يوحنا 1 – PCB & HCB

Persian Contemporary Bible

يوحنا 1:1‏-51

مسيح به دنيای ما آمد

1‏-2در ازل، پيش از آنكه چيزی پديد آيد، «كلمه» وجود داشت و نزد خدا بود. او همواره زنده بوده، و خود او خداست. 3هر چه هست، بوسيلهٔ او آفريده شده و چيزی نيست كه آن را نيافريده باشد. 4زندگی جاويد در اوست و اين زندگی به تمام مردم نور می‌بخشد. 5او همان نوری است كه در تاريكی می‌درخشد و تاريكی هرگز نمی‌تواند آن را خاموش كند.

6‏-7خدا يحيای پيامبر را فرستاد تا اين «نور» را به مردم معرفی كند و مردم به او ايمان آورند. 8يحيی آن نور نبود، او فقط شاهدی بود تا نور را به مردم معرفی كند. 9اما بعد، آن نور واقعی آمد تا به هر کس كه به اين دنيا می‌آيد، بتابد.

10گرچه جهان را او آفريده بود، اما زمانی كه به اين جهان آمد، كسی او را نشناخت. 11‏-12حتی در سرزمين خود و در ميان قوم خود، يهوديان، كسی او را نپذيرفت. اما او به تمام كسانی كه به او ايمان آوردند، اين حق را داد كه فرزندان خدا گردند؛ بلی، فقط كافی بود به او ايمان آورند تا نجات يابند. 13اين اشخاص تولدی نو يافتند، نه همچون تولدهای معمولی كه نتيجهٔ اميال و خواسته‌های آدمی است، بلكه اين تولد را خدا به ايشان عطا فرمود.

14«كلمهٔ خدا» انسان شد و بر روی اين زمين و در بين ما زندگی كرد. او لبريز از محبت و بخشش و راستی بود. ما بزرگی و شكوه او را به چشم خود ديديم، بزرگی و شكوه فرزند بی‌نظير پدر آسمانی ما، خدا.

15يحيی او را به مردم معرفی كرد و گفت: «اين همان كسی است كه به شما گفتم بعد از من می‌آيد و مقامش از من بالاتر است، زيرا پيش از آنكه من باشم، او وجود داشت.»

16لطف بی‌پايان او به همهٔ ما رسيد و بركت در پی بركت نصيب ما شد. 17خدا احكام خود را توسط موسی به مردم داد، اما راستی و محبت را به‌وسیلهٔ عيسی مسيح عطا فرمود. 18كسی هرگز خدا را نديده است؛ اما عيسی، فرزند يگانهٔ خدا، او را ديده است زيرا همواره همراه پدر خود، خدا می‌باشد. او هر آنچه را كه ما بايد دربارهٔ خدا بدانيم، به ما گفته است.

شهادت يحيی

19روزی سران قوم يهود از شهر اورشليم، چند تن از كاهنان و دستيارانش را نزد يحيی فرستادند تا بدانند آيا او ادعا می‌كند كه مسيح است يا نه.

20يحيی، صريحاً اظهار داشت: «نه، من مسيح نيستم.»

21پرسيدند: «خوب، پس كه هستيد؟ آيا الياس پيامبر هستيد؟»

جواب داد: «نه!»

پرسيدند: «آيا شما آن پيامبر نيستيد كه ما چشم به راهش می‌باشيم؟»

باز هم جواب داد: «نه.»

22گفتند: «پس به ما بگوييد كه هستيد تا بتوانيم برای سران قوم كه ما را به اينجا فرستاده‌اند، جوابی ببريم.»

23يحيی گفت: «چنانكه اشعيای نبی پيشگويی كرده، من صدای ندا كننده‌ای هستم كه در بيابان فرياد می‌زند: ای مردم، خود را برای آمدن خداوند آماده سازيد.»

24سپس، افرادی كه از طرف فرقهٔ فريسی‌ها آمده بودند، 25از او پرسيدند: «خوب، اگر شما نه مسيح هستيد، نه الياس و نه آن پيامبر، پس چه حق داريد مردم را غسل تعميد دهيد؟»

26يحيی گفت: «من مردم را فقط با آب غسل می‌دهم؛ ولی همين جا در ميان اين جمعيت، كسی هست كه شما او را نمی‌شناسيد. 27او بزودی خدمت خود را در بين شما آغاز می‌كند. مقام او به قدری بزرگ است كه من حتی شايسته نيستم كفشهای او را پيش پايش بگذارم.»

28اين گفتگو در «بيت‌عنيا» روی داد. بيت‌عنيا دهی است در آن طرف رود اردن و جايی است كه يحيی، مردم را غسل تعميد می‌داد.

عيسی، برّه خدا

29روز بعد، يحيی، عيسی را ديد كه به سوی او می‌آيد. پس به مردم گفت: «نگاه كنيد! اين همان برّه‌ای است كه خدا فرستاده تا برای آمرزش گناهان تمام مردم دنيا قربانی شود. 30اين همان كسی است كه گفتم بعد از من می‌آيد ولی مقامش از من بالاتر است، چون قبل از من وجود داشته است. 31من نيز او را نمی‌شناختم. ولی برای اين آمدم كه مردم را با آب غسل دهم تا به اين وسيله او را به قوم اسرائيل معرفی كنم.»

32سپس گفت: «من روح خدا را ديدم كه به شكل كبوتری از آسمان آمد و بر عيسی قرار گرفت. 33همانطور كه گفتم، من نيز او را نمی‌شناختم ولی وقتی خدا مرا فرستاد تا مردم را غسل تعميد دهم، در همان وقت به من فرمود: هرگاه ديدی روح خدا از آسمان آمد و بر كسی قرار گرفت، بدان كه او همان است كه منتظرش هستيد. اوست كه مردم را با روح‌القدس تعميد خواهد داد. 34و چون من با چشم خود اين را ديده‌ام، شهادت می‌دهم كه او فرزند خداست.»

نخستين شاگردان عيسی

35فردای آن روز، وقتی يحيی با دو نفر از شاگردان خود ايستاده بود، 36عيسی را ديد كه از آنجا می‌گذرد، يحيی با اشتياق به او نگاه كرد و گفت: «ببينيد! اين همان بره‌ای است كه خدا فرستاده است.» 37آنگاه دو شاگرد يحيی برگشتند و در پی عيسی رفتند.

38عيسی كه ديد دو نفر دنبال او می‌آيند، برگشت و از ايشان پرسيد: «چه می‌خواهيد؟»

جواب دادند: «آقا، كجا اقامت داريد؟»

39فرمود: «بياييد و ببينيد.»

پس همراه عيسی رفتند و از ساعت چهار بعد از ظهر تا غروب نزد او ماندند. 40(يكی از آن دو، «اندرياس» برادر «شمعون پطرس» بود.)

41اندرياس رفت و برادر خود را يافته، به او گفت: «شمعون، ما مسيح را پيدا كرده‌ايم!» 42و او را آورد تا عيسی را ببيند.

عيسی چند لحظه به او نگاه كرد و فرمود: «تو شمعون، پسر يونا هستی. ولی از اين پس پطرس (يعنی ”صخره“) ناميده خواهی شد!»

43روز بعد، عيسی تصميم گرفت به ايالت جليل برود. در راه، «فيليپ» را ديد و به او گفت: «همراه من بيا.» 44(فيليپ نيز اهل بيت‌صيدا و همشهری اندرياس و پطرس بود.)

45فيليپ رفت و «نتنائيل» را پيدا كرد و به او گفت: «نتنائيل، ما مسيح را يافته‌ايم، همان كسی كه موسی و پيامبران خدا درباره‌اش خبر داده‌اند. نامش عيسی است، پسر يوسف و اهل ناصره.»

46نتنائيل با تعجب پرسيد: «گفتی اهل ناصره؟ مگر ممكن است از ناصره هم چيز خوبی بيرون آيد؟»

فيليپ گفت: «خودت بيا و او را ببين.»

47وقتی نزديک می‌شدند، عيسی فرمود: «ببينيد، اين شخص كه می‌آيد، يک مرد شريف و يک اسرائيلی واقعی است.»

48نتنائيل پرسيد: «از كجا می‌دانی من كه هستم؟»

عيسی فرمود: «قبل از آنكه فيليپ تو را پيدا كند، من زير درخت انجير تو را ديدم.»

49نتنائيل حيرت‌زده گفت: «آقا، شما فرزند خدا هستيد؛ شما پادشاه اسرائيل می‌باشيد!»

50عيسی گفت: «چون فقط گفتم تو را زير درخت انجير ديدم، به من ايمان آوردی؟ بعد از اين چيزهای بزرگتر خواهی ديد. 51در حقيقت همهٔ شما آسمان را خواهيد ديد كه باز شده و فرشتگان خدا نزد من می‌آيند و به آسمان باز می‌گردند.»

Hausa Contemporary Bible

Yohanna 1:1-51

Kalman ya zama mutum

1Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne. 2Yana nan tare da Allah tun farar farawa. 3Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi. 4A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane. 5Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.

6Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna. 7Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya. 8Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.

9Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.1.9 Ko kuwa Wannan ne haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutumin da yake shigowa duniya 10Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba. 11Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba. 12Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama ’ya’yan Allah 13’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar ’yan adam,1.13 Girik na jini ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.

14Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.

15(Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’ ”) 16Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka. 17Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi. 18Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.

Yohanna Mai Baftisma ya ce ba shi ne Kiristi ba

19To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne. 20Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”

21Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?”

Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.”

“Kai ne Annabin nan?”

Ya amsa ya ce, “A’a.”

22A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”

23Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’ ”1.23 Ish 40.3

24To, waɗansu Farisiyawan da aka aika 25suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”

26Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba. 27Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”

28Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.

Yesu Ɗan Rago na Allah

29Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya! 30Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’ 31Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”

32Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa. 33Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’ 34Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”

Almajiran Yesu na farko

35Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa. 36Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”

37Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu. 38Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?”

Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”

39Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.”

Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.

40Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu. 41Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi). 42Ya kuma kawo shi wurin Yesu.

Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan1.42 Da Kefas (Arameyik) da kuma Bitrus (Girik) na nufin dutse.).

Yesu ya kira Filibus da Natanayel

43Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”

44Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne. 45Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”

46Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?”

Filibus ya ce, “Zo ka gani.”

47Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”

48Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?”

Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”

49Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”

50Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.” 51Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”