מעשי השליחים 25 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

מעשי השליחים 25:1-27

1שלושה ימים לאחר שנכנס פסטוס לתפקידו, עזב את קיסריה ועלה לירושלים. 2ראשי הכוהנים ומנהיגי העם ניגשו אל פסטוס וסיפרו לו את טענותיהם נגד פולוס. 3הם ביקשו ממנו להעלות את פולוס מקיסריה לירושלים ללא דיחוי (כי זממו לארוב לו בדרך ולרצוח אותו).

4אולם פסטוס השיב להם: ”פולוס נמצא עתה בקיסריה, וגם אני עומד לשוב לשם בקרוב. 5אני מציע שתבחרו מספר אנשים בעלי סמכות שילכו איתי לקיסריה, ואם פולוס חטא יוכלו אנשיכם לתבוע אותו למשפט.“

6כעבור שמונה או עשרה ימים חזר המושל לקיסריה, ולמחרת ערך את משפטו של פולוס.

7כשהגיע פולוס לאולם בית־הדין, הקיפו אותו היהודים שבאו מירושלים והטיחו בו האשמות חמורות, אך הם לא יכלו להוכיח אף אחת מהן. 8פולוס כפר בכל ההאשמות. ”אינני אשם“, אמר. ”לא עברתי על חוקי התורה, לא חיללתי את בית־המקדש ולא מרדתי בקיסר!“

9אולם פסטוס, שרצה מאוד למצוא־חן בעיני היהודים, פנה אליו ושאל: ”האם אתה מוכן לעלות לירושלים ולהישפט שם לפני?“

10‏-11”לא!“, השיב פולוס. ”בשום אופן לא. אני עומד בתוקף על זכותי לעמוד לדין לפני כס הקיסר! אתה יודע היטב שאיני אשם. אם ביצעתי פשע שדינו מוות – איני מבקש רחמים או חנינה. אולם אם אני חף מפשע – לאף אחד אין רשות להסגיר אותי לידי אנשים אלה כדי שירצחו אותי. ברצוני לערער לפני הקיסר!“

12פסטוס התייעץ עם יועציו, ואחר כך אמר: ”אתה רוצה לערער לפני הקיסר? יהיה כרצונך!“

13כעבור ימים אחדים באו המלך אגריפס וברניקה לבקר את פסטוס. 14ביקורם נמשך ימים אחדים, ופסטוס שוחח עם המלך על המקרה של פולוס. ”יש כאן אסיר אחד,“ פתח פסטוס, ”שפליקס השאירו בכלא. 15כשהייתי בירושלים סיפרו לי ראשי הכוהנים וזקני היהודים את גרסתם, ודרשו ממני להוציאו להורג. 16כמובן שמיהרתי להבהיר להם שהחוק הרומאי אינו מרשיע אדם לפני שמעמידים אותו לדין, ולפני שניתנה לו האפשרות לעמוד מול מאשימיו ולהגן על עצמו.

17”כשבאו לכאן מאשימיו כינסתי מיד את חברי בית־הדין, ושלחתי להביא את פולוס. 18אולם ההאשמות שהעלו נגדו כלל לא דמו לחשדות שהיו לי לגביו. 19המחלוקת ביניהם הייתה בנושא הדת היהודית, ועל אדם בשם ישוע אשר מת, ואילו פולוס מתעקש לטעון שהוא חי. 20לא ידעתי כיצד להחליט במקרה שכזה, ולכן שאלתי אותו אם יהיה מוכן להישפט על כך בירושלים. 21פולוס סרב, ודרש לערער לפני הקיסר אוגוסטוס! משום כך פקדתי להחזירו לכלא, עד שאוכל לקבוע לו ראיון אצל הקיסר.“

22”הייתי רוצה לשמוע את האיש הזה במו אוזני“, אמר אגריפס. ”בסדר“, ענה פסטוס.

”מחר תשמע אותו.“

23למחרת נכנסו המלך אגריפס וברניקה לאולם בית־הדין ברוב פאר והדר, ובליווי משמר קציני־צבא ואצילי העיר. פסטוס ציווה להכניס את פולוס לתוך האולם, 24ולאחר מכן פנה אל הנוכחים ואמר: ”המלך אגריפס, וכל הנאספים כאן: זהו האיש אשר היהודים בקיסריה ובירושלים רוצים במותו. 25לפי דעתי הוא לא עבר כל עברה שדינה מוות, אולם מאחר שדרש לערער לפני הקיסר, החלטתי לשלוח אותו לרומא. 26אבל מה אכתוב לקיסר? הרי אין נגדו שום טענה מבוססת! על כן הבאתי אותו לפני כולכם, ובמיוחד לפניך, המלך אגריפס, כדי שתחקור אותו ותאמר לי מה לכתוב. 27כי הרי אין זה הגיוני לשלוח אסיר אל הקיסר בלא אשמה כלשהי.“

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 25:1-27

Shari’a a gaban Festus

1Kwana uku bayan isowa a lardin, sai Festus ya haura daga Kaisariya zuwa Urushalima, 2inda manyan firistoci da shugabannin Yahudawa suka bayyana a gabansa suka kuma gabatar da ƙararsu a kan Bulus. 3Suka roƙi Festus a gaggauce a matsayin alfarma gare su, da yă sa a mai da Bulus Urushalima, gama sun ’yan kwanto su kashe shi a hanya. 4Festus ya amsa ya ce, “Bulus yana tsare a Kaisariya, ni da kaina kuma zan je can ba da daɗewa ba. 5Ku sa waɗansu daga cikin shugabanninku su tafi tare da ni su kawo ƙararsu a kan mutumin a can, in ya aikata wani laifi.”

6Bayan ya yi kwanaki takwas ko goma tare da su, sai ya gangara zuwa Kaisariya, kashegari kuma ya kira a yi zaman kotu ya kuma umarta a kawo Bulus a gabansa. 7Da Bulus ya bayyana, sai Yahudawan da suka gangaro daga Urushalima suka tsaya kewaye shi, suna kawo ƙarar masu tsanani da yawa a kansa, waɗanda ba su iya tabbatarwa ba.

8Sa’an nan Bulus ya kāre kansa ya ce, “Ban aikata wani laifi game da dokokin Yahudawa ko game da haikali ko kuma game da Kaisar ba.”

9Festus, da yake yana so yă yi wa Yahudawa alfarma, sai ya ce wa Bulus, “Ka yarda ka je Urushalima a yi maka shari’a a can a gabana a kan waɗannan zarge?”

10Bulus ya amsa ya ce, “Yanzu ina tsaye a gaban kotun Kaisar, inda ya kamata a yi mini shari’a. Ban yi wani laifi ga Yahudawa ba, kai da kanka ma ka san da haka sarai. 11In kuwa ina da wani laifin da ya isa kisa, ban ƙi in mutu ba. Amma in ƙarar da waɗannan Yahudawa suka kawo a kaina ba gaskiya ba ne, ba wanda yake da iko ya ba da ni a gare su. Na ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar!”

12Bayan Festus ya yi shawara da majalisarsa sai ya ce, “Ka ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar. To, ga Kaisar kuwa za ka tafi!”

Festus ya nemi shawarar Sarki Agiriffa

13Bayan ’yan kwanaki sai Sarki Agiriffa da Bernis suka iso Kaisariya don su yi wa Festus gaisuwar bangirma. 14Da yake za su yi kwanaki da dama a can, sai Festus ya tattauna batun Bulus da sarki. Ya ce, “Akwai mutumin da Felis ya bari a daure. 15Sa’ad da na je Urushalima, manyan firistoci da dattawan Yahudawa suka kawo ƙara game da shi suka kuma nema a hukunta shi.

16“Na gaya musu cewa ba al’adar Romawa ba ce a hukunta mutum kafin ya fuskanci masu ƙararsa ya kuma sami damar kāre kansa game da ƙararsu. 17Da suka zo nan tare da ni, ban yi wani jinkiri ba, na kira zaman kotu kashegari kuma na umarta a kawo mutumin. 18Sa’ad da masu zarginsa suka tashi tsaye don su yi magana, ba su zarge shi da wani laifin da na yi tsammani ba. 19A maimako haka, sai suka kawo waɗansu ’yan maganganu game da addininsu da ba su yarda da shi ba da kuma game da wani Yesu da ya mutu wanda Bulus ya ce yana da rai. 20Na rasa yadda zan bincike irin abubuwan nan; saboda haka na yi tambaya ko zai yarda ya tafi Urushalima a yi masa shari’a a can game da waɗannan zargi. 21Da Bulus ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Babban Sarki sai na umarta a tsare shi har kafin in aika shi zuwa ga Kaisar.”

22Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Ni ma zan so in saurari mutumin da kaina.”

Sai ya amsa ya ce, “Za ka kuwa ji shi gobe.”

Bulus a gaban Agiriffa

23Kashegari Agiriffa da Bernis suka yi shiga irin ta sarauta suka shiga ɗakin jama’a tare da manyan sojoji da manyan mutanen birni. Da umarnin Festus, sai aka shigo da Bulus. 24Sai Festus ya ce, “Sarki Agiriffa, da kuma dukan waɗanda suke tare da mu, kun ga wannan mutum! Dukan jama’ar Yahudawa sun kawo mini kararsa a Urushalima da kuma a nan Kaisariya, suna kururuwa suna cewa bai kamata a bar shi da rai ba. 25Ban same shi da wani laifin da ya isa kisa ba, amma saboda ya ɗaukaka ƙararsa zuwa gaban Babban Sarki sai na yanke shawara in aika da shi Roma. 26Ba ni da wata tabbatacciyar maganar da zan rubuta wa Mai Girma game da shi. Saboda haka na kawo shi a gabanku duka, musamman a gabanka, Sarki Agiriffa, saboda a sakamakon wannan bincike zan iya samun abin da zan rubuta. 27Don a ganina wauta ce a aika da ɗan kurkuku ba tare da an nuna zargin da ake yi a kansa ba.”