Zjevení 12 – SNC & HCB

Slovo na cestu

Zjevení 12:1-17

Ďábel pronásleduje Krista a věřící, ale je poražen

1Na nebi se objevil nápadný úkaz: Žena oděná sluncem, s měsícem pod nohama a korunou z dvanácti hvězd na hlavě. 2Byla těhotná a sténala, protože přicházely její porodní bolesti. 3Vzápětí další úkaz na obloze: Veliký ohnivě zbarvený drak se sedmi hlavami a deseti rohy, na každé hlavě korunu. 4Ocasem smetl třetinu hvězd z nebe na zem. Postavil se před ženu a číhal, aby sežral její dítě, jakmile se narodí. 5Porodila chlapce, který má vládnout všem národům železnou rukou. Bůh však vzal to dítě a přenesl je ke svému trůnu. 6Žena utekla na poušť, kde ji Bůh ukrýval a pečoval o ni dvanáct set šedesát dní.

7V nebi se strhla bitva: Michael se svými anděly bojoval proti draku a jeho andělům. 8-9Veliký drak se svou družinou byl poražen, vyhnán z nebe a svržen na zem. To je ten dávný had z ráje, nepřítel, pomlouvač a svůdce všech lidí.

10Nebem zazněl mohutný hlas:

„Nyní se dovršilo dílo záchrany.

Bůh dokázal svoji plnou moc,

nastolil svoje království a Kristus se ujal vlády.

Je svržen žalobce,

který dnem i nocí osočoval naše bratry před Bohem.

11Zvítězili nad ním krví Krista,

Beránka obětovaného za ně,

a svým svědectvím o něm.

Nemilovali svůj život natolik,

aby se zalekli smrti.

12Jásejte nebesa! Jásejte,

vy na nebi!

Ale běda zemi a moři.

Vrhl se na vás ďábel a zuří – ví,

jak málo času mu zbývá.“

13Když se drak octl na zemi, začal pronásledovat tu ženu, která porodila toho chlapce. 14Ona však dostala orlí křídla, aby mohla uletět do pustiny, kde se před tím hadem ukrývala po tři a půl roku. 15Had vychrlil z tlamy mohutný proud vody, aby ženu smetl. 16Země jí však přišla na pomoc: otevřela své útroby a proud pohltila. 17Rozlícený drak se chtěl ženě pomstít, a tak rozpoutal boj proti jejím ostatním dětem, které zachovávají Boží přikázání a je jim svěřeno Ježíšovo poselství.

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 12:1-17

Mace da ƙaton maciji

1Babbar alama mai banmamaki ta bayyana a sama, mace tana lulluɓe da rana, da kuma wata a ƙarƙashin sawunta, akwai kuma rawani mai taurari goma sha biyu a kanta. 2Tana da ciki ta kuma yi kuka mai zafi yayinda take gab da haihuwa. 3Sai wata alama ta bayyana a sama, wani babban jan maciji mai kawuna bakwai da ƙahoni goma da rawani bakwai a kan kawunansa. 4Wutsiyarsa ta share kashi ɗaya bisa uku na taurari daga sararin sama ta kuma zubar da su ƙasa. Ƙaton jan macijin ya tsaya a gaban macen wadda take gab da haihuwa, don yă cinye ɗanta nan take bayan an haife shi. 5Ta haifi ɗa, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al’ummai da sandar ƙarfe. Aka fyauce ɗanta zuwa wurin Allah da kuma kursiyinsa. 6Sai macen ta gudu zuwa hamada zuwa inda Allah ya shirya dominta, inda za a lura da ita har kwana 1,260.

7Aka kuwa yi yaƙi a sama. Mika’ilu da mala’ikunsa yaƙi macijin, maciji da mala’ikunsa su ma suka mai da martani. 8Amma macijin nan ba shi da isashen ƙarfi, har suka rasa matsayinsu a sama. 9Aka jefar da ƙaton jan macijin ƙasa, tsohon maciji nan da ake kira Iblis, ko Shaiɗan, wanda ya ɓad da dukan duniya. Aka jefar da shi ƙasa, tare da mala’ikunsa a duniya.

10Sa’an nan na ji babbar murya daga sama tana cewa,

“Yanzu ceto da iko da mulkin Allahnmu,

da kuma ikon Kiristinsa.

Gama mai zargin ’yan’uwanmu,

wanda yake zarginsu a gaban Allahnmu dare da rana,

an jefar da shi ƙasa.

11Sun ci nasara a kansa

ta wurin jinin Ɗan Ragon

da ta wurin kalmar shaidarsu;

ba su ƙaunaci rayukansu sosai

har da za su ja da baya daga mutuwa.

12Saboda haka ku yi farin ciki, ku sammai,

da ku da kuke zaune a cikinsu!

Amma kaiton duniya da kuma teku,

gama Iblis ya sauko gare ku!

Ya cika da fushi,

domin ya san cewa lokacinsa ya rage kaɗan.”

13Sa’ad da macijin ya ga an jefar da shi a duniya, sai ya fafari macen nan da ta haifi ɗa namiji. 14Sai aka ba wa macen fikafikai biyu na babban gaggafa, don ta tashi sama zuwa inda aka shirya mata a hamada, inda za a lura da ita na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci, inda macijin ba zai iya kaiwa ba. 15Sa’an nan daga bakinsa macijin ya kwarara ruwa kamar kogi, don ruwan ya cimma matan yă kuma kwashe ta tare da ambaliya. 16Amma ƙasa ta taimaki macen ta wurin buɗe bakinta ta kuma shanye ruwan kogin da macijin ya kwarara daga bakinsa. 17Sai macijin ya yi fushi da macen ya kuma koma wajen sauran zuriyarta don yă yaƙe su waɗannan waɗanda suke biyayya da umarnan Allah suke kuma riƙe da shaidar Yesu.