마태복음 5 – KLB & HCB

Korean Living Bible

마태복음 5:1-48

산상 설교

1예수님은 많은 사람들이 모여드는 것을 보시고 산에 올라가 앉으셨다. 그러자 제자들이 그분에게 나아왔다.

2그래서 예수님은 그들에게 이렇게 가르치셨다.

3“마음이 가난한 사람들은 행복하다. 하늘 나라가 그들의 것이다.

4슬퍼하는 사람들은 행복하다. 그들은 위로를 받을 것이다.

5유순한 사람들은 행복하다. 그들은 땅을 물려받을 것이다.

6의를 위해 굶주리고 목마른 사람들은 행복하다. 그들은 5:6 또는 ‘배부를 것임이요’원하는 것을 다 얻을 것이다.

7남을 불쌍히 여기는 사람들은 행복하다. 하나님도 그들을 불쌍히 여기실 것이다.

8마음이 깨끗한 사람들은 행복하다. 그들은 하나님을 볼 것이다.

9화평을 이루는 사람들은 행복하다. 그들은 하나님의 아들이라 불릴 것이다.

10의를 위해 핍박을 받는 사람들은 행복하다. 하늘 나라가 그들의 것이다.

11“나 때문에 사람들이 너희를 욕하고 핍박하고 거짓말로 온갖 악담을 할 때에 너희는 행복하다.

12하늘에서 큰 상이 너희를 기다리고 있다. 기뻐하고 즐거워하여라. 이전의 예언자들도 이런 핍박을 받았다.

13“너희는 세상의 소금이다. 그런데 소금이 그 맛을 잃으면 어떻게 다시 짜게 할 수 있겠느냐? 그런 것은 아무 쓸모가 없어 밖에 버려져 사람들에게 짓밟힐 뿐이다.

14너희는 세상의 빛이다. 산 위에 있는 마을은 잘 보이기 마련이다.

15등불을 켜서 그릇으로 덮어 둘 사람은 아무도 없다. 오히려 그것을 등잔대 위에 올려놓아 집 안에 있는 모든 사람에게 비치게 하지 않겠느냐?

16이와 같이 너희 빛을 사람들 앞에 비추게 하라. 그래서 사람들이 너희 착한 행실을 보고 하늘에 계신 너희 아버지를 찬양하게 하라.

17“내가 율법이나 예언자들을 없애러 왔다고 생각하지 말아라. 없애러 온 것이 아니라 완전하게 하러 왔다.

18내가 분명히 말해 둔다. 하늘과 땅이 없어지기 전에는 율법의 5:18 헬 ‘한 이오타’ (헬라어 알파벳 중 제일 작은 문자)한 점이나 한 획도 결코 없어지지 않고 다 이루어질 것이다.

19누구든지 이 계명 가운데 가장 작은 것 하나라도 어기거나 다른 사람에게 그렇게 하라고 가르치면 하늘 나라에서 가장 작은 사람이 될 것이다. 그러나 누구든지 계명을 실천하고 가르치면 하늘 나라에서 위대한 사람이 될 것이다.

20내가 너희에게 말해 두지만 너희 생활이 율법학자들과 바리새파 사람들보다 의롭지 못하면 너희가 절대로 하늘 나라에 들어가지 못할 것이다.

215:21 원문에는 ‘옛 사람에게 말한 바’모세의 법에는 5:21 출20:13‘살인하지 말아라. 살인하면 누구든지 재판을 받게 된다’ 라고 쓰여 있다.

22그러나 나는 너희에게 말한다. 누구든지 형제에게 이유 없이 화내는 사람은 재판을 받고, 자기 형제를 5:22 아람어 ‘라가.’ ‘미련한’, ‘어리석은’ 이란 뜻.어리석다고 욕하는 사람은 5:22 헬 ‘수네드리온’ (공회)법정에 끌려가게 될 것이며, ‘이 미련한 놈아!’ 하고 말하는 사람은 5:22 헬 ‘게엔나’지옥 불에 들어갈 것이다.

23그러므로 제단에 예물을 드리다가 형제에게 원망 들을 만한 일이 생각나거든

24예물을 제단 앞에 두고 먼저 가서 네 형제와 화해하라. 그리고 와서 예물을 드려라.

25너를 고소하려는 사람과 함께 법정으로 갈 때 너는 도중에 그와 재빨리 타협하라. 그렇지 않고 재판을 받는 날이면 유치장 신세를 져야 할 것이다.

26그렇게 되면 네가 5:26 또는 ‘호리’마지막 한푼까지 다 갚기 전에는 절대로 거기서 나오지 못할 것이다.

27“또 율법에는 5:27 출20:14, 신5:18‘간음하지 말아라’ 고 쓰여 있다.

28그러나 나는 너희에게 말한다. 누구든지 정욕의 눈으로 여자를 바라보는 사람은 이미 마음으로 그녀와 간음하였다.

29오른눈이 너를 죄 짓게 하거든 빼어 버려라. 몸의 한 부분을 잃을지라도 온 몸이 지옥에 던져지지 않는 것이 더 낫다.

30또 오른손이 너를 죄 짓게 하면 그 손을 잘라 버려라. 몸의 한 부분을 잃을지라도 온 몸이 지옥에 떨어지지 않는 것이 더 낫다.

31“또 율법에 5:31 신24:1‘자기 아내와 이혼하는 사람은 누구든지 그녀에게 이혼 증서를 써 주어야 한다’ 라고 쓰여 있다.

32그러나 나는 너희에게 말한다. 누구든지 음행한 일도 없는데 자기 아내와 이혼하는 사람은 아내로 간음하게 하는 자이며 이혼한 여자와 결혼하는 사람도 간음하는 자이다.

33“또 옛 사람들에게 ‘거짓 맹세를 하지 말고 주님께 맹세한 것은 다 지켜라’ 고 한 말을 들어서 알 것이다.

34그러나 나는 너희에게 말한다. 절대로 맹세하지 말아라. 하늘을 두고도 맹세하지 말아라. 하늘은 하나님의 보좌이다.

35땅을 두고도 맹세하지 말아라. 땅은 하나님의 발판이다. 예루살렘을 두고도 맹세하지 말아라. 예루살렘은 위대한 왕의 도시이다.

36네 머리를 두고도 맹세하지 말아라. 너는 머리카락 하나도 희거나 검게 할 수가 없다.

37너희는 그저 ‘예’ 할 것은 ‘예’ 하고 ‘아니오’ 할 것은 ‘아니오’ 라고만 말하여라. 그 이상의 말은 악에서 나오는 것이다.

38“또 5:38 출21:24, 레24:20, 신19:21‘눈은 눈으로, 이는 이로 갚아라’ 한 말을 듣지 않았느냐?

39그러나 나는 너희에게 말한다. 악한 사람을 대적하지 말아라. 누가 네 오른뺨을 때리거든 왼뺨도 돌려 대어라.

40너를 고소하여 속옷을 빼앗고자 하는 사람에게는 겉옷까지 주어라.

41누가 네게 억지로 오 리를 가자 하거든 십 리를 가 주어라.

42네게 요구하는 사람에게 주고 꾸어 달라는 사람에게 거절하지 말아라.

435:43 레19:18‘네 이웃을 사랑하고 원수를 미워하여라’ 는 말씀을 듣지 않았느냐?

44그러나 나는 너희에게 말한다. 원수를 사랑하고 너희를 핍박하는 사람들을 위해 기도하라.

45그렇게 하는 것이 하나님 아버지의 자녀 된 도리이다. 하나님은 해가 악한 사람과 선한 사람에게 다 같이 비치게 하시고 의로운 사람과 의롭지 못한 사람에게 비를 똑같이 내려 주신다.

46너희를 사랑하는 사람들만 사랑한다면 너희가 무슨 상을 받겠느냐? 세무원들도 그만큼은 하지 않느냐?

47또 너희가 너희 형제들에게만 인사한다면 남보다 나을 것이 무엇이겠느냐? 5:47 원문에는 ‘이방인들’믿지 않는 사람들도 그렇게 하지 않느냐?

48그러므로 하늘에 계신 너희 아버지께서 완전하심과 같이 너희도 완전하여라.”

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 5:1-48

Albarku

1Ganin taron mutane, sai ya hau kan gefen dutse ya zauna.

(Luka 6.20-23)

Almajiransa kuwa suka zo wurinsa, 2sai ya fara koya musu.

Yana cewa,

3“Masu albarka ne waɗanda suke matalauta a ruhu,

gama mulkin sama nasu ne.

4Masu albarka ne waɗanda suke makoki,

gama za a yi musu ta’aziyya.

5Masu albarka ne waɗanda suke masu tawali’u,

gama za su gāji duniya.

6Masu albarka ne waɗanda suke jin yunwa da ƙishirwa don gani an yi adalci,

gama za a ƙosar da su.

7Masu albarka ne waɗanda suke masu jinƙai,

gama za a nuna musu jinƙai.

8Masu albarka ne waɗanda suke masu tsabtar zuciya,

gama za su ga Allah.

9Masu albarka ne waɗanda suke masu ƙulla zumunci,

gama za a kira su ’ya’yan Allah.

10Masu albarka ne waɗanda ake tsananta musu don gani an yi adalci,

gama mulkin sama nasu ne.

11“Masu albarka ne ku, sa’ad da mutane suke zaginku, suna tsananta muku, suna kuma faɗin kowace irin muguwar magana a kanku saboda ni. 12Ku yi murna ku kuma yi farin ciki, domin ladarku mai yawa ne a sama, gama haka suka tsananta wa annabawan da suka riga ku.

Gishiri da kuma haske

(Markus 9.50; Luka 14.34,35)

13“Ku ne gishirin duniya, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa? Ba shi da sauran amfani, sai dai a zubar da shi mutane kuma su tattaka.

14“Ku ne hasken duniya. Birnin da yake a bisan tudu ba ya ɓoyuwa. 15Mutane ba sa ƙuna fitila su rufe ta da murfi. A maimako, sukan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, takan kuma ba da haske ga kowa a cikin gida. 16Haka ma, bari haskenku yă haskaka a gaban mutane, domin su ga ayyukanku masu kyau, su kuwa yabi Ubanku da yake cikin sama.

Cikar doka

17“Kada ku yi tsammani na zo ne domin in kawar da Doka ko kuma Annabawa; ban zo domin in kawar da su ba ne, sai dai domin in ciccika su. 18Gaskiya nake gaya muku, kafin sama da ƙasa sun shuɗe, babu ko ɗan wasali, babu wani ɗigo ta kowace hanya da zai ɓace daga Dokar, sai an cika kome. 19Duk wanda ya karya ɗaya daga cikin mafi ƙanƙanta na umarnan nan, ya kuma koya wa waɗansu su yi haka, za a ce da shi mafi ƙanƙanta a mulkin sama. Amma duk wanda ya aikata, ya kuma koyar da waɗannan umarnai, za a kira shi mai girma a cikin mulkin sama. 20Gama ina faɗa muku cewa in dai adalcinku bai fi na Farisiyawa da na malaman dokoki ba, faufau, ba za ku shiga mulkin sama ba.

Kisankai

21“Kun dai ji an faɗa wa mutanen dā cewa, ‘Kada ka yi kisankai;5.21 Fit 20.13 kuma duk wanda ya yi kisankai za a hukunta shi.’ 22Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da ɗan’uwansa, za a hukunta shi. Kuma duk wanda ya ce wa ɗan’uwansa ‘Raka,’5.22 Kalmar Arameyik ta reni za a kai shi gaban Majalisa. Amma duk wanda ya ce, ‘Kai wawa!’ Zai kasance a hatsarin shiga jahannama ta wuta.

23“Saboda haka, in kana cikin ba da baikonka a kan bagade, a can kuwa ka tuna cewa ɗan’uwanka yana riƙe da kai a zuci, 24sai ka bar baikonka a can gaban bagade. Ka je ka shirya tukuna da ɗan’uwanka; sa’an nan ka zo ka ba da baikonka.

25“Ka yi hanzari ka shirya al’amura da maƙiyinka wanda yake ƙararka a kotu. Ka yi haka, tun kana tare da shi a kan hanya, in ba haka ba, zai miƙa ka ga alƙali, alƙali kuma yă miƙa ka ga ɗan sanda, mai yiwuwa kuwa a jefa ka a kurkuku. 26Gaskiya nake gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.

Zina

27“Kun dai ji an faɗa, ‘Kada ka yi zina.’5.27 Fit 20.14 28Amma ina gaya muku, duk wanda ya dubi mace, sa’an nan ya yi sha’awarta a zuci, ya riga ya yi zina ke nan da ita a zuciyarsa. 29In idonka na dama yana sa ka yin zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. 30In kuma hannunka na dama yana sa ka yin zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta.

Kashen aure

(Mattiyu 19.9; Markus 10.11,12; Luka 16.18)

31“An kuma faɗa, ‘Duk wanda ya saki matarsa, dole yă ba ta takardar saki.’5.31 M Sh 24.1 32Amma ina gaya muku, duk wanda ya saki matarsa in ba a kan laifin zina ba, ya sa ta zama mazinaciya ke nan, kuma duk wanda ya auri macen da mijinta ya sake, shi ma yana zina ne.

Rantsuwa

33“Har wa yau dai kun ji an faɗa wa mutane a dā, ‘Kada ka karya alkawarinka, sai dai ka cika alkawaran da ka yi wa Ubangiji.’ 34Amma ina gaya muku, Kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama, domin kursiyin Allah ne; 35ko da ƙasa, domin matashin ƙafafunsa ne; ko kuma da Urushalima, domin birnin Babban Sarki ne. 36Kada kuma ka rantse da kanka, domin ba za ka iya mai da ko gashi ɗaya yă zama fari ko baƙi ba. 37Abin da ya kamata ku ce kawai, shi ne, I, ko A’a. Abin da ya wuce haka kuwa daga wurin Mugun nan yake.

Ramuwa

(Luka 6.29,30)

38“Kun dai ji an faɗa, ‘Ido domin ido, haƙori kuma domin haƙori.’5.38 Fit 21.24; Fir 24.20; M Sh 19.21 39Amma ina gaya muku, Kada ku yi tsayayya da mugun mutum. In wani ya mare ka a kumatun dama, juya masa ɗayan ma. 40In kuma wani yana so yă yi ƙararka yă ƙwace rigarka, to, ba shi mayafinka ma. 41In wani ya tilasta ka yin tafiya mil ɗaya, to, tafi tare da shi mil biyu. 42Ka ba wa duk wanda ya roƙe ka abu, kada kuma ka hana wa wanda yake neman bashi daga gare ka.

Ƙauna don abokan gāba

(Luka 6.27,28,32-36)

43“Kun dai ji an faɗa, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka,5.43 Fir 19.18 ka kuma ƙi abokin gābanka.’ 44Amma ina gaya muku, ku ƙaunaci abokan gābanku5.44 Waɗansu rubuce-rubucen hannun da ba su jima ba suna da abokan gāba, ku sa wa waɗanda suke la’antarku albarka, ku yi wa waɗanda suke ƙinku alheri kuma ku yi wa waɗanda suke tsananta muku addu’a, 45don ku zama ’ya’yan Ubanku na sama. Shi yakan sa ranarsa ta haskaka a kan mugaye da masu kirki; yakan kuma sako ruwan sama a bisa masu adalci da marasa adalci. 46In masoyarku kawai kuke ƙauna, wace lada ce gare ku? Ko masu karɓar haraji ma ba haka suke yi ba? 47In kuwa kuna gai da ’yan’uwanku ne kaɗai, me kuke yi fiye da waɗansu? Marasa bin Allah ma ba haka suke yi ba? 48Saboda haka sai ku zama cikakku, yadda Ubanku na sama yake cikakke.