路加福音 22 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

路加福音 22:1-71

犹大出卖耶稣

1除酵节,又名逾越节,快到了。 2祭司长和律法教师因为害怕百姓,便密谋如何杀害耶稣。 3这时,撒旦进入加略犹大的心,这人原是十二使徒之一。 4他去见祭司长和圣殿护卫长,商议如何把耶稣出卖给他们, 5他们喜出望外,答应给犹大一笔酬金。 6犹大同意了,便伺机找百姓不在的场合将耶稣交给他们。

最后的晚餐

7除酵节到了,那天要宰杀逾越羊羔。 8耶稣差派彼得约翰出去,说:“你们为我们准备逾越节吃的晚餐。”

9他们问:“你要我们到哪里去预备呢?”

10耶稣回答说:“你们进城的时候,一个男子会扛着一瓶水迎面走来,你们要跟着他,他进哪所房子,你们也进去, 11对房子的主人说,‘老师问你客房在哪里,祂要和门徒在里面吃逾越节的晚餐。’ 12那主人会带你们到楼上一间布置整齐的大房间,你们就在那里预备吧。”

13他们进了城,所遇见的果然和耶稣所说的一样。他们便在那里预备逾越节的晚餐。

设立圣餐

14晚餐时,耶稣和使徒们一同坐席。 15耶稣对他们说:“我一直盼望在受难之前和你们同吃这个逾越节的宴席。 16我告诉你们,在这宴席成就在上帝的国度之前,我不会再吃这宴席了。”

17祂接过杯来,祝谢后,说:“你们拿去分着喝吧。 18我告诉你们,在上帝的国降临之前,我不会再喝这葡萄酒了。”

19接着,祂拿起饼来,祝谢后,掰开递给他们,说:“这是我为你们牺牲的身体,你们今后也要这样做,以纪念我。”

20饭后,祂又举起杯来,说:“这杯是用我的血立的新约,这血是为你们流的。

21“但是看啊,那出卖我之人的手和我的手都在桌子上。 22按照所定的,人子要死去,但那出卖人子的人有祸了!” 23他们开始彼此追问谁会出卖耶稣。

谁最伟大

24门徒又开始争论他们当中谁最伟大。 25耶稣对他们说:“外族人有君王统治他们,那些统治者被称为恩主, 26但你们不可这样。相反,你们中间地位最高的,要像最卑微的;做首领的,要像服侍人的。 27坐着吃饭的和伺候的哪个地位高呢?难道不是坐着的那个吗?然而,我在你们当中是服侍人的。

28“在我患难之时,你们一直在我身边, 29所以,我父怎样将国赐给我,我也照样将国赐给你们, 30使你们在我的国中和我一同坐席,并且坐在宝座上审判以色列的十二个支派。”

预言彼得不认主

31耶稣说:“西门西门!撒旦已经要求像筛麦子一样筛你们, 32但我已经为你祷告了,叫你不至于失去信心。你回头以后,要让你的弟兄刚强。”

33西门·彼得说:“主啊,我愿意和你一起坐牢,一起受死!”

34耶稣说:“彼得,我告诉你,明早鸡叫之前,你会三次不认我。”

35耶稣又问门徒:“我派你们出去的时候,无钱袋、背包和鞋子,你们有任何缺乏吗?”

他们答道:“没有。”

36耶稣说:“但现在如果有钱袋或背包,都要带着;如果没有刀剑,要卖掉衣服买刀剑。 37我告诉你们,‘祂要被列在罪犯中’这句经文必在我身上应验,因为圣经上有关我的事情快要实现了。”

38他们说:“主啊,请看,这里有两把刀。”耶稣说:“够了。”

橄榄山上的祷告

39耶稣离开,像往常一样前往橄榄山,门徒也跟去了。 40到了山上,祂对门徒说:“你们要祷告,以免陷入诱惑!”

41然后,祂独自走到离门徒约有扔一块石头那么远的地方跪下祷告: 42“父啊,若你愿意,求你撤去此杯。然而,愿你的旨意成就,而非我的意愿。” 43有一位从天上来的天使向祂显现,给祂加添力量。

44祂心中极其悲痛,祷告更恳切,汗珠如血滴在地上。

45祂祷告完后,便起身回到门徒那里,看见他们因忧愁而疲惫地睡着了, 46就说:“你们为什么睡觉呢?要起来祷告,以免陷入诱惑!”

耶稣被捕

47耶稣还在说话的时候,十二使徒中的犹大已带着一群人赶到,他上前亲吻耶稣。 48耶稣对他说:“犹大,你用亲吻的暗号来出卖人子吗?”

49跟随耶稣的人见他们来势汹汹,就说:“主啊,我们该拔刀抵抗吗?” 50其中一人拔刀朝大祭司的奴仆砍过去,削掉了他的右耳。

51耶稣却说:“住手!够了!”于是祂摸那奴仆的耳朵,治好了他, 52然后对前来抓祂的祭司长、圣殿护卫长和长老说:“你们像对付强盗一样拿着刀棍来抓我吗? 53我天天和你们一起在圣殿里,你们没有抓我。但现在正是黑暗当权、你们得势的时候了!”

彼得不认主

54他们把耶稣押到大祭司的府第。彼得远远地跟在后面。

55他们在庭院当中生起了火,围坐取暖,彼得也坐在他们中间。 56有个婢女看见彼得坐在火堆边,打量他一番后,说:“这人是与耶稣一伙的!”

57彼得却否认说:“你这女子,我不认识祂。”

58过了一会儿,又有个人看见了彼得,就说:“你也是跟他们一伙的!”

彼得说:“你这人,我不是!”

59大约一小时之后,又有人指着彼得肯定地说:“这人确实是和耶稣一伙的,因为他也是加利利人。”

60彼得说:“你这人,我不知道你在说什么!”话才出口,鸡就叫了。

61这时,主转过头来望着彼得彼得想起主对他说的话:“明早鸡叫之前,你会三次不认我。” 62他就到外面,痛哭起来。

在公会受审

63看守耶稣的人嘲弄祂,殴打祂, 64蒙住祂的眼睛,对祂说:“说预言吧!是谁在打你?” 65还说了许多侮辱祂的话。

66天亮后,民间的长老、祭司长和律法教师聚在一起,把耶稣押到他们的公会, 67对祂说:“如果你是基督,就告诉我们。”

耶稣说:“即使我告诉你们,你们也不会相信。 68如果我问你们,你们也不会回答。 69但从今以后,人子要坐在全能上帝的右边。”

70他们都问:“那么,你是上帝的儿子吗?”耶稣回答说:“你们说我是。”

71他们说:“我们还需要什么见证呢?我们已经听见祂自己说的了。”

Hausa Contemporary Bible

Luka 22:1-71

Yahuda ya yarda ya bashe Yesu

(Mattiyu 26.1-5,14,16; Markus 14.1,2,10,11; Yohanna 11.45-53)

1Yanzu fa, Bikin Burodi Marar Yistin da ake kira Bikin Ƙetarewa ya yi kusa, 2manyan firistoci da malaman dokoki kuma suna neman yadda za su kashe Yesu a ɓoye, don suna tsoron mutane. 3Shaiɗan kuwa ya shiga Yahuda, wanda ake kira Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun. 4Sai Yahuda ya je ya tattauna da manyan firistoci, da ma’aikatan ’yan gadin haikali, a kan yadda zai ba da Yesu a gare su. 5Suka kuwa yi murna, suka yarda su ba shi kuɗi. 6Ya ko yarda, ya fara neman zarafin da zai ba da Yesu a gare su, sa’ad da taro ba sa nan tare da shi.

Abincin yamma na ƙarshe

(Mattiyu 26.17-25; Markus 14.12-21; Yohanna 13.21-30)

7Sai ranar Bikin Burodi Marar Yisti ta kewayo, wato, ranar hadayar ɗan ragon kafara na Bikin Ƙetarewa. 8Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yohanna, ya ce musu, “Ku je ku yi shirye-shiryen Bikin Ƙetarewar da za mu ci.”

9Suka tambaye shi suka ce, “Ina kake so mu je mu yi shirin?”

10Ya amsa ya ce, “Sa’ad da kuka shiga cikin gari, za ku sadu da wani mutum yana ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi zuwa gidan da zai shiga. 11Ku ce wa maigidan, Malam ya aike mu mu ce maka, ‘Ina ɗakin baƙi, inda ni da almajiraina za mu ci abincin Bikin Ƙetarewa?’ 12Zai nuna muku wani babban ɗakin sama a shirye. Nan za ku yi shirin.”

13Sai suka tafi, suka kuma iske kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.

(Mattiyu 26.26-30; Markus 14.22-26; 1 Korintiyawa 11.23-25)

14Da lokaci ya yi, sai Yesu ya zauna tare da manzanninsa don cin abinci. 15Sai ya ce musu, “Na yi marmari ƙwarai don in ci wannan Bikin Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wahala. 16Ina dai gaya muku, ba zan ƙara cinsa ba, sai ya sami cika a mulkin Allah.”

17Bayan ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, sai ya ce, “Ku karɓa, ku rarraba wa junanku. 18Ina dai gaya muku, ba zan ƙara sha daga ’ya’yan inabi ba, sai mulkin Allah ya zo.”

19Sai ya ɗauki burodi ya yi godiya, ya kakkarya ya ba su, da cewa, “Wannan jikina ne, da aka bayar dominku. Ku riƙa yin haka don tunawa da ni.”

20Haka kuma, bayan abincin, ya ɗauki kwaf ruwan inabi ya ce, “Wannan kwaf ruwan inabi shi ne, na sabon alkawari cikin jinina, da aka zubar dominku. 21Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni. 22Ɗan Mutum zai mutu kamar yadda aka ƙaddara, amma kaiton mutumin da zai bashe shi.” 23Sai suka fara tambayar junansu, ko wane ne a cikinsu zai yi wannan.

24Gardama ta tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne a cikinsu ya fi girma. 25Yesu ya ce musu, “Sarakunan Al’ummai suna nuna iko a kan mutanensu, kuma waɗanda suke nuna iko a kansu, suna kiran kansu Masu Taimakon mutane. 26Amma ku, kada ku zama haka. A maimakon haka, sai dai wanda ya fi girma a cikinku, ya zama kamar wanda ya fi ƙanƙanta, wanda kuma ke mulki, ya zama kamar mai hidima. 27Wane ne ya fi girma? Wanda yake zaune a tebur ne, ko kuma shi da yake yin hidima? Ashe, ba wanda yake zaune a tebur ba ne? Amma ga ni, ni mai yin hidima ne a cikinku. 28Ku ne kuka tsaya tare da ni a gwaje-gwajen da na sha. 29Daidai kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka ni ma nake ba ku. 30Saboda ku ci, ku sha a teburina a cikin mulkina. Kuma ku zauna a kan gadon sarauta, ku yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a.

(Mattiyu 26.31-35; Markus 14.27-31; Yohanna 13.36-38)

31“Siman, Siman, Shaiɗan ya nemi izini ya sheƙe ka22.31 Girik yana da ku ne a nan kamar alkama. 32Amma na yi maka addu’a, Siman, domin kada bangaskiyarka ta kāsa. Bayan ka juyo, ka ƙarfafa ’yan’uwanka.”

33Amma ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina a shirye in tafi tare da kai har kurkuku, ko mutuwa ma.”

34Yesu ya ce, “Ina gaya maka Bitrus, kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.”

35Sai Yesu ya tambaye, su ya ce, “Lokacin da na aike ku ba tare da jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma ba, kun rasa wani abu?”

Suka amsa, “Babu.”

36Ya ce musu, “Amma yanzu, in kuna da jakar kuɗi, ko jaka, ku ɗauka. In kuma ba ku da takobi, ku sayar da rigarku, ku saya. 37A rubuce yake cewa, ‘An lissafta shi tare da masu zunubi.’ Ina kuwa gaya muku, dole wannan ya cika a kaina. I, abin da aka rubuta a kaina yana kusan cikawa.”

38Almajiran suka ce, “Duba Ubangiji, ga takuba biyu.”

Yesu ya ce, “Ya isa.”

Yesu ya yi addu’a a Dutsen Zaitun

(Mattiyu 26.36-46; Markus 14.32-42)

39Yesu ya fita zuwa Dutsen Zaitun kamar yadda ya saba, almajiransa kuma suka bi shi. 40Da ya kai wurin, sai ya ce musu, “Ku yi addu’a don kada ku fāɗi cikin jarraba.” 41Sai ya janye daga wurinsu, misalin nisan jifa, ya durƙusa a ƙasa ya yi addu’a, 42“Uba, in ka yarda, ka ɗauke mini wannan kwaf, amma ba nufina ba, sai dai naka.” 43Wani mala’ika daga sama ya bayyana gare shi, ya ƙarfafa shi. 44Domin tsananin azaba, sai ya ƙara himma cikin addu’a, zuffansa kuma na ɗigowa ƙasa kamar jini.

45Da ya tashi daga addu’a, ya koma inda almajiransa suke, sai ya iske su suna barci, daga gajiyar baƙin ciki. 46Ya tambaye su, “Don me kuke barci? Ku tashi ku yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba.”

An kama Yesu

(Mattiyu 26.47-56; Markus 14.43-50; Yohanna 18.3-11)

47Yana cikin magana sai ga taro sun zo. Mutumin nan da ake kira Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun, shi ya bi da su. Sai ya matso kusa da Yesu don yă yi masa sumba. 48Amma Yesu ya tambaye shi ya ce, “Yahuda, ashe, da sumba za ka bashe Ɗan Mutum?”

49Da masu bin Yesu suka ga abin da zai faru, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takubanmu ne?” 50Sai ɗayansu ya kai sara ga bawan babban firist, ya sare kunnen damansa.

51Amma Yesu ya amsa ya ce, “Kada a ƙara yin wannan!” Sai ya taɓa kunnen mutumin da aka sara, ya warkar da shi.

52Sai Yesu ya ce wa manyan firistoci, da ma’aikatan ’yan gadin haikali, da dattawa, waɗanda suka zo don su kama shi, “Ina jagoran wani tawaye ne, da za ku zo da takuba da sanduna? 53Kullum ina tare da ku a filin haikali, amma ba ku kama ni ba. Amma wannan ne sa’a naku, lokacin da duhu yake mulki.”

Bitrus ya yi mūsun sanin Yesu

(Mattiyu 26.57,58,67-75; Markus 14.53,54,66-72; Yohanna 18.12-18,25-27)

54Sai suka kama shi suka kai shi gidan babban firist. Bitrus ya bi su daga nesa. 55Amma da suka hura wuta a tsakiyar harabar gidan, kowa ya zauna, sai Bitrus ya zo ya zauna tare da su. 56Wata baiwa ta gan shi zaune kusa da wutar. Ta dube shi sosai sa’an nan, ta ce, “Ai, wannan mutum ma yana tare da shi.”

57Amma ya yi mūsu ya ce, “Mace, ban san shi ba!”

58Bayan ɗan lokaci kaɗan, wani dabam ya gan shi ya ce, “Kai ma ɗayansu ne.”

Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ba na cikinsu!”

59Bayan kamar sa’a ɗaya, sai wani mutum ya ce, “Ba shakka, mutumin nan ma yana tare da shi, don shi mutumin Galili ne.”

60Bitrus ya amsa ya ce, “Kai, ban ma san abin da kake magana a kai ba!” Yana cikin magana, sai zakara ya yi cara. 61Ubangiji kuma ya juya ya kafa wa Bitrus ido. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Ubangiji ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau, za ka yi mūsun sanina sau uku.” 62Sai ya fita waje, ya yi kuka mai zafi.

Masu gadi sun yi wa Yesu ba’a

(Mattiyu 26.59-66; Markus 14.55-64; Yohanna 18.19-24)

63Mutanen da suke gadin Yesu suka fara masa ba’a da dūka. 64Suka rufe masa idanu suna tambaya cewa, “Ka yi annabci! Wa ya mare ka?” 65Suka kuma yi masa waɗansu baƙaƙen maganganu masu yawa.

Yesu a gaban Bilatus da Hiridus

66Da gari ya waye, sai majalisar dattawa na mutane, da manyan firistoci, da malaman dokoki, suka taru wuri ɗaya. Sai aka kawo Yesu a gabansu. 67Suka ce, “Ka faɗa mana, ko kai ne Kiristi?”

Yesu ya amsa ya ce, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ni ba, 68in kuma na yi muku tambaya ba za ku iya ba ni amsa ba. 69Amma daga yanzu, Ɗan Mutum zai zauna a hannun dama na Allah Mai Iko.”

70Sai dukansu suka yi tambaya suka ce, “Wato, kai Ɗan Allah ke nan?”

Ya amsa ya ce, “Kun faɗa daidai, ni ne.”

71Sai suka ce, “Wace shaida kuma muke nema? Ai, mun ji abin da ya ce da bakinsa.”