Colossians 3 – NIVUK & HCB

New International Version – UK

Colossians 3:1-25

Living as those made alive in Christ

1Since, then, you have been raised with Christ, set your hearts on things above, where Christ is, seated at the right hand of God. 2Set your minds on things above, not on earthly things. 3For you died, and your life is now hidden with Christ in God. 4When Christ, who is your3:4 Some manuscripts our life, appears, then you also will appear with him in glory.

5Put to death, therefore, whatever belongs to your earthly nature: sexual immorality, impurity, lust, evil desires and greed, which is idolatry. 6Because of these, the wrath of God is coming.3:6 Some early manuscripts coming on those who are disobedient 7You used to walk in these ways, in the life you once lived. 8But now you must also rid yourselves of all such things as these: anger, rage, malice, slander, and filthy language from your lips. 9Do not lie to each other, since you have taken off your old self with its practices 10and have put on the new self, which is being renewed in knowledge in the image of its Creator. 11Here there is no Gentile or Jew, circumcised or uncircumcised, barbarian, Scythian, slave or free, but Christ is all, and is in all.

12Therefore, as God’s chosen people, holy and dearly loved, clothe yourselves with compassion, kindness, humility, gentleness and patience. 13Bear with each other and forgive one another if any of you has a grievance against someone. Forgive as the Lord forgave you. 14And over all these virtues put on love, which binds them all together in perfect unity.

15Let the peace of Christ rule in your hearts, since as members of one body you were called to peace. And be thankful. 16Let the message of Christ dwell among you richly as you teach and admonish one another with all wisdom through psalms, hymns, and songs from the Spirit, singing to God with gratitude in your hearts. 17And whatever you do, whether in word or deed, do it all in the name of the Lord Jesus, giving thanks to God the Father through him.

Instructions for Christian households

18Wives, submit yourselves to your husbands, as is fitting in the Lord.

19Husbands, love your wives and do not be harsh with them.

20Children, obey your parents in everything, for this pleases the Lord.

21Fathers,3:21 Or Parents do not embitter your children, or they will become discouraged.

22Slaves, obey your earthly masters in everything; and do it, not only when their eye is on you and to curry their favour, but with sincerity of heart and reverence for the Lord. 23Whatever you do, work at it with all your heart, as working for the Lord, not for human masters, 24since you know that you will receive an inheritance from the Lord as a reward. It is the Lord Christ you are serving. 25Anyone who does wrong will be repaid for their wrongs, and there is no favouritism.

Hausa Contemporary Bible

Kolossiyawa 3:1-25

Umarnai don zaman tsarki

1Da yake an tashe ku tare da Kiristi, sai ku sa zukatanku a kan abubuwan da suke sama, inda Kiristi yake zaune a hannun dama na Allah. 2Ku sa hankulanku a kan abubuwan sama, ba kan abubuwan duniya ba. 3Gama kun mutu, ranku yanzu kuwa yana ɓoye tare da Kiristi a cikin Allah. 4Sa’ad da Kiristi, wanda shi ne ranku,3.4 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da ranmu ya bayyana, ku ma za ku bayyana tare da shi cikin ɗaukaka.

5Saboda haka, sai ku fid da duk wani abin da yake kawo sha’awa a zukatanku, fasikanci, ƙazanta, sha’awa, muguwar sha’awa, da kuma kwaɗayi wanda shi ma bautar gumaka ne. 6Gama fushin Allah zai sauko a kan masu aikata waɗannan.3.6 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na farko-farko suna da zuwa a kan waɗanda suke rashin biyayya 7Dā kun yi waɗannan abubuwa, sa’ad da rayuwar tana cikin duniya mai wannan hali. 8Amma yanzu dole ku raba kanku da dukan ire-iren abubuwan nan. Ku daina fushi, ku daina ƙiyayya da ƙeta. Ku bar ɓatan suna da kuma ƙazamar magana daga leɓunanku. 9Kada ku yi wa juna ƙarya, da yake kun tuɓe tsohon halinku tare da ayyukansa 10kun ɗauki sabon halin nan da ake sabuntawa ga sani, bisa ga kamannin Mahaliccinsa. 11A wannan sabuwar rayuwa babu bambanci ko kai mutumin Al’ummai ne ko mutumin Yahuda, mai kaciya ne ko marar kaciya, baƙo, baƙauye, bawa ne ko ’yantacce, gama Kiristi shi ne kome, kuma yana cikin kome.

12Da yake Allah ya mai da ku zaɓaɓɓu, tsarkaka, ƙaunatattu, sai ku dinga jin tausayin juna, kuna yin alheri, kuna nuna tawali’u da sauƙinkai da jimrewa. 13Ku riƙa yin haƙuri da juna kuna kuma gafarta wa juna duk wani laifin da wani ya yi muku. Ku gafarta kamar yadda Ubangiji ya gafarce ku. 14Fiye da waɗannan duka, ku yi ƙaunar juna, gama ƙauna ce take haɗa kome gaba ɗaya.

15Ku bar salamar Kiristi tă yi mulki a zukatanku, da yake a matsayin gaɓoɓin jiki ɗaya an kira ku ga salama. Ku zama masu godiya. 16Ku bar maganar Kiristi ta zauna a cikinku a yalwace yayinda kuke koya, kuna kuma yi wa juna gargaɗi da dukan hikima, da kuma yayinda kuke waƙoƙin zabura, waƙoƙi da waƙoƙin ruhaniya tare da godiya a zukatanku ga Allah. 17Kuma ko mene ne kuke yi, ko cikin magana ko cikin ayyuka, ku yi shi duka a cikin sunan Ubangiji Yesu, kuna yin godiya ga Allah Uba ta wurinsa.

Umarnai don iyalan masu bi

18Mata, ku yi biyayya ga mazanku, yadda ya dace cikin Ubangiji.

19Maza, ku ƙaunaci matanku kada ku nuna musu hali marar tausayi.

20’Ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku cikin kome, gama wannan yakan gamshi Ubangiji.

21Ubanni, kada ku matsa wa yaranku lamba, don kada su fid da zuciya.

22Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya cikin kome; kada ku yi aikin ganin ido kamar masu neman yabon mutane, sai dai ku yi aiki tsakaninku da Allah, kamar masu tsoron Ubangiji. 23Kome kuke yi, ku yi shi da dukan zuciyarku, sai ka ce ga Ubangiji kuke yi, ba ga mutum ba. 24Kun san cewa zai ba ku gādo a matsayin ladanku. Ubangiji Kiristi ne fa kuke bauta wa. 25Duk wanda ya yi laifi, za a sāka masa don laifinsa, babu sonkai.