प्रेरितमन के काम 3 – NCA & HCB

New Chhattisgarhi Translation (नवां नियम छत्तीसगढ़ी)

प्रेरितमन के काम 3:1-26

पतरस ह एक झन खोरवा भिखमंगा ला बने करथे

1एक दिन पतरस अऊ यूहन्ना मंझनियां के तीन बजे पराथना के बेरा मंदिर जावत रिहिन। 2मनखेमन एक जनम के खोरवा ला लावत रिहिन। ओमन ओला हर दिन मंदिर के सुन्‍दर नांव के दुवारी म बईठा देवंय कि ओह मंदिर म जवइयामन ले भीख मांगय। 3जब ओह पतरस अऊ यूहन्ना ला मंदिर म जावत देखिस, त ओमन ले भीख मांगिस। 4पतरस ह यूहन्ना के संग ओकर कोति एकटक देखके कहिस, “हमर कोति देख।” 5ओह ओमन ले कुछू पाय के आसा म ओमन कोति ताके लगिस।

6तब पतरस ह कहिस, “चांदी अऊ सोना तो मोर करा नइं ए, पर जऊन चीज मोर करा हवय, मेंह तोला देवत हंव। यीसू मसीह नासरी के नांव म, तेंह उठ अऊ रेंग।” 7पतरस ह ओकर जेवनी हांथ ला धरके ओला ठाढ़ होय म मदद करिस अऊ तुरते खोरवा के गोड़ अऊ एड़ी मन म बल आ गीस। 8ओह कूदके ठाढ़ हो गीस अऊ चले फिरे लगिस। ओह चलत, कूदत अऊ परमेसर के भजन करत ओमन के संग मंदिर म गीस। 9जब जम्मो मनखेमन ओला चलत-फिरत अऊ परमेसर के भजन करत देखिन, 10त ओमन ओला चिन डारिन कि एह ओहीच ए, जऊन ह मंदिर के सुन्‍दर नांव के दुवारी म बईठके भीख मांगे करत रिहिस, अऊ ओमन ओकर संग जऊन कुछू होय रिहिस, ओला देखके अचरज अऊ अचम्भो करिन।

पतरस ह भीड़ ले गोठियाथे

11जब ओ भिखमंगा ह पतरस अऊ यूहन्ना के संग रहय, त जम्मो मनखेमन बहुंत अचरज करत सुलेमान के मंडप म ओमन करा दऊड़त आईन। 12एला देखके पतरस ह मनखेमन ला कहिस, “हे इसरायलीमन, तुमन ए मनखे ला देखके काबर अचरज करत हव? तुमन हमर कोति अइसने काबर देखत हव कि मानो हमेच मन अपन सक्ति या भक्ति ले एला चले-फिरे के लइक बना दे हवन? 13अब्राहम, इसहाक, अऊ याकूब के परमेसर, हमर बाप-ददा मन के परमेसर ह अपन दास यीसू के महिमा करिस, जऊन ला तुमन मरवाय बर पकड़वाय रहेव। अऊ जब पीलातुस ह ओला छोंड़ देके फैसला करिस, त तुमन ओकर आघू म यीसू के इनकार करेव। 14तुमन ओ पबितर अऊ धरमी जन के इनकार करेव, अऊ पीलातुस ले ए बिनती करेव कि एक हतियारा ला तुम्‍हर खातिर छोंड़ देवय। 15तुमन जिनगी के देवइया ला मार डारेव, जऊन ला परमेसर ह मरे मन ले जियाईस, अऊ हमन ए बात के गवाह हवन। 16ओहीच यीसू के नांव म बिसवास के दुवारा, ए मनखे ह सक्ति पाईस, जऊन ला तुमन देखत अऊ जानत हवव। एह यीसू के नांव अऊ बिसवास, जऊन ह यीसू के दुवारा आथे, एला एकदम भला-चंगा कर दे हवय जइसने कि तुमन जम्मो देखत हवव।

17हे भाईमन हो, मेंह जानत हंव कि ए काम ला तुमन अगियानता म करेव अऊ वइसनेच तुम्‍हर अगुवामन घलो करिन। 18पर जऊन बातमन ला परमेसर ह जम्मो अगमजानीमन के दुवारा आघू ले बताय रिहिस कि ओकर मसीह ह दुःख उठाही, ओ बातमन ला ओह अइसने पूरा करिस। 19एकरसेति, अब तुमन अपन पापमन ले मन फिरावव अऊ परमेसर करा लहुंटव कि तुम्‍हर पापमन मिटाय जावय, अऊ परभू करा ले आनंद मिलय, 20अऊ ओह ओ मसीह यीसू ला पठोवय, जऊन ह तुम्‍हर बर आघूच ले ठहराय गे हवय। 21ए जरूरी ए कि ओह स्‍वरग म ओ बखत तक रहय, जब तक कि ओह जम्मो बातमन के सुधार नइं कर लेवय, जेकर बारे म परमेसर ह अपन पबितर अगमजानीमन के दुवारा बहुंत पहिली कहे रिहिस। 22जइसने मूसा ह कहे रिहिस, ‘परभू परमेसर ह तुम्‍हर अपन मनखेमन ले तुम्‍हर बर मोर सहीं एक अगमजानी ठाढ़ करही; जऊन कुछू ओह तुम्‍हर ले कहय, तुमन ओकर जरूर सुनव। 23पर जऊन मनखे ओ अगमजानी के बात ला नइं सुनही, ओह अपन मनखेमन ले पूरा-पूरी नास करे जाही।’3:23 ब्यवस्था 18:15, 18, 19

24वास्तव म, सामुएल अगमजानी ले लेके ओकर बाद अवइया जम्मो अगमजानीमन परमेसर के जऊन बचन कहे हवंय, ओ जम्मो झन इहीच दिनमन के बारे म कहे हवंय। 25तुमन अगमजानीमन के संतान अऊ ओ करार के संतान अव, जऊन ला परमेसर ह तुम्‍हर बाप-ददा संग करे रिहिस। ओह अब्राहम ले कहे रिहिस, ‘तोर बंस के दुवारा धरती के जम्मो मनखेमन आसिस पाहीं।’3:25 उतपत्ती 22:18 26जब परमेसर ह अपन दास ला जियाईस, त ओह ओला पहिली तुम्‍हर करा पठोईस कि ओह तुमन ले हर एक ला ओकर बुरई ले बचाय के दुवारा आसिस देवय।”

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 3:1-26

Bitrus ya warkar da gurgu mai bara

1Wata rana, Bitrus da Yohanna suna haurawa zuwa haikali a lokacin addu’a da ƙarfe uku na rana. 2To, sai ga wani da aka haifa gurgu ana ɗauke da shi zuwa ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, inda akan ajiye kowace rana, don yă yi bara daga masu shigowa cikin filayen haikali. 3Da ya ga Bitrus da Yohanna suna gab da shiga, sai ya roƙe su kuɗi. 4Bitrus kuwa ya kafa masa ido, haka ma Yohanna. Sai Bitrus ya ce, “Dube mu!” 5Saboda haka mutumin ya mai da hankalinsa a kansu, yana fata samun wani abu daga gare su.

6Sai Bitrus ya ce, “Azurfa ko zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. A cikin sunan Yesu Kiristi Banazare, ka yi tafiya.” 7Ta wurin kama hannunsa na dama, ya taimake shi ya miƙe, nan take ƙafafu da idon sawun mutumin suka yi ƙarfi. 8Sai ya yi wuf da ƙafafunsa ya fara tafiya. Ya tafi tare da su ya shiga cikin filin haikali yana tafiya yana tsalle, yana kuma yabon Allah. 9Sa’ad da dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana yabon Allah, 10sai suka gane cewa shi ne mutumin nan wanda dā yake zama yana bara a bakin ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, suka kuwa cika da mamaki da tsoro a kan abin da ya faru gare shi.

Bitrus ya yi wa masu kallo magana

11Tun mai bawan yana riƙe da Bitrus da Yohanna, dukan mutanen suka yi mamaki, suka zo wurinsu a guje a inda ake kira Shirayin Solomon. 12Da Bitrus ya ga haka, sai ya ce musu, “Mutanen Isra’ila, don me wannan ya ba ku mamaki? Don me kuke kallonmu sai ka ce da ikon kanmu ne ko kuwa don ibadarmu ne muka sa wannan mutum ya yi tafiya? 13Allah na Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub, Allah na kakanninmu, ya ɗaukaka bawansa Yesu. Ku kuka ba da shi domin a kashe, kuka yi mūsun saninsa a gaban Bilatus, ko da yake ya yi niyya ya sake shi. 14Kuka yi mūsun sanin Mai Tsarki da Mai Adalci kuka roƙa a sakar muku mai kisankai. 15Kuka kashe tushen rai, amma Allah ya tashe shi daga matattu. Mu shaidu ne ga wannan. 16Ta wurin bangaskiya cikin sunan Yesu ne wannan mutum da kuke gani kuka kuma sani ya sami ƙarfi. Da sunan Yesu, da kuma bangaskiyar da take samuwa ta wurinsa ne ya ba shi cikakkiyar warkarwa, yadda dukanku kuke gani.

17“To, ’yan’uwa, na san cewa, kun aikata wannan cikin jahilci ne, yadda shugabanninku suka yi. 18Amma ta haka ne Allah ya cika abin da ya rigyafaɗi ta bakin dukan annabawa cewa, Kiristinsa zai sha wahala. 19Saboda haka ku tuba, ku juyo ga Allah, don a shafe zunubanku, don lokutan wartsakewa su zo daga wurin Ubangiji, 20don kuma ya iya aika da Kiristi, wanda aka naɗa tun dā saboda ku, Yesu ke nan. 21Dole yă kasance a sama, sai lokaci ya yi da Allah zai mai da kome sabo, yadda ya yi alkawari tun dā ta wurin annabawansa masu tsarki. 22Gama Musa ya ce, ‘Ubangiji Allahnku zai tasar muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku; dole ku saurari duk abin da ya faɗa muku. 23Duk wanda bai saurare shi ba za a ware shi gaba ɗaya daga mutanensa.’3.23 M Sh 18.15,18,19

24“Tabbatacce, dukan annabawa daga Sama’ila zuwa gaba, dukansu da suka yi magana, sun rigya faɗin waɗannan kwanaki. 25Ku kuwa magādan annabawan ne da kuma na alkawarin da Allah ya yi da kakanninku. Ya ce wa Ibrahim, ‘Ta wurin zuriyarka, dukan kabilan duniya za su sami albarka.’3.25 Far 22.18; Far 26.4 26Da Allah ya tashe bawansa, ya aike shi da fari zuwa gare ku don yă albarkace ku ta wurin juye kowannenku daga mugayen hanyoyinku.”