慟,

不肯接受安慰,

因為他們都死了!」

定居拿撒勒

19希律死後,主的天使在夢中向在埃及約瑟顯現,說: 20「起來,帶著孩子和祂母親回以色列去吧!因為要殺害孩子的人已經死了。」 21約瑟就起來,帶著孩子和祂母親返回以色列

22約瑟聽聞亞基勞繼承父親希律的王位統治猶太,就不敢回猶太。這時,他在夢中得到主的指示,便前往加利利地區, 23定居在拿撒勒鎮。這應驗了先知的話:「祂將被稱為拿撒勒人。」

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 2:1-23

Ziyarar Masana

1Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana,2.1 A al’adance Masu Hikima daga gabas suka zo Urushalima 2suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas2.2 Ko kuwa a tauraro sa’ad da ya taso mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”

3Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima. 4Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi. 5Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.

6“ ‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda,

ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba,

gama daga cikinki mai mulki zai zo,

wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’2.6 Mik 5.2

7Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana. 8Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”

9Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake. 10Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai. 11Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur. 12Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.

Tserewa zuwa Masar

13Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”

14Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar, 15inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”2.15 Hos 11.1

16Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan ’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan. 17Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,

18“An ji murya a Rama,

tana kuka da makoki mai tsanani,

Rahila ce take kuka domin ’ya’yanta,

an kāsa ta’azantar da ita,

don ba su.”2.18 Irm 31.15

Komowa zuwa Nazaret

19Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar, 20ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”

21Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila. 22Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili, 23ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”