Откривење 3 – NSP & HCB

New Serbian Translation

Откривење 3:1-22

Цркви у Сарду

1Анђелу цркве у Сарду напиши:

’Ово говори онај који има седам Божијих духова и седам звезда.

Знам твоја дела. Називају те живим, а у ствари си мртав! 2Пробуди се и учврсти остале који су на умору. Нисам, наиме, нашао да су твоја дела савршена пред мојим Богом. 3Сети се онога што си примио и чуо. Држи се тога и покај се. А ако не будеш будан, доћи ћу као лопов, па нећеш знати у који ћу час доћи к теби.

4Ипак, имаш неколико њих у Сарду који нису окаљали своју одећу; они ће ходити са мном обучени у бело, јер су достојни. 5Победника ћу обући у белу одежду и нећу избрисати његово име из Књиге живота, него ћу изјавити да ми припада пред мојим Оцем и пред његовим анђелима.

6Ко има уши, нека слуша шта Дух говори црквама!’

Цркви у Филаделфији

7Анђелу цркве у Филаделфији напиши:

’Ово говори Свети, Истинити, који има кључ Давидов. Што он отвори, нико не може да затвори, и што затвори, нико не може да отвори.

8Знам твоја дела. Ево, отворио сам врата пред тобом која нико не може да затвори. Јер, премда имаш мало силе, ипак си одржао моје учење и ниси се одрекао мога имена. 9Ево, довешћу неке из Сатанине синагоге који за себе говоре да су Јевреји, а у ствари лажу, јер то нису. Ја ћу учинити да дођу к теби и да се поклоне пред твојим ногама, па ће разумети да те волим. 10А пошто си постојано одржао што сам ти заповедио, сачуваћу те од часа искушења који ће доћи на сав свет, да искуша становнике земље.

11Ево, долазим ускоро. Држи чврсто оно што имаш, да нико не узме твој венац! 12Победника ћу учинити стубом у храму свога Бога, те никада неће изаћи из њега. Написаћу на њему име свога Бога и име града Бога свога, новог Јерусалима, који силази са неба од мог Бога, и моје ново име.

13Ко има уши, нека слуша шта Дух говори црквама!’

Цркви у Лаодикији

14Анђелу цркве у Лаодикији напиши:

’Ово говори Амин, Верни и Истинити сведок, узрок свему што је Бог створио.

15Знам твоја дела. Ти ниси ни хладан ни врућ. Да си бар хладан или врућ! 16Али пошто си млак, ни врућ ни хладан, избљуваћу те из својих уста. 17Ти, наиме, говориш: „Богат сам и пребогат; ништа ми не треба!“, а не знаш да си јадан и бедан, сиромашан, слеп и го. 18Зато ти саветујем да купиш од мене злата жеженог да се обогатиш, и белу одећу да се обучеш, да се не покаже твоја голотиња, па да се осрамотиш, и лековиту маст да намажеш очи, те да прогледаш.

19Ја корим и кажњавам оне које волим. Стога, буди ревностан и покај се. 20Ево, стојим пред вратима и куцам; ко чује мој глас и отвори врата, ући ћу к њему и вечерати с њим, и он са мном.

21Победнику ћу дати да седне са мном на мој престо, као што сам и ја победио и сео са својим Оцем на његов престо.

22Ко има уши, нека слуша шта Дух говори црквама!’“

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 3:1-22

Zuwa ga ikkilisiya a Sardis

1“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Sardis, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomi, na wanda yake riƙe da ruhohi bakwai na Allah da kuma taurari bakwai.

Na san ayyukanka; ana ganinka kamar rayayye, amma kai matacce ne. 2Ka farka! Ka ƙarfafa abin da ya rage wanda kuma yake bakin mutuwa, don ban ga ayyukanka cikakke ne ba a gaban Allahna. 3Saboda haka, ka tuna fa, abin da ka karɓa ka kuma ji; ka yi biyayya da shi, ka kuma tuba. Amma in ba ka farka ba, zan zo kamar ɓarawo, ba kuwa za ka san lokacin da zan zo maka ba.

4Duk da haka kana da mutane kima cikin Sardis waɗanda ba su ɓata tufafinsu ba. Za su yi tafiya tare da ni, saye da fararen tufafi, don sun cancanta. 5Wanda ya ci nasara, kamar su, za a sanya masa fararen tufafi. Ba zan taɓa share sunansa daga cikin littafin rai ba, sai dai zan shaida sunansa a gaban Ubana da mala’ikunsa. 6Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.

Zuwa ga ikkilisiya a Filadelfiya

7“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Filadelfiya, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomi, na wanda yake mai tsarki da kuma gaskiya, wanda yake riƙe da mabuɗin Dawuda. Abin da ya buɗe ba mai rufewa, abin da kuma ya rufe ba mai buɗewa.

8Na san ayyukanka. Duba, na sa a gabanka buɗaɗɗen ƙofa wadda ba mai iya rufewa. Na san cewa kana da ɗan ƙarfi, duk da haka ka kiyaye maganata ba ka kuwa yi mūsun sunana ba. 9Zan sa waɗanda suke na majami’ar Shaiɗan, waɗanda suke cewa su Yahudawa ne alhali kuwa ba haka ba ne, sai dai maƙaryata, zan sa su zo su fāɗi a ƙasa a gabanka su kuma shaida cewa na ƙaunace ka. 10Da yake ka kiyaye umarnina ta wurin jimrewa, ni ma zan tsare ka daga lokacin nan na gwaji wanda zai zo bisan dukan duniya don a gwada waɗanda suke zama a duniya.

11Ina zuwa ba da daɗewa ba. Ka riƙe abin da kake da shi, don kada wani ya karɓe rawaninka. 12Duk wanda ya ci nasara zan mai da shi ginshiƙi a haikalin Allahna. Ba kuwa zai sāke barin wurin ba. Zan rubuta a kansa sunan Allahna da kuma sunan birnin Allahna, sabuwar Urushalima, wadda take saukowa daga sama daga Allahna; ni kuma zan rubuta a kansa sabon sunana. 13Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.

Zuwa ga ikkilisiya a Lawodiseya

14“Zuwa ga mala’ikan ikkilisiya a Lawodiseya, ka rubuta,

Waɗannan su ne kalmomina Amin, amintaccen mashaidi mai gaskiya, da kuma mai mulkin halittar Allah.

15Na san ayyukanka, ba ka da sanyi ba ka kuma da zafi. Na so da kai ɗaya ne daga ciki, ko sanyi, ko zafi! 16Amma domin kana tsaka-tsaka ba zafi ba, ba kuma sanyi ba, ina dab da tofar da kai daga bakina. 17Ka ce, ‘Ina da arziki; na sami dukiya ba na kuma bukatar kome.’ Amma ba ka gane ba cewa kai matsiyaci ne, abin tausayi, matalauci, makaho kana kuma tsirara. 18Na shawarce ka ka sayi zinariyar da aka tace cikin wuta daga gare ni, don ka yi arziki; da fararen tufafi ka sa, don ka rufe kunyar tsirancinka; da kuma maganin ido ka sa a idanunka, don ka gani.

19Waɗanda nake ƙauna su nake tsawata wa, nake kuma horo. Saboda haka ka yi himma ka tuba. 20Ga ni! Ina tsaye a bakin ƙofa, ina ƙwanƙwasawa. Duk wanda ya ji muryata ya kuma buɗe ƙofar, zan shiga in kuma ci tare da shi, shi kuma tare da ni.

21Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ikon zama tare da ni a kursiyina, kamar yadda na ci nasara, kuma ina zaune tare da Ubana a kursiyinsa. 22Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikkilisiyoyi.”