约翰一书 3 – CCB & HCB

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

约翰一书 3:1-24

上帝的儿女

1你们看,父上帝何等爱我们,称我们为祂的儿女!我们也实在是祂的儿女,世人之所以不认识我们,是因为他们不认识父上帝。 2亲爱的弟兄姊妹,我们现在是上帝的儿女,将来如何还未显明。但我们知道,当主显现的时候,我们必会像祂,因为我们必见到祂的本体。 3凡心存这种盼望的人都会自洁,因为主是圣洁的。

4犯罪的人都违背上帝的律法,违背上帝的律法就是罪。 5你们知道,耶稣降世是为了除掉人的罪,祂自己并没有罪。 6住在祂里面的人不会一直犯罪;一直犯罪的人既没见过祂也不认识祂。

7孩子们,不要受人迷惑,要知道行义的才是义人,正如主是公义的。 8一直犯罪的人是属魔鬼的,因为魔鬼从起初便犯罪,但上帝儿子的显现是为了摧毁魔鬼的工作。 9从上帝生的人不会继续犯罪,因为他里面有上帝的生命3:9 上帝的生命”希腊文是“上帝的种子”。。他不能犯罪,因为他是从上帝生的。 10这样,就可以看出谁是上帝的儿女,谁是魔鬼的儿女。凡不按公义行事、不爱弟兄姊妹的,都不是上帝的儿女。

彼此相爱

11我们应当彼此相爱,这是你们起初听见的信息。 12不要步该隐的后尘。他属于那恶者,杀害了自己的弟弟。他为什么要杀害自己的弟弟呢?因为他的行为邪恶,而他弟弟秉行公义。

13弟兄姊妹,世人若恨你们,不要惊奇。 14我们因爱弟兄姊妹,便知道自己已经出死入生了。不爱弟兄姊妹的,仍然陷在死亡中。 15恨弟兄姊妹的就是杀人的,你们知道杀人的没有永生。 16主耶稣为我们舍命,我们由此便知道什么是爱,我们也应当为弟兄姊妹舍命。 17如果一个丰衣足食的人看见贫穷的弟兄姊妹,却毫无怜悯之心,怎能说他爱上帝呢? 18所以,孩子们啊,不要单在口头上说爱人,总要以真诚的行动表现出来。

19-20这样,我们必知道自己属于真理,即使我们心中自责,也可以在上帝面前心安,因为上帝比我们的心大,祂知道一切。

21亲爱的弟兄姊妹,我们若能凡事问心无愧,就可以在上帝面前坦然无惧。 22这样,我们无论向上帝祈求什么,都必得到,因为我们遵守祂的命令,做祂喜悦的事。 23其实上帝的命令是:我们要信祂儿子耶稣基督的名,遵照祂的命令彼此相爱。 24遵行上帝命令的人就住在上帝里面,上帝也住在他里面。我们借着上帝赐给我们的圣灵知道:祂住在我们里面。

Hausa Contemporary Bible

1 Yohanna 3:1-24

1Dubi irin ƙaunar da Uba ya ƙaunace mu da ita mana, har ana ce da mu ’ya’yan Allah! Haka kuwa muke! Dalilin da ya sa duniya ba tă san mu ba shi ne, don ba tă san shi ba. 2Abokaina ƙaunatattu, yanzu, mu ’ya’yan Allah ne, kuma abin da za mu zama nan gaba ba a riga an bayyana ba. Sai dai mun san cewa sa’ad da Kiristi ya bayyana, za mu zama kamar sa, domin za mu gan shi kamar yadda yake. 3Duk mai wannan bege a cikinsa yakan tsarkake kansa, kamar yadda shi Kiristi yake da tsabta.

4Duk mai yin zunubi yana karya doka ne; tabbatacce, zunubi, karya doka ne. 5Sai dai kun san cewa Kiristi ya bayyana ne domin yă ɗauke zunubanmu. A cikinsa kuwa babu zunubi. 6Ba mai rayuwa a cikinsa da yake cin gaba da yin zunubi. Kowa da yake aikata zunubi, bai taɓa ganinsa ba, bai ma san shi ba.

7’Ya’yana ƙaunatattu, kada ku yarda wani yă ruɗe ku. Duk mai yin abin da yake daidai mai adalci ne, yadda Kiristi yake mai adalci. 8Duk mai aikata abin da yake zunubi shi na Iblis ne, domin Iblis mai aikata zunubi ne tun farko. Dalilin da ya sa Ɗan Allah ya bayyana kuwa shi ne don yă rushe aikin Iblis. 9Babu haifaffe na Allah da zai ci gaba da yin zunubi, domin iri na Allah yana a cikinsa; ba zai iya ci gaba da yin zunubi ba, domin haifaffe ne na Allah. 10Ta haka muka san waɗanda suke ’ya’yan Allah da kuma waɗanda suke ’ya’yan Iblis. Duk wanda ba ya yin abin da yake daidai, ba ɗan Allah ba ne; haka ma wanda ba ya ƙaunar ɗan’uwansa.

Ku ƙaunaci juna

11Wannan shi ne saƙon da kuka ji tun farko. Ya kamata mu ƙaunaci juna. 12Kada ku zama kamar Kayinu, wanda ya zama na mugun nan, ya kuma kashe ɗan’uwansa. Me ya sa ya kashe shi? Domin ayyukansa mugaye ne, na ɗan’uwansa kuma na adalci ne. 13Kada ku yi mamaki ’yan’uwana, in duniya ta ƙi ku. 14Mun san cewa mun riga mun ratsa daga mutuwa zuwa rai, domin muna ƙaunar ’yan’uwanmu. Duk wanda ba ya ƙauna matacce ne har yanzu. 15Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa.

16Yadda muka san ƙauna ke nan, wato, Yesu Kiristi ya ba da ransa dominmu. Ya kamata mu ma mu ba da rayukanmu domin ’yan’uwanmu. 17In wani yana da arziki, ya kuma ga ɗan’uwansa cikin rashi, bai kuwa taimake shi ba, anya, ƙaunar Allah tana a cikinsa kuwa? 18’Ya’yana ƙaunatattu, kada mu yi ƙauna da fatar baki kawai, sai dai mu nuna ta ta wurin aikatawa da kuma gaskiya.

19Ta haka muka san cewa mu na gaskiya ne, kuma za mu iya tsaya a gaban Allah ba tare da rawar jiki ba. 20Idan zuciyarmu ta nuna mana muna da laifi, mun san cewa Allah ya fi zuciyarmu, ya kuma san dukan kome. 21Abokaina ƙaunatattu, in zukatanmu ba su ba mu laifi ba, muna da ƙarfin halin tsayawa a gaban Allah ke nan. 22Muna kuma samun dukan abin da muka roƙa daga gare shi, domin muna biyayya da umarnansa, muna kuma yin abin da ya gamshe shi. 23Umarninsa kuwa shi ne, mu gaskata da sunan Ɗansa, Yesu Kiristi, mu kuma ƙaunaci juna kamar yadda ya umarce mu. 24Waɗanda suke biyayya da umarnansa kuwa suna rayuwa a cikinsa, shi kuma a cikinsu. Ta haka muka san cewa yana raye a cikinmu. Mun san haka ta wurin Ruhun da ya ba mu.