הבשורה על-פי מרקוס 8 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי מרקוס 8:1-38

1יום אחד כשהתאסף קהל גדול סביב ישוע, שוב לא היה להם מה לאכול. ישוע כינס את תלמידיו כדי לדון במצב.

2”אני מרחם על האנשים האלה“, אמר. ”הם נמצאים כאן כבר שלושה ימים, ונגמר להם האוכל. 3אם אשלח אותם הביתה רעבים, הם יתעלפו בדרך, מפני שחלקם באו ממקומות רחוקים.“

4”מאין נמצא להם אוכל במקום השומם הזה?“ שאלו התלמידים בפליאה.

5”כמה ככרות לחם יש לכם?“ שאל אותם ישוע. ”שבע“, השיבו. 6ישוע ביקש מהקהל לשבת על הארץ. הוא לקח את שבע ככרות הלחם, הודה לאלוהים עליהן, פרס את הלחם לפרוסות ונתן לתלמידיו כדי שיגישו לקהל. 7הם מצאו גם כמה דגים קטנים. ישוע ברך עליהם וביקש מתלמידיו להגישם לקהל. 8‏-9למרבה הפלא אכלו כולם עד ששבעו, ולאחר מכן שלח אותם ישוע הביתה. כארבעת־אלפים איש השתתפו בארוחה באותו יום, וכשאספו את השאריות והפירורים הם מילאו שבעה סלים גדולים!

10מיד לאחר מכן עלו ישוע ותלמידיו לסירה ושטו לאזור דלמנותא. 11הפרושים בדלמנותא שמעו על בואו, ובאו להתווכח איתו ולנסותו. הם אמרו לישוע: ”הראה לנו אות מהשמים, ואז נאמין בך.“

12ישוע נאנח אנחה עמוקה והשיב: ”לא אחולל למענכם כל פלא ולא אראה לכם כל אות מהשמים. כמה הוכחות דרושות לכם כדי שתאמינו?“

13ישוע עזב אותם, חזר לסירה ושט לגדה השנייה של הכינרת. 14התלמידים שכחו לקחת איתם מספיק אוכל, ונותרה להם בסירה רק כיכר לחם אחת.

15בהיותם בסירה הזהיר ישוע את תלמידיו בתקיפות: ”היזהרו מהשאור של המלך הורדוס ושל הפרושים!“

16”למה הוא מתכוון?“ שאלו התלמידים זה את זה. לבסוף הגיעו למסקנה שהוא ודאי מדבר על כך ששכחו לקחת איתם מספיק לחם.

17ישוע הקשיב לשיחתם והגיב: ”אתם טועים לגמרי. איני מדבר כלל על הלחם שבסירה. האם קשה לכם כל־כך להבין זאת? 18למה אתם לא רואים, למה אתם לא שומעים? למה אתם לא קולטים דבר?

19”האם שכחתם את חמשת־אלפים האנשים שהאכלתי בחמש כיכרות לחם? אמרו לי, כמה לחם נותר לאחר הארוחה?“

”שנים־עשר סלים מלאים“, ענו התלמידים.

20”וכאשר האכלתי את ארבעת־אלפים האנשים בשבע ככרות לחם, כמה נותר בסוף?“

”שבעה סלים מלאים“, השיבו התלמידים.

21”ואתם עוד מעזים לחשוב שאני דואג משום שיש לנו רק כיכר לחם אחת?“

22בהגיעם לבית־צידה הביאו אליו מספר אנשים אדם עיוור, והתחננו לפניו שיגע בו וישיב לו את ראייתו. 23ישוע אחז ביד העיוור והוציאו אל מחוץ לכפר, שם ירק בעיניו והניח עליהן את ידיו.

”האם אתה רואה עכשיו?“ שאל ישוע.

24האיש הביט סביבו והשיב: ”כן! אני רואה אנשים; אבל הם נראים מטושטשים – כמו עצים מהלכים!“

25ישוע הניח שוב את ידיו על עיני האיש, והן נרפאו כליל. עתה יכול היה האיש לראות למרחוק בבירור.

26ישוע שלח אותו הביתה אל משפחתו ואמר: ”אל תלך לספר את הדבר לאנשי הכפר; לך ישר הביתה.“

27ישוע ותלמידיו עזבו את הגליל והלכו לכפרי קיסריה של פיליפוס. בדרך שאל ישוע את תלמידיו: ”מה אומרים עלי אנשים? למי הם חושבים אותי?“

28”יש אנשים שחושבים שאתה יוחנן המטביל,“ ענו התלמידים, ”ואחרים חושבים שאתה אליהו הנביא או נביא אחר.“

29”ומי אתם חושבים שאני?“ המשיך ישוע לשאול.

”אתה המשיח!“ קרא פטרוס. 30אולם ישוע הזהיר אותם שלא יגלו זאת לאיש.

31רק מאז החל ישוע לספר להם על הייסורים המצפים לו, והוא עוד סיפר שראשי הכוהנים, הסופרים והזקנים יגרמו למותו, אך יקום לתחייה לאחר שלושה ימים. 32ישוע דיבר אתם בגלוי לב, אולם פטרוס לקח אותו הצידה והוכיח אותו: ”אל תדבר כך!“

33ישוע הביט בפטרוס ואמר לו בחומרה: ”סור ממני, שטן שכמוך! אתה מסתכל על הדברים מנקודת ראות אנושית, ולא מנקודת ראותו של אלוהים.“

34ישוע ביקש מתלמידיו להתקרב אליו ולהקשיב. ”מי שרוצה ללכת בעקבותיי עליו להתכחש לעצמו, לשאת את צלבו וללכת אחרי. 35מי שחפץ להציל את חייו – יאבד אותם, ואילו מי שיוותר על חייו למעני ולמען הבשורה – יציל אותם.

36”איזה רווח יש לאדם שיכול להשיג את כל העולם אבל מפסיד חיי־נצח? 37מה כבר יכול בן־אדם לתת בתמורה לחייו? 38דעו לכם, שכל מי שמתבייש בי ובדברי בדור החוטא וחסר האמונה הזה, הוא יהיה לבושה לבן־האדם כאשר יבוא בכבודו עם המלאכים הקדושים.“

Hausa Contemporary Bible

Markus 8:1-38

Yesu ya ciyar da dubu huɗu

(Mattiyu 15.32-39)

1A kwanakin nan wani taro mai girma ya taru. Tun da yake ba su da abin da za su ci, sai Yesu ya kira almajiransa ya ce, 2“Ina jin tausayin mutanen nan, kwanansu uku ke nan tare da ni, kuma ba su da abin da za su ci. 3In na sallame su gida da yunwa, za su kāsa a hanya, don waɗansu daga cikinsu sun zo daga nesa.”

4Almajiransa suka amsa suka ce, “Amma a ina, a wannan wurin da ba kowa, wani zai iya samun isashen burodi, don a ciyar da su?”

5Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Burodi guda nawa kuke da su?”

Suka ce, “Bakwai.”

6Sai ya gaya wa taron su zazzauna a ƙasa. Bayan ya ɗauki burodin nan bakwai, ya yi godiya, sai ya kakkarya, ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutanen, suka kuwa yi haka. 7Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan, ya ba da godiya dominsu, ya kuma ce wa almajiran su rarraba musu. 8Mutanen suka ci, suka ƙoshi. Daga baya, almajiran suka tattara gutsattsarin da suka rage cike da kwanduna bakwai. 9Wajen maza dubu huɗu ne suka kasance. Da ya sallame su, 10sai ya shiga jirgin ruwa tare da almajiransa, suka tafi yankin Dalmanuta.

(Mattiyu 16.1-4)

11Farisiyawa suka zo suka fara yin wa Yesu tambayoyi. Don su gwada shi, sai suka nemi yă nuna musu wata alama daga sama. 12Sai ya ja numfashi mai zurfi ya ce, “Don me wannan zamani yake neman ganin abin banmamaki? Gaskiya nake gaya muku, ba wata alamar da za a ba su.” 13Sai ya bar su, ya koma cikin jirgin ruwan, suka ƙetare zuwa ɗaya hayin.

Yistin Farisiyawa da na Hiridus

(Mattiyu 16.5-12)

14Almajiran suka manta su riƙe burodi, sai dai guda ɗaya da suke da shi a cikin jirgin ruwan. 15Yesu ya gargaɗe su ya ce, “Ku yi hankali, ku kuma lura da yistin Farisiyawa da na Hiridus.”

16Suka tattauna wannan da juna, suna cewa, “Don ba mu da burodi ne.”

17Da ya gane abin da suke tattaunawa, sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Don me kuke zancen rashin burodi? Har yanzu ba ku gane ko fahimta ba? Zukatanku sun taurare ne? 18Kuna da idanu, amma kun kāsa gani, kuna da kunnuwa, amma kun kāsa ji? Ba ku tuna ba? 19Da na kakkarya burodi guda biyar wa mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?”

Suka amsa, “Sha biyu.”

20“Da na kuma kakkarya burodin nan bakwai wa mutum dubu huɗu, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?”

Suka ce, “Bakwai.”

21Ya ce musu, “Har yanzu ba ku fahimta ba?”

An warkar da makaho

22Suka iso Betsaida, sai waɗansu mutane suka kawo wani makaho, suka roƙi Yesu yă taɓa shi. 23Yesu ya kama hannun makahon ya kai shi bayan ƙauyen. Bayan ya tofa miyau a idanun mutumin, ya kuma ɗibiya masa hannuwansa, sai ya tambaye shi ya ce, “Kana iya ganin wani abu?”

24Sai ya ɗaga kai ya ce, “Ina ganin mutane, suna kama da itatuwa da suke tafiya.”

25Yesu ya sāke ɗibiya hannuwansa a idanun mutumin, sai idanunsa suka buɗe, ya sami gani, ya kuma ga kome sarai. 26Yesu ya sallame shi gida ya ce, “Kada ka shiga cikin ƙauyen.”8.26 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da Kada ka faɗa wa kowa a ƙauyen

Shaidar Bitrus a kan Kiristi

(Mattiyu 16.13-20; Luka 9.18-21)

27Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan da suke kewaye da Kaisariya Filibbi. A hanya ya tambaye su ya ce, “Wa, mutane suke ce da ni?”

28Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu Iliya, waɗansu kuma har wa yau sun ce, ɗaya daga cikin annabawa.”

29Sai ya yi tambaya ya ce, “Amma ku fa, wa kuke ce da ni?”

Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi.8.29 Ko kuwa Almasihu “Kiristi” (da Girik) “Almasihu” kuma (da Ibraniyanci) duk suna nufin “Shafaffen nan.”

30Yesu ya gargaɗe su kada su gaya wa kowa kome a kansa.

Yesu ya yi zancen mutuwarsa

(Mattiyu 16.21-28; Luka 9.22-27)

31Sai ya fara koya musu cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahaloli da yawa, dattawa, manyan firistoci da malaman dokoki kuma su ƙi shi. Dole kuma a kashe shi, bayan kwana uku kuma, yă tashi. 32Ya yi wannan zance a sarari. Sai Bitrus ya jawo shi gefe, ya fara tsawata masa.

33Amma da Yesu ya juya ya dubi almajiransa, sai ya tsawata wa Bitrus ya ce, “Tashi daga nan Shaiɗan! Ba ka da al’amuran Allah a zuciyarka, sai na mutane.”

34Sai ya kira taron wurinsa tare da almajiransa ya ce, “Duk wanda zai bi ni, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa yă bi ni. 35Domin duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, da kuma bishara, zai same shi. 36Me mutum zai amfana, in ya ribato duniya duka a bakin ransa? 37Ko kuma, me mutum zai bayar a musayar ransa? 38Duk wanda ya ji kunyata, da na kalmomina a wannan zamani na fasikanci da zunubi, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa lokacin da ya shiga cikin ɗaukakar Ubansa, tare da tsarkakan mala’iku.”