ヨハネの黙示録 7 – JCB & HCB

Japanese Contemporary Bible

ヨハネの黙示録 7:1-17

7

神に選ばれた人々

1それから私は、四人の天使が地の四すみに立っているのを見ました。彼らは、四方からの風をしっかり押さえていたので、木の葉一枚そよがず、海面は鏡のように静かでした。 2次に、もう一人の天使が、生ける神の大きな刻印を持って、東から来るのが見えました。彼は、地と海とを破壊する権限を与えられた四人の天使に、大声で叫びました。 3「お待ちなさい。私たちが、神に仕える人々の額に神の刻印を押し終わるまでは、手出しをしてはなりません。地にも海にも木にも、害を加えてはいけません。」

4-8それから私が、「いったい何人の人に、神の刻印がつけられたのでしょうか」と尋ねると、「十四万四千人」という答えが返ってきました。その人々は、イスラエルの全十二部族から選ばれていました。内訳は次のようです。ユダの部族一万二千人、ルベンの部族一万二千人、ガドの部族一万二千人、アセルの部族一万二千人、ナフタリの部族一万二千人、マナセの部族一万二千人、シメオンの部族一万二千人、レビの部族一万二千人、イッサカルの部族一万二千人、ゼブルンの部族一万二千人、ヨセフの部族一万二千人、ベニヤミンの部族一万二千人。

9その後、私の目には、おびただしい群衆が映りました。あらゆる国民、民族、国語の人々で、とても数えきれません。彼らは白い衣をまとい、しゅろの枝を手にして、王座と小羊との前に立っていました。 10そして、声を張り上げ、「救いは、王座に座っておられる神と小羊とから来ます」と叫んでいました。 11天使はみな、王座と長老、それに四つの生き物の回りに集まり、ひれ伏して神を礼拝してから、 12こう言いました。「アーメン。祝福と栄光と知恵と感謝と誉れと力と勢いとが、永遠に神にありますように。アーメン。」

13その時、二十四人の長老の一人が、私に尋ねました。「この白い衣の人たちがだれだか、わかりますか。どこから来たか知っていますか。」 14「わかりません。どうか教えてください」と答えると、彼は言いました。「あの人たちは激しい迫害をくぐり抜け、小羊の血で、その衣を洗って白くした人たちです。 15だから、こうして神の王座の前にいて、昼も夜も、神殿で奉仕しているのです。そして、王座に座っておられる方によって、安全にかくまわれています。 16彼らはもう二度と飢えることも、渇くこともありません。灼熱の太陽からも守られています。 17それは、王座の正面に立たれる小羊が、羊飼いとして彼らを養い、いのちの水の泉に導いてくださるからです。また神は、彼らの目からあふれる涙を、すっかりぬぐい取ってくださるのです。」

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 7:1-17

An yi wa 144,000 hatimi

1Bayan wannan, na ga mala’iku huɗu, a tsaye a kusurwoyi huɗu na duniya, suna tsare iskoki huɗu na duniya, domin su hana wani iska hurawa a bisan ƙasa ko a bisan teku ko a bisa wani itace. 2Sai na ga wani mala’ika yana zuwa daga gabas, yana da hatimin Allah mai rai. Ya yi kira da babbar murya wa mala’ikun nan huɗu da aka ba su iko su cuci ƙasa da teku ya ce, 3“Kada ku cuci ƙasa ko teku ko kuma itatuwa sai bayan mun sa hatimi a goshin dukan bayin Allahnmu.” 4Sai na ji yawan waɗanda aka sa musu hatimi. Su 144,000 daga dukan kabilan Isra’ila.

5Daga kabilar Yahuda mutum 12,000 ne aka sa musu hatimin,

daga kabilar Ruben mutum 12,000,

daga kabilar Gad mutum 12,000,

6daga kabilar Asher mutum 12,000,

daga kabilar Naftali mutum 12,000,

daga kabilar Manasse mutum 12,000,

7daga kabilar Simeyon mutum 12,000,

daga kabilar Lawi mutum 12,000,

daga kabilar Issakar mutum 12,000,

8daga kabilar Zebulun mutum 12,000,

daga kabilar Yusuf mutum 12,000,

daga kabilar Benyamin mutum 12,000.

Babban taro sanye da fararen tufafi

9Bayan wannan sai na duba, can a gabana kuwa ga wani taro mai girma, wanda ba mai iya ƙirgawa, daga kowace al’umma, kabila, mutane da kuma harshe, suna tsaye a gaban kursiyin da kuma gaban Ɗan Ragon nan. Suna saye da fararen tufafi suna kuma riƙe da rassan dabino a hannuwansu. 10Suka tā da murya da ƙarfi suna cewa,

“Ceto na Allahnmu ne,

wanda yake zaune a bisan kursiyi,

da kuma na Ɗan Ragon.”

11Dukan mala’iku suna tsaye kewaye da kursiyin da kuma kewaye da dattawan tare da halittu huɗun nan masu rai. Suka fāɗi da fuskokinsu ƙasa a gaban kursiyin suka kuma yi wa Allah sujada, 12suna cewa,

“Amin!

Yabo da ɗaukaka,

da hikima da godiya da girma

da iko da ƙarfi

sun tabbata ga Allahnmu har abada abadin.

Amin!”

13Sai ɗaya daga cikin dattawan ya tambaye ni ya ce, “Waɗannan da suke saye da fararen tufafi su wane ne, daga ina kuma suka fito?”

14Na amsa na ce, “Ranka yă daɗe, kai ka sani.”

Sai ya ce, “Waɗannan su ne waɗanda suka fito daga matsananciyar wahala; sun wanke tufafinsu suka kuma mai da su farare da jinin Ɗan Ragon nan. 15Saboda haka,

“suna a gaban kursiyin Allah

suna masa hidima dare da rana a cikin haikalinsa;

kuma wannan mai zaune a kursiyin zai shimfiɗa tentinsa a bisansu.

16‘Ba za su sāke jin yunwa ba;

ba za su kuma sāke jin ƙishirwa ba.

Rana ba za tă buga su ba,’

ko kuma kowane irin zafin ƙuna.

17Gama Ɗan Ragon da yake a tsakiyar kursiyin zai zama makiyayinsu;

‘zai bi da su zuwa ga maɓulɓular ruwan rai.’

‘Allah kuwa zai share dukan hawaye daga idanunsu.’ ”