Yohana 10 – NEN & HCB

Kiswahili Contemporary Version (Neno: Bibilia Takatifu)

Yohana 10:1-42

Mchungaji Mwema

110:1 Yn 10:8, 10“Amin, amin nawaambia, yeye asiyeingia katika zizi la kondoo kwa kupitia kwenye lango, lakini akwea kuingia ndani kwa njia nyingine, ni mwizi na mnyangʼanyi. 210:2 Mk 6:34; Yn 10:11, 14Yeye anayeingia kwa kupitia kwenye lango ndiye mchungaji wa kondoo. 310:3 Yn 10:4, 5, 14Mlinzi humfungulia lango na kondoo huisikia sauti yake. Huwaita kondoo wake kwa majina yao na kuwatoa nje ya zizi. 410:4 Yn 10:3Akiisha kuwatoa wote nje, hutangulia mbele yao na kondoo humfuata kwa kuwa wanaijua sauti yake. 510:5 Yn 10:27Lakini kondoo hawatamfuata mgeni bali watamkimbia, kwa sababu hawaijui sauti ya mgeni.” 610:6 Yn 16:25; 16:25Yesu alitumia mfano huu, lakini wao hawakuelewa hayo aliyokuwa akiwaambia.

710:7 Za 118:20; Yn 14:6; Mt 7:13; 14Kwa hiyo Yesu akasema nao tena akawaambia, “Amin, amin nawaambia, mimi ndimi lango la kondoo. 810:8 Yer 23:1-2; Eze 34:2Wote walionitangulia ni wevi na wanyangʼanyi, lakini kondoo hawakuwasikia. 910:9 Za 118:20; Yn 14:6; 1Kor 3:15Mimi ndimi lango, yeyote anayeingia zizini kwa kupitia kwangu ataokoka, ataingia na kutoka, naye atapata malisho. 1010:10 Yn 1:4; 3:15, 16; 5:40; 20:31; Za 65:11; Rum 5:17Mwizi huja ili aibe, kuua na kuangamiza. Mimi nimekuja ili wapate uzima kisha wawe nao tele.

1110:11 Za 23:1; Mt 2:6; Yn 15:13; 1Yn 3:16“Mimi ndimi mchungaji mwema. Mchungaji mwema huutoa uhai wake kwa ajili ya kondoo. 1210:12 Zek 11:16-17Mtu wa kuajiriwa sio mchungaji mwenye kondoo. Amwonapo mbwa mwitu akija, yeye hukimbia na kuwaacha kondoo. Naye mbwa mwitu hulishambulia kundi na kulitawanya. 13Yeye hukimbia kwa sababu ameajiriwa wala hawajali kondoo.

1410:14 Kut 33:12; 2Tim 2:19“Mimi ndimi mchungaji mwema. Ninawajua kondoo wangu nao kondoo wangu wananijua. 1510:15 Mt 11:27; Yn 15:16Kama vile Baba anavyonijua mimi, nami ninavyomjua Baba, nami nautoa uhai wangu kwa ajili ya kondoo. 1610:16 Isa 56:8; Mdo 10:34-35; Yn 17:20-21; Efe 2:11-19; Eze 34:23; 1Pet 2:25Ninao kondoo wengine ambao si wa zizi hili, inanipasa kuwaleta, nao wataisikia sauti yangu, hivyo patakuwa na kundi moja na mchungaji mmoja. 1710:17 Isa 53:7, 8, 12; Ebr 2:9Baba yangu ananipenda kwa kuwa ninautoa uhai wangu ili niupate tena. 1810:18 Mt 26:53; Flp 2:8; Ebr 5:8Hakuna mtu aniondoleaye uhai wangu, bali ninautoa kwa hiari yangu mwenyewe. Ninao uwezo wa kuutoa uhai wangu na pia ninao uwezo wa kuutwaa tena. Amri hii nimepewa na Baba yangu.”

1910:19 Yn 6:52Kwa maneno haya Wayahudi waligawanyika. 2010:20 Mk 3:22; Yn 7:20; 2Fal 9:11Wengi wao wakasema, “Huyu amepagawa na pepo mchafu, naye amechanganyikiwa.”

2110:21 Mt 4:24; Kut 4:11; Yn 9:32-33Wengine wakasema, “Haya si maneno ya mtu aliyepagawa na pepo mchafu. Je, pepo mchafu aweza kufungua macho ya kipofu?”

Yesu Akataliwa Na Wayahudi

22Wakati huo ilikuwa Sikukuu ya Kuwekwa wakfu kwa Hekalu10:22 Sikukuu ya Kuwekwa wakfu kwa Hekalu ni Hanukkah kwa Kiebrania. huko Yerusalemu, nao ulikuwa wakati wa majira ya baridi. 2310:23 Mdo 3:11; 5:12Naye Yesu alikuwa akitembea ndani ya Hekalu katika ukumbi wa Solomoni. 2410:24 Yn 1:19; Lk 22:67Wayahudi wakamkusanyikia wakamuuliza, “Utatuweka katika hali ya mashaka mpaka lini? Kama wewe ndiye Kristo10:24 Kristo maana yake ni Masiya, yaani Aliyetiwa mafuta. tuambie waziwazi.”

2510:25 Yn 4:26; 4:11Yesu akawajibu, “Nimewaambia, lakini hamwamini. Mambo ninayoyatenda kwa jina la Baba yangu yananishuhudia. 2610:26 Yn 8:47Lakini hamwamini, kwa sababu ninyi si wa kundi la kondoo wangu. 2710:27 Yn 10:4, 14Kondoo wangu huisikia sauti yangu nami nawajua, nao hunifuata, 2810:28 Yn 6:39nami ninawapa uzima wa milele, hawataangamia kamwe wala hakuna mtu atakayewapokonya kutoka mikono yangu. 2910:29 Yn 17:2, 6, 24; 14:28Baba yangu aliyenipa hawa ni mkuu kuliko wote na hakuna awezaye kuwapokonya kutoka mikononi mwake. 3010:30 Kum 6:4; Yn 17:21-24Mimi na Baba yangu tu umoja.”

3110:31 Yn 8:59Kwa mara nyingine Wayahudi wakainua mawe ili wampige nayo, 32lakini Yesu akawaambia, “Nimewaonyesha miujiza mingi mikubwa kutoka kwa Baba yangu. Ni ipi katika hiyo mnataka kunipiga mawe?”

3310:33 Law 24:16; Mt 26:63-66Wayahudi wakamjibu, “Hatukupigi mawe kwa sababu ya mambo mema uliyotenda, bali ni kwa kuwa umekufuru. Wewe ingawa ni mwanadamu unajifanya kuwa Mungu.”

3410:34 Rum 3:19; 1Kor 14:21; Za 82:6Yesu akawajibu, “Je, haikuandikwa katika Sheria ya kwamba, ‘Nimesema kuwa, ninyi ni miungu?’ 3510:35 Rum 13:1; Mt 5:17, 18Kama aliwaita ‘miungu,’ wale ambao neno la Mungu liliwafikia, nayo Maandiko hayawezi kutanguka, 3610:36 Yer 1:5; Yn 6:69; 3:17je, mwawezaje kusema kwamba yule ambaye Baba amemweka wakfu na kumtuma ulimwenguni anakufuru, kwa sababu nilisema, ‘Mimi ni Mwana wa Mungu?’ 3710:37 Yn 15:24Ikiwa sifanyi kazi za Baba yangu, basi msiniamini, 3810:38 Yn 14:10-11; 20:17-21lakini ikiwa nazifanya kazi za Mungu, hata kama hamniamini mimi ziaminini hizo kazi, ili mpate kujua na kuelewa kwamba Baba yu ndani yangu, nami ndani yake.” 3910:39 Yn 7:30; Lk 4:30; Yn 8:59Ndipo wakajaribu kumkamata kwa mara nyingine, lakini akaponyoka kutoka mikononi mwao.

4010:40 Yn 1:28Akaenda tena ngʼambo ya Mto Yordani mpaka mahali pale ambapo Yohana alikuwa akibatiza hapo awali, naye akakaa huko. 4110:41 Yn 2:1; 1:26-34Watu wengi wakamjia, nao wakawa wakisema, “Yohana hakufanya muujiza wowote, lakini kila jambo alilosema kumhusu huyu mtu ni kweli.” 4210:42 Yn 7:31Nao wengi wakamwamini Yesu huko.

Hausa Contemporary Bible

Yohanna 10:1-42

Makiyayi da garkensa

1“Gaskiya nake gaya muku, mutumin da bai shiga inda ake ajiye garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya hau ta katanga, ɓarawo ne, ɗan fashi kuma. 2Mutumin da ya shiga ta ƙofa makiyayin tumakinsa ne. 3Mai gadin yakan buɗe wa makiyayin ƙofa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa. Yakan kira tumakinsa da suna, yă kuma fid da su waje. 4Sa’ad da ya fitar da dukan nasa waje, sai ya ja gabansu, tumakinsa kuma sukan bi shi domin sun san muryarsa. 5Amma ba za su taɓa bin baƙo ba; sai dai ma su guje masa don ba su san muryar baƙo ba.” 6Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su fahimci abin da yake faɗa musu ba.

7Saboda haka Yesu ya sāke cewa, “Gaskiya nake gaya muku, ni ne ƙofar tumakin. 8Duk waɗanda suka riga ni zuwa ɓarayi ne, ’yan fashi kuma, amma tumakin ba su saurare su ba. 9Ni ne ƙofar; duk wanda ya shiga ta wurina zai sami ceto. Zai riƙa shiga yă fita yă kuwa sami wurin kiwo. 10Ɓarawo yakan zo don yă yi sata ne kawai da kisa da kuma ɓarna. Ni kuwa na zo ne don su sami rai, su kuma same shi a yalwace.

11“Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau yakan ba da ransa domin tumakin. 12Wanda aka ɗauko haya ba shi ne makiyayi mai tumakin ba. Saboda haka sa’ad da ya ga kyarkeci yana zuwa, sai yă sheƙa da gudu yă bar tumakin. Sai kyarkecin yă kai wa garken hari, yă kuma watsar da su. 13Mutumin yakan gudu don shi ɗan haya ne kawai, bai kuwa damu da tumakin ba.

14“Ni ne makiyayi mai kyau; na san tumakina, tumakina kuma sun san ni, 15kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uba, ina kuwa ba da raina domin tumakin. 16Ina da waɗansu tumaki da ba na wannan garken ba ne. Dole ne in kawo su su ma. Za su saurari muryata, za su kasance garke guda ɗaya, makiyayi guda kuma. 17Abin da ya sa Ubana yake ƙaunata ke nan, domin ina ba da raina, in ɗauko shi kuma. 18Ba mai karɓe mini rai, ina dai ba da shi. Ina da iko in ba da shi, ina da iko in ɗauko shi kuma. Wannan umarni kuwa daga wurin Ubana na karɓo shi.”

19Saboda waɗannan kalmomi fa, sai ɓaraka ta sāke shiga cikin Yahudawa. 20Da yawa daga cikinsu suka ce, “Yana da aljani, yana kuma hauka. Don me za ku saurare shi?”

21Amma waɗansu suka ce, “Kai, waɗannan kalmomi ba na mai aljani ba ne. Anya, aljani yana iya buɗe idanun makaho?”

Rashin bangaskiyar Yahudawa

22Bikin Miƙawa10.22 Wato, Hanukka a Urushalima ya kewayo, lokacin sanyin hunturu ne kuwa. 23Sai ga Yesu a filin haikali yana zagawa a Shirayin Solomon, 24sai Yahudawa suka taru kewaye da shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In kai ne Kiristin, ka faɗa mana a fili mana.”

25Yesu ya amsa ya ce, “Na faɗa muku, amma ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi cikin sunan Ubana su suke nuna ko wane ne ni. 26Amma ba ku gaskata ba domin ku ba tumakina ba ne. 27Tumakina sukan saurari muryata; na sansu, suna kuma bi na. 28Ina ba su rai madawwami, ba za su taɓa hallaka ba; ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. 29Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba mai ƙwace su daga hannun Ubana. 30Da ni da Uba ɗaya ne.”

31Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, 32amma Yesu ya ce musu, “Na nuna muku ayyukan alheri masu yawa da Uba ya aiko ni in yi, a kan wanne kuke so ku jajjefe ni?”

33Yahudawa suka amsa suka ce, “Ai, ba don wani daga cikin waɗannan ayyukan alheri ne muke so mu jajjefe ka ba, amma don saɓon da kake yi, kai da kake mutum kawai, kana mai da kanka Allah.”

34Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a cikin Dokarku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne’10.34 Zab 82.6? 35Mun dai san Nassi ba ya ƙarya, In har ya kira su waɗanda maganar Allah ta zo musu, ‘alloli,’ 36to, game da wanda Uba ya keɓe a matsayin nasa ne ya kuma aiko shi duniya. Don me kuke ce saɓo nake, domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’ 37In ba ayyukan da Ubana yake yi ne nake yi ba, to, kada ku gaskata ni. 38Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.” 39Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.

40Sa’an nan Yesu ya sāke koma ƙetaren Urdun inda dā Yohanna yake baftisma. A can ya zauna 41mutane da yawa suka zo wurinsa. Suka ce, “Ko da yake Yohanna bai yi wani abin banmamaki ba, duk abubuwan da Yohanna ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.” 42A nan kuwa mutane da yawa suka gaskata da Yesu.