מעשי השליחים 2 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

מעשי השליחים 2:1-47

1שבעה שבועות חלפו מאז מותו של ישוע ותחייתו מן המתים, ויום חג השבועות הגיע. כשהתאספו המאמינים יחד באותו יום, 2נשמע לפתע קול סערה גדולה מן השמים, והרעש מילא את הבית שבו ישבו. 3הנוכחים ראו מעין לשונות אש קטנות יורדות ונחות על ראשיהם, 4וכל אחד מהם נמלא ברוח הקודש והחל לדבר בשפה שלא הייתה מוכרת לו, כי רוח הקודש העניק להם יכולת זאת.

5הרבה יהודים אדוקים מארצות שונות עלו לירושלים לרגל החג, 6ובשמעם את רעש הסערה מעל הבית ההוא, מיהרו אל המקום כדי לראות מה קרה. לתדהמתם הרבה כל אחד שמע את התלמידים מדברים בשפה שלו.

7”כיצד ייתכן הדבר?“ שאלו עולי־הרגל. ”הלא כל האנשים האלה גרים בגליל! 8כיצד הם יכולים לדבר בשפות המדוברות בארצות מולדתנו? 9הרי אנחנו פרתיים, מדיים, עילמיים, אנשי ארם־נהריים, יהודה, קפודקיה, פונטוס, אסיה הקטנה; 10פריגיה, פמפוליה, מצרים; יש בינינו אנשים מהאזורים שליד קוריניה שבלוב, ומרומא; 11יהודים וגרים, כרתים וערבים – וכל אחד מאיתנו שומע בשפתו כיצד אנשים אלה מספרים על מעשיו של אלוהים ועל נפלאותיו!“

12כולם עמדו שם נבוכים ומבולבלים. ”מה פירושו של הדבר?“ שאלו זה את זה.

13אולם בקרב הקהל היו גם כאלה שלעגו: ”הם סתם שיכורים!“

14שמעון פטרוס צעד קדימה, יחד עם אחד־עשר השליחים, ופנה אל ההמון: ”תושבי ירושלים ואורחיה, הקשיבו היטב לדברי. 15אחדים מכם טוענים שאנשים אלה שיכורים, אבל דעו לכם שהם אינם שיכורים! בני־אדם אינם נוהגים להשתכר בשעה תשע בבוקר! 16מה שאתם רואים כאן הבוקר כבר נובא לפני שנים רבות בפי יואל הנביא, אשר אמר:2‏.16 ב 16 יואל ג

17’והיה אחרי כן (באחרית הימים), אמר אלוהים,

אשפוך את רוחי על כל בשר.

ונבאו בניכם ובנותיכם,

זקניכם חלמות יחלמון,

בחוריכם חזינות יראו.

18וגם על העבדים ועל השפחות

בימים ההמה אשפוך את רוחי.

19ונתתי מופתים בשמים ובארץ –

דם ואש ותימרות עשן.

20השמש יהפך לחשך,

והירח – לדם, לפני בוא יום ה׳ הגדול והנורא.

21והיה כל אשר יקרא בשם ה׳ ימלט!‘

22”אנשי ישראל, הקשיבו!“ המשיך פטרוס. ”אלוהים אישר בפומבי שישוע המשיח אכן שליח משמים, באמצעות הניסים והנפלאות שחולל על־ידו, ואתם יודעים זאת היטב, שהרי הניסים והנפלאות נעשו אצלכם. 23אולם אלוהים, שפעל לפי תוכניתו הערוכה מראש, הרשה לכם להסגיר את ישוע לידי הרומאים, כדי שיוקיעו אותו ויהרגוהו. 24ואז אלוהים שחרר אותו מייסורי המוות והחזירו לחיים, כי המוות לא יכול היה להחזיק בו!

25”דוד המלך דיבר על ישוע כשאמר:2‏.25 ב 25 תהלים טז 8‏-11

’שויתי ה׳ לנגדי תמיד, כי מימיני בל אמוט.

26לכן שמח לבי ויגל כבודי,

אף בשרי ישכן לבטח,

27כי לא תעזב נפשי לשאול;

לא תתן חסידך לראות שחת.

28תודיעני ארחות חיים, שבע שמחות את פניך‘.

29”אחים יקרים, חשבו נא! הרי דוד לא התכוון לעצמו כשאמר את הדברים שציטטתי זה עתה, שהרי הוא מת ונקבר, וקברו נמצא בעירנו עד היום הזה. 30אולם דוד היה נביא, ועל כן ידע היטב שה׳ הבטיח, בשבועה נצחית, שאחד מצאצאיו יהיה המשיח ויישב על כסאו. 31דוד חזה את העתיד הרחוק וניבא את תחייתו של המשיח, באמרו שנפש המשיח לא תישאר בשאול, ושגופו לא יירקב. 32הוא דיבר על המשיח, וכולנו עדים לכך שישוע זה, שעליו אנו מדברים, באמת קם מן המתים.

33”עתה יושב ישוע בשמים לימין האלוהים, וכפי שהובטח העניק לו אלוהים את הסמכות לשלוח את רוח הקודש, אשר גרם לכל מה שאתם רואים ושומעים היום.

34”לא, דוד לא התייחס אל עצמו בדברים שאמר, שהרי הוא מעולם לא עלה לשמים. מלבד זאת, דוד הוסיף ואמר במקום אחר:2‏.34 ב 34 תהלים קי 1

’נאם ה׳ לאדני, שב לימיני,

35עד אשית אויביך

הדם לרגליך‘.

36”משום כך אני קורא אל בית ישראל: דעו לכם שאלוהים הפקיד את ישוע, אשר צלבתם, להיות האדון והמשיח!“

37דבריו של פטרוס נגעו ללב השומעים, והם פנו אליו ואל השליחים האחרים בשאלה: ”אחים, מה עלינו לעשות?“

38”עליכם לחזור בתשובה ולהיטבל בשם ישוע המשיח, כדי שייסלחו לכם חטאיכם“, השיב פטרוס. ”ואז תקבלו את מתנת רוח הקודש. 39כי ה׳ הבטיח לתת את רוח הקודש לכל מי שיקרא בשם ה׳ אלוהינו, וגם לבניו – לרחוקים ולקרובים.“

40פטרוס המשיך לספר להם על ישוע, והפציר בכל מאזיניו לחזור בתשובה ולהינצל מהדור הסורר הזה. 41כשלושת אלפים איש האמינו באותו יום לדבריו של פטרוס ונטבלו במים. 42הם הצטרפו אל יתר המאמינים, והשתתפו בקביעות בשיעוריהם של השליחים, בבציעת הלחם (כמצוות ישוע לזיכרון מותו) ובאסיפות תפילה. 43הניסים והנפלאות הרבים שחוללו השליחים מלאו את כולם יראת־כבוד לאלוהים.

44כל המאמינים התמידו להתאסף יחד, וחילקו ביניהם את כל מה שהיה להם. 45הם מכרו את כל רכושם, והתחלקו בכספם עם הנצרכים. 46מדי יום הם השתחוו יחד בבית־המקדש, נפגשו בבתיהם בקבוצות, לשם התחברות, ואכלו יחד את ארוחותיהם בשמחה ובהכרת־תודה. 47הם הללו את אלוהים, והם מצאו־חן בעיני כל העם. מדי יום הוסיף להם ה׳ את אלה שנושעו.

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 2:1-47

Ruhu Mai Tsarki ya zo a Fentekos

1Da ranar Fentekos ta yi, dukansu suna tare wuri ɗaya. 2Ba zato ba tsammani sai aka ji motsi kamar ta babbar iska tana hurowa daga sama ta kuma cika dukan gidan da suke zaune. 3Suka ga wani abin da ya yi kama da harsunan wuta, suka rarrabu suna kuma sassauka a kan kowannensu. 4Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka kuma fara magana da waɗansu harsuna yadda Ruhu ya sa suka iya.

5To, a Urushalima akwai Yahudawa masu tsoron Allah, daga kowace ƙasa a duniya. 6Da suka ji wannan motsi, taro ya haɗu wuri ɗaya a ruɗe, domin kowannensu ya ji suna magana da yarensa. 7Cike da mamaki, suka yi tambaya suna cewa, “Ashe, duk waɗannan mutane masu magana ba Galiliyawa ba ne? 8To, yaya kowannenmu yana ji suna yarensa? 9Fartiyawa, Medes da Elamawa; mazaunan Mesofotamiya, Yahudiya da Kaffadokiya, Fontus da Asiya, 10Firjiya da Famfiliya, Masar da sassa Libiya kusa da Sairin; baƙi daga Roma 11(Yahudawa da kuma waɗanda suka tuba suka shiga Yahudanci); Kiretawa da Larabawa, mun ji su suna shelar abubuwan banmamaki na Allah da yarenmu!” 12A ruɗe kuma cike da mamaki, suka tambayi junansu cewa, “Mene ne wannan yake nufi?”

13Duk da haka waɗansu suka yi musu ba’a suka ce, “Sun yi tatil da ruwan inabi ne.”

Bitrus ya yi wa taron jawabi

14Sai Bitrus ya miƙe tsaye tare da Sha Ɗayan nan, ya ɗaga muryarsa ya yi wa taron jawabi ya ce, “’Yan’uwana Yahudawa da dukanku da kuke zama cikin Urushalima, bari in bayyana muku wannan, ku saurara da kyau ga abin da zan faɗa. 15Waɗannan mutane ba su bugu ba, kamar yadda kuka ɗauka. Yanzu ƙarfe tara na safe ne kawai! 16A’a, ai, abin da aka yi magana ta bakin annabi Yowel ke nan cewa,

17“Allah ya ce, ‘A kwanakin ƙarshe,

zan zubo Ruhuna bisa dukan mutane.

’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci,

samarinku za su ga wahayoyi,

dattawanku kuma za su yi mafarkai.

18Kai, har ma a kan bayina, maza da mata,

zan zubo Ruhuna a waɗancan kwanaki,

za su kuwa yi annabci.

19Zan nuna abubuwan banmamaki a sararin sama

da alamu a nan ƙasa,

jini da wuta da kuma hauhawan hayaƙi.

20Za a mai da rana duhu,

wata kuma ya zama jini,

kafin zuwa rana mai girma da kuma ta ɗaukaka ta Ubangiji.

21Kuma duk wanda ya kira

bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.’2.21 Yow 2.28-32

22“Mutanen Isra’ila, ku saurari wannan. Yesu Banazare shi ne mutumin da Allah ya tabbatar muku ta wurin mu’ujizai, ayyukan banmamaki, da kuma alamu, waɗanda Allah ya yi a cikinku ta wurinsa, kamar yadda ku kanku kuka sani. 23An ba da wannan mutum gare ku bisa ga nufin Allah da kuma rigyasaninsa, ku kuma tare da taimakon mugayen mutane, kuka kashe shi ta wurin kafa shi a kan gicciye. 24Amma Allah ya tashe shi daga matattu, ya ’yantar da shi daga azabar mutuwa, don ba ya yiwuwa mutuwa ta riƙe shi. 25Dawuda ya yi faɗi game da shi cewa,

“ ‘Kullum ina ganin Ubangiji a gabana.

Gama yana a hannuna na dama,

ba zan jijjigu ba.

26Saboda haka, zuciyata na farin ciki, harshena kuma na murna,

jikina kuma zai kasance da bege,

27gama ba za ka bar ni cikin kabari ba,

ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka yă ruɓa ba.

28Ka sanar da ni hanyoyin rai,

za ka cika ni da farin ciki a gabanka.’2.28 Zab 16.8-11

29“’Yan’uwa, zan iya tabbatar muku gabagadi cewa kakanmu Dawuda ya mutu aka kuma binne shi, kabarinsa kuwa yana a nan har yă zuwa yau. 30Amma shi annabi ne ya kuma san abin da Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa zai ɗora ɗaya daga cikin zuriyarsa a kan gadon sarautarsa. 31Ganin abin da yake gaba, ya yi magana a kan tashin Kiristi daga matattu cewa, ba a bar shi a kabari ba, jikinsa kuma bai ruɓa ba. 32Allah ya tashe wannan Yesu zuwa rai, mu kuwa duk shaidu ne ga wannan. 33An ɗaukaka shi zuwa ga hannun dama na Allah, ya karɓi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga Uba, ya kuma zubo abin da yanzu kuke gani kuke kuma ji. 34Gama Dawuda bai hau zuwa sama ba, duk da haka ya ce,

“ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,

“Zauna a hannun damana,

35sai na sa abokan gābanka

su zama matashin sawunka.” ’2.35 Zab 110.1

36“Saboda haka bari dukan Isra’ila su tabbatar da wannan. Allah ya mai da wannan Yesu, da kuka gicciye, Ubangiji da kuma Kiristi.”

37Sa’ad da mutane suka ji wannan, sai suka soku a zuci sai suka ce wa Bitrus da sauran manzanni, “’Yan’uwa, me za mu yi?”

38Bitrus ya amsa, “Ku tuba a kuma yi muku baftisma, kowannenku a cikin sunan Yesu Kiristi domin gafarar zunubanku. Za ku kuwa karɓi kyautar Ruhu Mai Tsarki. 39Alkawarin dominku ne da ’ya’yanku da kuma dukan waɗanda suke da nesa, domin dukan waɗanda Ubangiji Allahnmu zai kira.”

40Da waɗansu kalmomi masu yawa ya gargaɗe su; ya kuma roƙe su cewa, “Ku ceci kanku daga wannan lalataccen zamani.” 41Waɗanda suka yarda da saƙonsa kuwa aka yi musu baftisma, a ranar kuwa yawansu ya ƙaru da mutum kusan dubu uku.

Zumuncin masu bi

42Suka ba da kansu ga koyarwar manzanni da kuma ga zumunci, ga gutsuttsura burodin da kuma ga addu’a. 43Kowa ya cika da tsoro, manzannin kuwa suka aikata abubuwan banmamaki da alamu masu yawa. 44Dukan masu bi suna tare, suna kuma mallakar kome tare. 45Suka dinga sayar da ƙaddarorinsu da kayayyakinsu, suka ba wa kowa gwargwadon bukatarsa. 46Kowace rana suka ci gaba da taruwa a filin haikali. Suka gutsuttsura burodi a gidajensu suna cin abinci tare da farin ciki da zuciya ɗaya, 47suna yabon Allah suna kuma samun tagomashin dukan mutane. Ubangiji kuwa ya ƙara yawansu kowace rana na waɗanda suke samun ceto.