Lukáš 5 – SNC & HCB

Slovo na cestu

Lukáš 5:1-39

Ježíšova rada přinese zázračný úlovek

1Jednoho dne stál Ježíš u Genezaretského jezera. Lidé se kolem něho tlačili a chtěli slyšet jeho kázání. 2Všiml si, že u břehu jsou dvě lodi. Opodál prali rybáři svoje sítě. 3Posadil se do jedné lodi, která patřila Šimonovi, a požádal ho, aby ho zavezl kousek od břehu. Odtud pak kázal zástupům. 4Když skončil, navrhl Šimonovi: „Zajeď s lodí na hloubku a roztáhněte sítě k lovu.“ 5Šimon namítal: „Pane, celou noc jsme se namáhali, ale marně. Když to však říkáš ty, zkusím to ještě jednou.“ 6Vypluli a zatáhli takové množství ryb, že se i sítě trhaly. 7Museli si zavolat na pomoc své přátele z druhé lodi. Obě lodi byly nakonec rybami tak naplněny, že se div nepotopily. 8Když to viděl Šimon, padl před Ježíšem na kolena a prosil: „Odejdi Pane, neobstojím v tvé blízkosti, jsem hříšný člověk.“ 9-10Všichni rybáři, kteří u toho byli – mezi nimi také Šimonovi přátelé, Jakub a Jan, synové Zebedeovi, žasli nad tím neobvyklým úlovkem. Ježíš řekl Šimonovi: „Neboj se! Učiním tě rybářem lidí. Budeš je získávat pro mne.“ 11Přirazili s loděmi ke břehu, všechno tam nechali a šli s Ježíšem.

12V jednom městečku potkal Ježíš člověka s pokročilým malomocenstvím. Ubožák před ním poklekl a prosil: „Pane, kdybys chtěl, mohl bys mne uzdravit.“ 13Ježíš se ho dotkl a řekl: „Ano, chci, buď zdráv!“ V tom okamžiku malomocenství zmizelo. 14Ježíš mu poručil: „Nikomu o tom nevyprávěj, jdi, ukaž se knězi, ať tě prohlásí za zdravého, a pak obětuj předepsanou oběť vděčnosti.“ 15Zpráva o Ježíšovi se rychle šířila. Lidé za ním přicházeli v houfech, aby ho slyšeli a aby uzdravoval jejich nemoci. 16On si však vždycky našel čas, aby se v ústraní modlil.

Ježíš uzdravuje ochrnutého

17Jednoho dne se kolem Ježíše shromáždili farizejové a učitelé zákona z různých měst Galileje a Judska a dokonce i z Jeruzaléma. Posadili se kolem něho a naslouchali mu. I zde mu dal Bůh moc k uzdravování. 18-19Nějací lidé přinesli na nosítkách ochrnutého muže. Chtěli ho vnést dveřmi a položit před Ježíše, ale bylo tam tolik lidí, že nemohli projít. Vystoupili tedy na střechu a otvorem spustili nemocného i s lehátkem přímo před něho. Když 20Ježíš viděl, kolik důvěry v něho mají, řekl: „Příteli, tvoje hříchy jsou ti odpuštěny.“ 21Učitelé zákona a farizejové uvažovali: „Jak se může opovážit něco takového říci? To je přece rouhání. Nikdo jiný než Bůh nemůže odpouštět hříchy!“ 22Ježíš dobře věděl, co si myslí, a proto řekl: „To vám vadí? 23Co je snazší? Zvěstovat člověku odpuštění jeho hříchů, anebo ho uzdravit? 24Přesvědčím vás, že Syn člověka má na zemi právo odpouštět hříchy.“ Obrátil se k ochrnutému se slovy: „Vstaň, vezmi si svoje lehátko a jdi domů!“ 25A tak se stalo: před očima všech muž vstal, sbalil svou rohož, šel domů a cestou hlasitě děkoval Bohu. 26Celé shromáždění bylo vzrušeno a lidé, plni svaté bázně, chválili Boha a říkali: „Dnes jsme viděli neuvěřitelné věci.“

Ježíš stoluje s hříšníky v Matoušově domě

27Ježíš šel dál. Cestou uviděl v celnici výběrčího daní jménem Levi a řekl mu: „Pojď, staň se mým následovníkem!“ 28Levi nechal všeho, vstal a šel za Ježíšem. 29Doma pak vystrojil pro Ježíše a jeho žáky hostinu. Na ni pozval i mnoho svých dřívějších kolegů. 30To pohoršilo farizeje a učitele zákona, takže vytýkali učedníkům: „Proč jíte a pijete s lidmi, kterými každý slušný člověk pohrdá?“ 31Ježíš na to odpověděl: „Lékaře nepotřebují zdraví, ale nemocní. 32Nepřišel jsem volat k pokání ty, kteří mají o sobě dobré mínění, ale hříšníky.“

Spor o půst

33Někteří farizejové Ježíšovi předhazovali: „Janovi učedníci se často s postem modlí a právě tak i naši žáci. Jak to tedy, že tvoji hodují?“ 34Ježíš odpověděl: „Je přirozené, aby se svatebčané postili, když je ženich s nimi? 35Však přijde chvíle, kdy ženicha odvedou, a pak bude vhodný čas k půstu.“ 36Ještě přidal další přirovnání: „Nikdo si přece nevystřihne kus látky z nových šatů, aby si jím vyspravil starý oděv. Zničil by si tak šaty nové a na starých šatech by se záplata srazila a díra by byla ještě větší. 37Nikdo také nebude nalévat víno do starých kožených měchů, protože kvasící víno by staré měchy roztrhalo, a tak by obojí přišlo nazmar. 38Proto mladé víno patří do nových měchů. 39Vás ovšem znepokojuje moje poselství. Jako mladé víno nesnesou staré měchy, ani ono se nevtěsná do vašich starých tradic a zvyklostí. Jste jako pijáci, kteří si libují ve starém uleželém vínu.“

Hausa Contemporary Bible

Luka 5:1-39

Kiran almajirai na farko

(Mattiyu 8.14-17; Markus 1.29-34)

1Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah, 2sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu. 3Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.

4Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”

5Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”

6Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa. 7Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.

8Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!” 9Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama. 10Yaƙub da Yohanna, ’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki.

Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.” 11Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.

Warkar da kuturu

(Mattiyu 8.1-4; Markus 1.40-45)

12Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”

13Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.

14Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”

15Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu. 16Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.

Yesu ya warkar da shanyayye

(Mattiyu 9.1-8; Markus 2.1-12)

17Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo. 18Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu. 19Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.

20Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”

21Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”

22Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku? 23Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’? 24Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.” 25Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah. 26Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”

Kiran Lawi

(Mattiyu 9.9-13; Markus 2.13-17)

27Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.” 28Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.

29Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su. 30Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”

31Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya. 32Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”

An tuhumi Yesu a kan azumi

(Mattiyu 9.14-17; Markus 2.18-22)

33Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”

34Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su? 35Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”

36Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba. 37Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace. 38A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna. 39Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’ ”