Jan 20 – SNC & HCB

Slovo na cestu

Jan 20:1-31

Ježíš vstává z mrtvých

1První den po sobotě, ještě před rozedněním, přišla k Ježíšovu hrobu Marie Magdaléna. Uviděla, že kamenný uzávěr hrobky je odsunut. 2Běžela k Petrovi a k učedníkovi, kterého měl Ježíš tolik rád, a oznámila jim: „Našeho Pána vzali z hro-bu a nevíme, kam ho položili.“

3-4Ti dva se zvedli a spěchali ke hrobu. Druhý učedník Petra předběhl a byl tam první. 5Do hrobu však jenom nahlédl a uviděl prázdné plátno. 6Ale tu přiběhl Petr, který vešel dovnitř a kromě plátna nalezl 7i šátek, jímž byla ovázána Ježíšova hlava; ten byl svinutý a položený zvlášť. 8-9Za Petrem vstoupil do hrobu i druhý učedník, všechno si prohlédl a uvěřil, že Ježíš vstal z mrtvých. Až dosud to totiž stejně jako ostatní nechápal.

Ježíš se zjevuje Marii z Magdaly

10Oba učedníci se vrátili zpět, 11ale Marie zůstala u hrobu a plakala. 12Náhle spatřila v hrobce dva anděly v bílém; seděli na obou koncích kamenné lavice, na níž předtím spočívalo Ježíšovo tělo.

13„Ženo, proč pláčeš?“ zeptali se jí.

„Vzali mého Pána a nevím, kam ho uložili.“

14Když to řekla, obrátila se a spatřila, že za ní někdo stojí. 15Neznámý ji oslovil: „Ženo, proč pláčeš? Koho hledáš?“

Myslela, že je to zahradník, a odpověděla: „Pane, jestli jsi ho odnesl, řekni mi, kam jsi ho uložil, a já ho pochovám.“

16Ježíš jí řekl: „Marie!“

Pohlédla na něj a řekla: „Můj Mistře!“ a poklekla před ním.

17„Nedotýkej se mne!“ varoval ji Ježíš, „ještě jsem se nevrátil k svému Otci. Běž a pověz bratřím, že odcházím k svému i vašemu Bohu a Otci.“ 18Marie Magdaléna vyhledala učedníky a řekla jim: „Viděla jsem Pána,“ a sdělila jim, co jí uložil.

Ježíš se zjevuje učedníkům za zavřenými dveřmi

19Téhož dne večer byli učedníci pohromadě za zamčenými dveřmi, protože se báli, že teď přijdou Židé na ně. Pojednou stál Ježíš mezi nimi a řekl: „Pokoj vám!“ 20Potom jim ukázal rány v rukou a v boku.

To byla radost pro učedníky, že zase vidí svého Pána! 21Ježíš opakoval: „Pokoj vám!“ a pokračoval: „Otec vyslal mne a já vysílám vás.“ 22Dýchl na ně a řekl: „Přijměte svatého Ducha! 23Komu budete zvěstovat odpuštění hříchů a kdo je přijme, tomu bude odpuštěno. Komu tu zvěst zadržíte, zůstává ve svém hříchu.“

Ježíš se zjevuje učedníkům včetně Tomáše

24Toho večera chyběl mezi učedníky Tomáš, kterému přezdívali Dvojče. 25Ostatní mu o setkání s Ježíšem vyprávěli, ale on pochyboval: „Neuvěřím, dokud neuvidím a neohmatám rány na jeho rukou a boku.“

26Po týdnu byli učedníci znovu spolu a tentokrát byl s nimi i Tomáš. Dveře byly zase zamčeny, když se Ježíš mezi ně postavil a oslovil je: „Pokoj vám!“ 27Potom se obrátil k Tomášovi: „Podívej se a sáhni si na mé rány! Už nepochybuj, ale věř!“

28Tomáš přesvědčen vyznal: „Jsi můj Pán a můj Bůh!“

29Ježíš mu na to řekl: „Viděl jsi mne, a proto věříš. Cennější však je nevidět a uvěřit.“

30-31Za dobu svého působení Ježíš před zraky učedníků vykonal mnoho dalších mocných činů, které nejsou v této knize zaznamenány. Ty činy, které jsou zaznamenány, ve vás mají vzbudit víru v Ježíše jako Božího Syna a zajistit vám tak věčný život.

Hausa Contemporary Bible

Yohanna 20:1-31

Kabarin da ba kowa

(Mattiyu 28.1-10; Markus 16.1-8; Luka 24.1-12)

1Da sassafe a ranar farko ta mako, tun da sauran duhu, Maryamu Magdalin ta tafi kabarin ta kuwa tarar an kawar da dutsen daga bakin kabarin. 2Sai ta zo da gudu wajen Siman Bitrus da ɗayan almajirin, wanda Yesu yake ƙauna, ta ce, “Sun ɗauke Ubangiji daga kabarin, ba mu kuma san inda suka sa shi ba!”

3Sai Bitrus da almajirin nan suka nufi kabarin. 4Dukansu biyu suna gudu, amma ɗayan almajirin ya tsere wa Bitrus ya kuma fara kai kabarin. 5Ya sunkuya ya duba ciki ya ga ƙyallayen lilin ne kwance a can amma bai shiga ba. 6Sa’an nan Siman Bitrus, wanda yake bayansa, ya iso ya kuwa wuce cikin kabarin. Ya ga ƙyallayen lilin kwance a can, 7haka ma zanen binnewar da aka naɗe kan Yesu da shi. Zanen a naɗe yake shi kaɗai, a keɓe da lilin ɗin. 8A ƙarshe sai almajirin nan, wanda ya kai kabarin da farko, shi ma ya shiga. Ya gani ya kuma gaskata. 9(Har yanzu ba su fahimci Nassin nan da ya ce lalle ne Yesu yă tashi daga matattu ba.) 10Sai almajiran suka koma zuwa inda suke zama.

Yesu ya bayyana ga Maryamu Magdalin

(Mattiyu 28.1-10; Markus 16.1-8; Luka 24.1-12)

11Maryamu kuwa ta tsaya a bakin kabarin daga waje tana kuka. Da tana cikin kuka, sai ta sunkuya ta leƙa cikin kabarin, 12sai ta ga waɗansu mala’iku biyu saye da fararen tufafi, zaune a inda dā gawar Yesu take, ɗaya wajen kai ɗayan kuma wajen ƙafafu.

13Suka tambaye ta cewa, “Mace, don me kike kuka?”

Ta ce, “Sun ɗauke Ubangijina, ban kuma san inda suka ajiye shi ba.” 14Da ta faɗin haka, sai ta juya ta ga Yesu tsaye, sai dai ba tă gane cewa Yesu ne ba.

15Sai ya ce, “Mace, don me kike kuka? Wa kike nema?”

Ta yi tsammani shi ne mai aikin lambun, sai ta ce, “Ranka yă daɗe, in kai ne ka ɗauke shi, gaya mini inda ka ajiye shi, in je in ɗauke shi.”

16Yesu ya ce mata, “Maryamu.”

Sai ta juya wajensa ta ɗaga murya ta ce da Arameyanci, “Rabboni!” (Wanda yake nufin “Malam”).

17Yesu ya ce, “Kada ki riƙe ni, gama ban riga na koma wajen Uba tukuna ba. A maimako, ki tafi wajen ’yan’uwana ki gaya musu, ‘Ina komawa wajen Ubana da Ubanku, wajen Allahna da kuma Allahnku.’ ”

18Sai Maryamu Magdalin ta wajen almajiran da labari cewa, “Na ga Ubangiji!” Ta kuma gaya musu cewa ya faɗa mata waɗannan abubuwa.

Yesu ya bayyana ga almajiransa

(Mattiyu 28.16-20; Markus 16.14-18; Luka 24.36-49)

19Da Yamman ranar farko ta mako, sa’ad da almajiran suna tare, ƙofofi kuma suna a kulle saboda tsoron Yahudawa, sai ga Yesu ya zo ya tsaya a tsakiyarsu ya ce, “Salama tă kasance tare da ku!” 20Bayan ya faɗa haka, sai ya nuna musu hannuwansa da gefensa. Sai almajiran suka yi farin ciki ƙwarai da suka ga Ubangiji.

21Sai Yesu ya sāke ce musu, “Salama tă kasance tare da ku! Kamar yadda Uba ya aiko ni, haka ni ma ina aikan ku.” 22Da wannan sai ya hura musu numfashinsa ya ce, “Ku karɓi Ruhu Mai Tsarki. 23Duk wanda kuka gafarta wa zunubansa, an gafarta masa ke nan. Duk wanda ba ku gafarta wa ba kuwa, ba a gafarta masa ba ke nan.”

Yesu ya bayyana ga Toma

24Toma kuwa (wanda ake kira Didaimus), ɗaya daga cikin Sha Biyun, ba ya tare da almajiran sa’ad da Yesu ya zo. 25Saboda haka sauran almajiran suka ce masa, “Ai, mun ga Ubangiji!”

Amma ya ce musu, “Ina, ai, sai na ga ramin ƙusa a hannuwansa na sa yatsata a inda ƙusoshi suka kasance, na kuma sa hannuna a gefensa, in ba haka ba, ba zan gaskata ba.”

26Bayan mako guda, har wa yau almajiransa suna cikin gidan, Toma kuwa yana tare da su. Ko da yake ƙofofi suna kulle, sai ga Yesu ya zo ya tsaya a tsakiyarsu ya ce, “Salama tă kasance tare da ku!” 27Sa’an nan ya ce wa Toma, “Sa yatsarka nan; dubi hannuwana. Miƙa hannunka ka sa a gefena. Ka daina shakka ka gaskata.”

28Toma ya ce masa, “Ya Ubangijina da Allahna!”

29Sai Yesu ya ce masa, “Wato ka gaskata saboda ka gan ni ne, masu albarka ne waɗanda ba su gan ni ba, amma suka gaskata.”

30Yesu ya yi waɗansu abubuwan banmamaki da yawa a gaban almajiransa da ba a rubuta a wannan littafi ba. 31An dai rubuta waɗannan ne don ku gaskata Yesu ne Kiristi, Ɗan Allah kuma ta wurin gaskatawa ku sami rai a cikin sunansa.