Zjevení 2 – SNC & HCB

Slovo na cestu

Zjevení 2:1-29

Do Efezu: Chybí vám to nejdůležitější – láska

1Představiteli efezského sboru napiš:

Hovoří k vám ten, který je ve vašich sborech neustále činně přítomen a na němž jsou jejich představitelé plně závislí. 2-3Vím o tom, co jste už vykonali a také o vaší usilovné práci. Jste vytrvalí, stateční a trpěliví, snášíte pro mne mnoho a neochabujete. Cením si toho, že jste se nenechali svést falešnými apoštoly, ale vyzkoušeli jste je a odhalili jejich lži. Dobře děláte, že jste ostře vystoupili proti zastáncům nevázaného života, který já také odsuzuji.

4Musím vám však vytknout, že jste polevili v lásce; není už tak vřelá jako na počátku. 5-6Vzpomeňte si, jak to s vámi bylo, jděte do sebe a navraťte se k činorodé lásce. Nebudete-li činit pokání, hrozí vašemu sboru zánik.

7Slyšte, co vám říká Bůh: Kdo zvítězí, okusí ovoce stromu věčného života, který je v Božím ráji.

Do Smyrny: Věrnost osvědčíte v utrpení

8Představiteli smyrenského sboru napiš:

Hovoří k vám První a Poslední, ten, který zemřel a ožil. 9Znám vaše činy, těžkosti a chudobu – ale přesto jste bohatí! Vím, jak vás lživě obviňují ti, kteří se pyšní svou pravověrností, ale pracují vlastně pro satana. 10Nebojte se utrpení, které ještě přijde. Ďábel dostane některé z vás i do vězení a bude zkoušet vaši věrnost po deset dnů. Buďte věrní až do smrti a dám vám věčný život – cenu vítězů.

11Slyšte, co vám říká Bůh: Kdo zvítězí, nepodlehne věčné smrti.

Do Pergamu: Zbavte se tolerance k hříchu

12Představiteli pergamského sboru napiš:

Hovoří k vám ten, jehož slovo platí. 13Vím, na jak nebezpečném místě působíte. Hlásíte se k mému jménu přímo v satanově sídelním městě, ve stínu jeho trůnu. Nezapřeli jste víru ve mne ani tehdy, když byl umučen můj věrný svědek Antipas.

14-15Jednu věc vám však přece musím vytknout: klidně ponecháváte mezi sebou ty, kteří se pod rouškou křesťanské svobody účastní nestydatých orgií, a to já nenávidím. 16Dejte tu záležitost rychle do pořádku, nebo přijdu a vynesu nad nimi spravedlivý rozsudek.

17Slyšte, co vám říká Bůh: Toho, kdo zvítězí, dokonale nasytím. Vtisknu mu nový charakter a poctím ho svým osobním přátelstvím.

Do Tyatiry: Žádné kompromisy s hříchem

18Představiteli tyatirského sboru napiš:

Hovoří k vám Boží Syn, jehož oči září jako oheň a nohy žhnou jako rozpálená mosaz.

19Znám vaše činy lásky, víry, trpělivé naděje a vím, že v tom všem rostete. 20Avšak to vám musím vytknout, že mezi sebou trpíte tu ženu, která se vydává za prorokyni, ale svádí moje věrné k sexuálním zvrácenostem a modlářským hostinám. 21Dal jsem jí lhůtu k nápravě, ale ona provádí své nečisté rejdy dál. 22-23Dopustím těžkou nemoc na ni i na ty, které svedla, pokud nebudou činit pokání z toho, co páchali; nezůstane po ní ani památka. Tak bude jasné všem sborům, že každému vidím do svědomí a každého budu soudit podle jeho činů.

24Vám, kteří odmítáte její učení a nejste zvědavi na to, čemu pyšně říká „satanova nejhlubší tajemství“, vám, věrní Tyatirští, slibuji: víc už na vás nenaložím. 25Musíte se však pevně držet toho, čemu jste uvěřili, dokud nepřijdu.

26Tomu, kdo zvítězí a splní mou vůli, dám mocné poslání ke všem lidem. 27Bude mít mezi nimi takovou autoritu, jakou dal Otec mně, a to, na čem si zakládají, rozbije jako hliněné hrnce. 28Vítězům vyjdu vstříc jako jitřní hvězda, která ohlašuje den. 29Slyšte, to vám říká Bůh.

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 2:1-29

Zuwa ga ikkilisiya a Afisa

1“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Afisa, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomi na wannan wanda yake riƙe da taurari bakwai a hannunsa na dama yana kuma tafiya a tsakanin alkukan fitilu bakwai na zinariya.

2Na san ayyukanka, faman aikinka da daurewarka. Na san cewa ba ka iya haƙuri da mugayen mutane, ka gwada waɗanda suke cewa su manzanni ne, alhali kuwa ba haka ba ne, ka kuwa tarar cewa su na ƙarya ne. 3Kai kam ka daure ka kuma jimre da wahala saboda sunana, ba ka kuwa gaji ba.

4Duk da haka ina riƙe da wannan game da kai. Ka watsar da ƙaunarka ta farko. 5Ka tuna da matsayinka a dā kafin ka fāɗi! Ka tuba ka kuma yi ayyukan da ka yi da fari. In ba ka tuba ba, zan zo wajenka in ɗauke wurin ajiye fitilanka daga inda yake. 6Sai dai kana da wannan abu mai kyau. Ka ƙi ayyukan Nikolaitawa da ni ma nake ƙi.

7Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ikon ci daga itacen rai, da yake cikin aljannar Allah.

Zuwa ga ikkilisiya a Simirna

8“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Simirna, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomin wannan da yake na Farko da na Ƙarshe, wanda ya mutu ya kuma sāke tashi da rai.

9Na san wahalarka da kuma talaucinka, duk da haka kai mai arziki ne! Na san ɓata suna da waɗannan suke yi maka waɗannan da suke cewa su Yahudawa ne alhali kuwa ba haka ba ne, su dai majami’ar Shaiɗan ne. 10Kada ka ji tsoron wahalar da kake gab da sha. Ina gaya maka, Iblis zai sa waɗansunku a kurkuku don yă gwada ku. Za ku sha tsanani na kwana goma. Ka yi aminci ko da za a kashe ka, ni kuwa zan ba ka rawanin rai.

11Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara mutuwa ta biyu ba za tă cuce shi ba ko kaɗan.

Zuwa ga ikkilisiya a Fergamum

12“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Fergamum, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomin wannan wanda yake da takobi mai kaifi biyu.

13Na san inda kake da zama, inda Shaiɗan yana da gadon sarautarsa. Duk da haka ka riƙe sunana da gaske. Ba ka yi mūsun bangaskiyarka gare ni ba, har ma a kwanakin Antifas, amintaccen mashaidina, wanda aka kashe a birninku, inda Shaiɗan yake zama.

14Duk da haka, ina da abubuwa kima game da kai. Kana da mutane a can waɗanda suke riƙe da koyarwar Bala’am, wanda ya koya wa Balak yă ja hankalin Isra’ilawa su yi zunubi ta wurin cin abincin da aka miƙa wa gumaka hadaya, su kuma yi fasikanci. 15Haka ma kana da waɗanda suke riƙe da koyarwar Nikolaitawa. 16Saboda haka ka tuba! In ba haka ba, zan zo wajenka ba da daɗewa ba in yaƙe su da takobin bakina.

17Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara zan ba shi kaɗan daga cikin ɓoyayyiyar Manna. Zan kuma ba shi farin dutse tare da sabon suna a rubuce a bisansa, sananne kawai ga mai karɓan dutsen.

Zuwa ga ikkilisiya a Tiyatira

18“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Tiyatira, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomin Ɗan Allah, wanda idanunsa suna kama da harshen wuta wanda kuma ƙafafunsa suna kama da tagullar da aka goge.

19Na san ayyukanka, ƙaunarka da bangaskiyarka, hidimarka da daurewarka, kuma cewa kana yin abubuwa a yanzu fiye da abin da ka yi da farko.

20Duk da haka, ina da wannan game da kai. Kana haƙuri da matan nan Yezebel, wadda take kira kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta tana ɓad da bayina ga yin fasikanci suka kuma ci abincin da aka miƙa wa gumaka. 21Na ba ta lokaci tă tuba daga fasikancinta, amma ba ta da niyya. 22Don haka zan jefa ta a kan gadon wahala, zan kuma sa waɗanda suke zina da ita, su sha azaba ƙwarai, sai dai in sun tuba daga hanyoyinta. 23Zan kashe ’ya’yanta. Sa’an nan dukan ikkilisiyoyi za su san cewa ni ne mai bincika zukata da tunani, zan kuwa sāka wa kowannenku gwargwadon ayyukansa.

24Yanzu, ina ce wa sauranku da kuke a Tiyatira, ku da ba ku riƙe da koyarwarta ba kuma ba ku koyi abin da suke kira zurfafan asiran Shaiɗan, ‘Ba zan ƙara muku wani nauyi ba. 25Sai dai ku riƙe abin da kuke da shi har sai na zo.’

26Gare shi wanda ya ci nasara ya kuma aikata nufina har ƙarshe, zan ba shi iko a kan al’ummai. 27‘Zai yi mulki a kansu da sandar sarauta ta ƙarfe, zai farfashe su, kamar tukwanen yumɓu’2.27 Zab 2.9 kamar yadda na karɓi iko daga Ubana. 28Zan kuma ba shi tauraron asubahi. 29Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.