路加福音 21 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

路加福音 21:1-38

穷寡妇的奉献

1耶稣抬头观看,见有钱人正把捐项投进奉献箱里, 2又见一个穷寡妇投进两个小铜钱, 3就说:“我实在告诉你们,这位穷寡妇奉献的比其他人都多。 4因为他们不过奉献了自己剩余的,但这穷寡妇却奉献了她赖以为生的一切。”

预言将来的事

5有些人正在谈论由精美的石头和珍贵的供物所装饰的圣殿, 6耶稣说:“你们现在所见到的,将来有一天要被完全拆毁,找不到两块叠在一起的石头。”

7他们问:“老师,这些事什么时候会发生呢?发生的时候有什么预兆呢?”

8耶稣回答说:“你们要小心提防,不要被迷惑。因为将来会有许多人冒我的名来,说,‘我就是基督’,或说,‘时候到了’,你们切勿跟从他们。 9你们听见打仗和叛乱的事,不要害怕,因为这些事一定会先发生,但末日将不会立刻来临。”

10耶稣接着说:“民族将与民族互斗,国家将与国家相争, 11将有大地震,各处将有饥荒和瘟疫,天上也将出现恐怖的景象和大异兆。

12“这些事情出现之前,人们要拘捕你们,迫害你们,把你们押到会堂和监牢,你们将为了我的名而被君王和官长审问。 13那时,正是你们为我做见证的好机会。 14你们要立定心志,不要为怎样申辩而忧虑, 15因为我会赐给你们口才、智慧,使你们的仇敌全无反驳的余地。 16你们将被父母、弟兄、亲戚、朋友出卖,你们有些人会被他们害死。 17你们将为我的名而被众人憎恨, 18但你们连一根头发也不会失落。 19你们只要坚忍到底,必能保全自己的灵魂。

20“你们看见耶路撒冷被重兵包围时,就知道它被毁灭的日子快到了。 21那时,住在犹太地区的人要赶快逃到山上去,住在城里的人要跑到城外,住在乡村的人不要进城, 22因为那是报应的日子,要应验圣经的全部记载。 23那时,孕妇和哺育婴儿的母亲们可就遭殃了!因为将有大灾难降在这地方,烈怒要临到这些人民。 24他们要死在刀剑之下,要被掳到外国去。耶路撒冷要被外族人蹂躏,直到外族人肆虐的日期满了为止。

25“日月星辰必显出异兆,怒海汹涌、波涛翻腾,令各国惊恐不安。 26天体必震动,人类想到世界要面临的事都吓得魂不附体。 27那时,他们要看见人子驾着云、带着能力和极大的荣耀降临。 28当这些事发生时,你们要昂首挺胸,因为你们蒙救赎的日子近了。”

警醒祷告

29耶稣又讲了一个比喻:“看看无花果树和其他树木吧。 30当你们看见树木发芽长叶时,就知道夏天近了。 31同样,当你们看见这些事情发生时,就知道上帝的国近了。

32“我实在告诉你们,这个世代还没有过去,这一切都要发生。 33天地都要消逝,但我的话永不消逝。

34“你们要小心,不要被宴乐、醉酒和人生的挂虑所拖累,免得那日子像网罗般突然临到你们, 35因为那日子将要这样临到世上每一个人。 36你们要时刻警醒,常常祷告,使你们能逃过这一切将要发生的灾难,并能站在人子面前。”

37耶稣每天在圣殿里讲道,晚上则到城外的橄榄山上过夜。 38百姓一早都赶去圣殿听祂的教导。

Hausa Contemporary Bible

Luka 21:1-38

Bayarwar gwauruwa

(Markus 12.41-44)

1Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin. 2Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu. 3Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran. 4Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”

Alamun ƙarshen zamani

(Mattiyu 24.1,2; Markus 13.1,2)

5Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce, 6“Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”

(Mattiyu 24.3-14; Markus 13.3-13)

7Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”

8Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su. 9Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”

10Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki. 11Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.

12“Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana. 13Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su. 14Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku. 15Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata. 16Har iyayenku, da ’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku. 17Duk mutane za su ƙi ku saboda ni. 18Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba. 19Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.

(Mattiyu 24.15-21; Markus 13.14-19)

20“In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa. 21A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin. 22Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta. 23Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon ’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan. 24Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su ’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.

(Mattiyu 24.29-31; Markus 13.24-27)

25“Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku. 26Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama. 27A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma. 28Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”

(Mattiyu 24.32-35; Markus 13.28-31)

29Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa. 30A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa. 31Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.

32“Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika. 33Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.

34“Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko. 35Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya. 36Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”

37Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun. 38Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.