Lukáš 15 – SNC & HCB

Slovo na cestu

Lukáš 15:1-32

Ježíš vypráví podobenství o ztracené ovci

1Za Ježíšem přicházeli výběrčí daní a jiní lidé se stejně špatnou pověstí, aby si ho poslechli. 2Farizejové a učitelé zákona se nad tím pohoršovali a říkali: „S takovou sebrankou se přátelí a sedá s nimi za jedním stolem!“ 3Ježíš na to odpověděl podobenstvím: 4„Kdyby někdo z vás měl sto ovcí a jedna z nich by se mu zaběhla, nepokusil by se ji nalézt? Těch devadesát devět ponechá na pastvě a půjde za tou ztracenou tak dlouho, dokud ji nenalezne. 5Když ji najde, vezme ji na ramena 6a s radostí ji ponese domů. Svolá své přátele a sousedy a vybídne je: ‚Radujte se se mnou, našel jsem svou ztracenou ovečku.‘ 7Říkám vám, že v nebi je daleko větší radost nad jedním ztraceným člověkem, který lituje svých hříchů, než nad devadesáti devíti takovými, kteří si myslí, že pokání nepotřebují.

Ježíš vypráví podobenství o ztracené minci

8Nebo si představte ženu, která má deset stříbrných mincí a jedna se jí doma někam zakutálí. Nerozsvítí světlo, nevymete kouty a nebude hledat tak dlouho, až peníz najde? 9Určitě pak svolá přítelkyně a sousedky a řekne jim: ‚Radujte se se mnou, našla jsem svůj ztracený peníz.‘ 10Říkám vám: Zrovna takovou radost mají v nebi andělé nad jedním ztraceným člověkem, který lituje svých hříchů.“

Ježíš vypráví podobenství o ztraceném synu

11Ježíš dále vyprávěl: „Jeden muž měl dva syny. 12Mladší přišel za otcem a řekl: ‚Otče, dej mi už teď podíl z dědictví, které nám chceš jednou odkázat.‘ A tak otec rozdělil svůj majetek mezi oba syny. 13Po několika dnech zpeněžil ten mladší svůj podíl a odešel daleko od domova. Tam prohýřil všechno, co měl. 14A nejenže všechno utratil; v té krajině vypukl hlad, a tak neměl co do úst. 15Konečně si našel práci u jednoho sedláka. Ten ho poslal na pole pást vepře. 16Byl by se rád dosyta najedl alespoň sladkých lusků, kterými krmili vepře, ale nikdo mu nic nedal. 17A tak šel do sebe a uvažoval: ‚Dělníci mého otce mají jídla více, než mohou spotřebovat, a já tu umírám hlady. 18Půjdu za ním a řeknu mu: Otče, zhřešil jsem proti Bohu i proti tobě 19a dobře vím, že si nezasloužím, abys mne ještě nazýval svým synem. Najmi mne, prosím, jako dělníka.‘ 20A tak se vydal na cestu k domovu. Otec ho už z dálky uviděl a plný soucitné lásky mu vyběhl naproti, objal ho a políbil. 21‚Otče,‘ řekl syn, ‚zhřešil jsem proti Bohu a proti tobě, nejsem hoden, abych byl ještě tvým synem.‘ 22Ale otec nařídil služebníkům: ‚Rychle přineste nejlepší šaty, navlékněte mu synovský prsten a obujte ho! 23Poražte vykrmené tele a připravte hostinu. Oslavíme společně návrat mého syna. 24Vždyť je to, jako by umřel, a zase oživl. Byl ztracen, a je nalezen.‘ A tak oslavovali jeho návrat. 25Starší syn se vracel z pole a uslyšel hluk hostiny. 26Zavolal si jednoho sluhu a zeptal se, co se děje. 27Sluha řekl: ‚Tvůj bratr přišel domů a otec dal porazit pěkné tele z radosti, že se mu syn vrátil zdráv.‘ 28Starší bratr se rozhněval a vůbec nechtěl jít dovnitř. Otec vyšel ven a domlouval mu. 29Ale syn mu vyčítal: ‚Tolik let jsem pro tebe dřel, ve všem tě poslechl a co z toho mám? Nikdy jsi mi nedal ani kůzle, abych se poveselil se svými přáteli. 30A teď, když se vrátil tenhle tvůj synáček, který všechno prohýřil s děvkami, ještě mu vystrojíš hostinu.‘ 31‚Hochu,‘ řekl otec, ‚my jsme tu přece vždycky byli spolu a ty víš, že všechno, co mám, je tvoje. 32Ale teď nemůžeme dělat nic jiného než se radovat. Vždyť tvůj bratr, kterého jsme považovali za mrtvého, žije, ztratil se a je nalezen.‘ “

Hausa Contemporary Bible

Luka 15:1-32

Misalin ɓatacciyar tunkiya

(Mattiyu 18.12-14)

1Yanzu fa, masu karɓar haraji da “masu zunubi” duka suna taruwa don jin koyarwar Yesu. 2Amma Farisiyawa da malaman dokoki suka yi gunaguni, suna cewa, “Wannan mutum yana karɓan ‘masu zunubi,’ kuma yana ci tare da su.”

3Sai Yesu ya faɗa musu wannan misali ya ce, 4“In ɗayanku yana da tumaki ɗari, sa’an nan ɗayansu ta ɓace. Ashe, ba zai bar tasa’in da tara a fili ya je neman wadda ta ɓace, har sai ya same ta ba? 5In ya same ta, zai sa ta a kafaɗa da murna, 6ya dawo gida. Sa’an nan zai kira abokansa da maƙwabtansa wuri ɗaya ya ce, ‘Ku taya ni murna, na sami tunkiyana da ta ɓata.’ 7Ina gaya muku, haka za a yi murna sosai a sama, a kan mai zunubi guda ɗaya da ya tuba, fiye da masu adalci tasa’in da tara, waɗanda ba su bukatan tuba.

Misalin kuɗi da ya ɓace

8“Ko kuwa in wata mace tana da kuɗi na azurfa guda goma, sa’an nan ɗaya ya ɓata, ashe, ba za tă ƙuna fitila, ta share gidan, ta nema a hankali, har sai ta samu ba? 9In ta same shi, sai ta kira ƙawayenta da maƙwabtanta wuri ɗaya, ta ce musu, ‘Ku taya ni murna, na sami kuɗina da ya ɓata.’ 10Haka, ina gaya muku, akwai murna a gaban mala’ikun Allah a kan mai zunubi guda ɗaya, da ya tuba.”

Misalin ɗa da ya ɓace

11Yesu ya ci gaba da cewa, “Akwai wani mutum wanda yake da ’ya’ya biyu maza. 12Ƙaramin ya ce wa mahaifinsu, ‘Baba, ba ni rabon gādona.’ Sai mahaifin ya raba musu dukiyarsa.

13“Bayan ’yan kwanaki, sai ƙaramin ɗan ya tattara kayansa duk, ya tashi ya tafi wata ƙasa mai nisa. A can, ya ɓatar da dukiyarsa duka a rayuwar banza. 14Bayan ya ɓatar da kome, sai ga muguwar yunwa a dukan ƙasar, har ya shiga rashi. 15Sai ya je ya sami aiki a wurin wani mutumin ƙasar, wanda ya aike shi a gonakinsa, ya yi kiwon aladu. 16Ya yi marmarin cin dusan da aladun suke ci, amma ba wanda ya ba shi wani abu.

17“Da hankalinsa ya dawo, sai ya ce, ‘Kai, bayin mahaifina guda nawa ne, da suke da abinci fiye da isashe, ni kuma ina nan, zan mutu don yunwa! 18Zan tashi in koma wurin mahaifina, in ce masa, “Baba, na yi wa sama, na kuma yi maka zunubi. 19Ni ban isa a ƙara kira na ɗanka ba. Ka mai da ni kamar ɗaya daga cikin bayinka.” ’ 20Sai ya tashi ya kama hanya ya koma wurin mahaifinsa.

“Amma tun yana nesa, mahaifinsa ya hange shi. Tausayi kuma ya kama shi, sai ya tashi ya ruga da gudu wurinsa, ya rungume shi, ya yi masa sumba.

21“Sai ɗan ya ce masa, ‘Baba, na yi wa sama, na kuma yi maka zunubi. Ni ban isa a ƙara kira na ɗanka ba.’

22“Amma mahaifin ya ce wa bayinsa, ‘Maza! Ku kawo riga mafi kyau ku sa masa. Ku sa zobe a yatsarsa, da takalma kuma a ƙafafunsa. 23Ku kawo ɗan saniya mai ƙiba ku yanka. Bari mu yi biki mu yi shagali. 24Gama ɗan nan nawa, da ya mutu, amma yanzu yana da rai kuma. Da ya ɓata, amma yanzu an same shi.’ Sai suka fara shagali.

25“Yayinda ake haka, babban ɗan yana gona. Da ya zo kusa da gida, sai ya ji ana kiɗi ana rawa. 26Sai ya kira ɗaya daga cikin bayin, ya tambaye shi abin da yake faruwa. 27Bawan ya ce, ‘Ai, ɗan’uwanka ne ya dawo, shi ne mahaifinka ya yanka ɗan saniya mai ƙiba, gama ya yi murna ya karɓi ɗansa da ya dawo gida lafiyayye, ba abin da ya same shi.’

28“Sai yayan ya yi fushi, ya ƙi shiga gida. Sai mahaifinsa ya fita ya roƙe shi. 29Amma ya amsa wa mahaifinsa ya ce, ‘Duba! Duk waɗannan shekaru, ina yin maka aiki kamar bawa, ban taɓa maka rashin biyayya ba. Duk da haka, ba ka taɓa ba ni ko ɗan akuya domin in yi shagali da abokaina ba. 30Amma da wannan ɗan naka, wanda ya ɓatar da dukiyarka a kan karuwai ya dawo, ka yanka masa ɗan saniya mai ƙiba!’

31“Sai mahaifin ya ce masa, ‘Ɗana, kullum kana nan tare da ni, kuma duk abin da nake da shi, naka ne. 32Amma ya zama mana dole, mu yi shagali, mu yi murna, domin ɗan’uwan nan naka, da ya mutu, yanzu kuwa yana da rai, da ya ɓata, amma yanzu an same shi.’ ”