הבשורה על-פי יוחנן 5 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי יוחנן 5:1-47

1כעבור זמן מה חזר ישוע לירושלים לרגל אחד החגים. 2ליד שער הצאן בירושלים הייתה ברכה שנקראת בעברית5‏.2 ה 2 בארץ ישראל בתקופה הזו היהודים דיברו בעברית ובארמית. כאשר מופיע תעתיק ביוונית המקורית בברית החדשה, מלבד מקרים בודדים (התגלות ט 11, טז 16), הציטוט מובא בארמית ולא בעברית (גם כאשר כתוב שזה עברית). עובדה זו מומחשת במעשי השליחים א 19: ”הדבר הזה נודע לכל יושבי ירושלים ולפיכך נקרא אותו שדה בלשונם ’חקל דמא‘, שפירושו שדה הדם“. ”בית־חסדא“, וסביבה חמישה רציפים. 3על רציפים אלה שכבו חולים רבים, עיוורים, פיסחים, משותקים וכדומה (כשהם מחכים שהמים יסערו, 4כי מדי פעם ירד מלאך ה׳ אל הברכה והסעיר את המים, והחולה הראשון שנכנס אל המים לאחר מכן נרפא). 5בין החולים הרבים היה אדם שסבל ממחלתו במשך שלושים ושמונה שנים. 6ישוע הביט באיש ומיד ידע את משך מחלתו. ”אתה רוצה להירפא?“ שאל ישוע.

7”איני יכול!“ השיב האיש בייאוש. ”אין מי שיעזור לי להיכנס למים בעת הסערה, ובזמן שאני מנסה להיכנס לברכה בכוחות עצמי, מישהו זריז ממני מקדים אותי ונכנס למים לפני.“

8”קום, קפל את האלונקה שלך והתהלך!“ פקד ישוע. 9האיש נרפא מיד, עמד על רגליו, קיפל את האלונקה והלך לדרכו. מאחר שהמעשה התרחש בשבת, 10לא מצא הדבר חן בעיני היהודים.5‏.10 ה 10 בברית החדשה כאשר משתמשים במונח ”היהודים“, לעתים הכוונה לכלל העם היהודי או לתושבי ירושלים והאזור, הרשויות היהודיות בירושלים, או למתנגדיו של ישוע. כאן, כמו ברוב המקרים בספר זה, הכוונה לרשויות של היהודים בירושלים. ”אסור לך לשאת את האלונקה, כי שבת היום!“ קראו לעבר הנרפא.

11”האיש שריפא אותי פקד עלי לקפל את האלונקה וללכת“, ענה האיש.

12”מיהו האיש הזה?“ שאלו.

13אך הנרפא לא יכול היה להשיב להם, כי הוא בעצמו לא ידע מי הוא כי בינתיים נעלם ישוע בקהל הרב שהיה במקום.

14מאוחר יותר פגש ישוע את הנרפא בבית־המקדש ואמר לו: ”עתה, לאחר שהבראת, אל תמשיך לחטוא, פן יבוא עליך משהו יותר רע.“ 15האיש הלך מהר וסיפר ליהודים כי ישוע הוא זה שריפא אותו. 16ואז החלו מנהיגי היהודים לרדוף את ישוע, מפני שחילל את השבת. 17אבל ישוע אמר להם: ”אבי לא הפסיק לעבוד עד עתה, ואני נוהג כמוהו!“

18דבריו עוררו עוד יותר את חמת מנהיגי היהודים, והם רצו להרגו לא רק על שום שחילל את השבת, אלא גם על שקרא לאלוהים ”אביו“, ובכך השווה את עצמו לאלוהים.

19”הבן אינו יכול לעשות דבר בעצמו,“ אמר ישוע, ”הוא עושה רק מה שראה את אביו עושה, ובאותה דרך. 20כי האב אוהב את בנו ומלמד אותו את כל מעשיו, ואפילו מלמדו לעשות מעשים גדולים יותר מריפוי האיש הזה. אתם יודעים מדוע? כדי שתתפלאו ותשתוממו! 21הבן אף יקים מהמתים את מי שירצה, ממש כפי שעושה האב. 22האב לא ישפוט איש – הוא נתן לבנו את סמכות המשפט, כדי שכולם יכבדו את הבן כפי שהם מכבדים את האב. 23מי שאינו מכבד את הבן אינו מכבד גם את האב אשר שלח אותו.

24”אני מבטיח לכם שכל השומע את דברי ומאמין באלוהים אשר שלח אותי, יחיה חיי נצח ולא יישפט על חטאיו לעולם, משום שהוא כבר עבר מהמוות לחיים. 25אני מבטיח לכם, יגיע הזמן, ולמעשה הוא כבר הגיע, שהמתים ישמעו את קולו של בן־האלוהים – וכל השומעים יחיו. 26כשם שלאב עצמו יש כוח המעניק חיים, כך גם לבן יש אותו כוח, שהוא מתנת האב. 27כבן־האדם יש לו זכות וסמכות לשפוט את חטאיהם של כל בני־האדם. 28אל תתפלאו על כך, כי יבוא הזמן שכל המתים ישמעו בקבריהם את קולו של בן האלוהים, 29והם יקומו מקבריהם – עושי הטוב לחיי נצח, ועושי הרע למשפט.

30”איני שופט איש לפני התייעצות עם אבי; אני שופט רק לפי מה שהוא אומר לי. משפטי ישר וצודק, כי איני מבקש את טובת עצמי, אלא את רצון אבי שבשמים אשר שלחני.

31”אם אני מעיד על עצמי, תאמרו שעדותי אינה מהימנה. 32אולם מישהו אחר מעיד עלי – יוחנן המטביל, ואני יודע שאפשר לסמוך על דבריו. 33אתם שלחתם את אנשיכם אל יוחנן כדי להקשיב לדבריו, ויוחנן אמר את האמת. 34אל תחשבו שאני זקוק לעדות בני־אדם; אני מספר לכם כל זאת רק כדי שתאמינו ותיוושעו.

35”יוחנן הפיץ אור כנר דולק כדי להאיר לכם את הדרך, ולזמן קצר אף שמחתם להתענג על האור הזה. 36ברם יש לי עדות גדולה יותר מעדותו של יוחנן: המעשים שאני עושה. אלוהים אבי הטיל עלי לעשות את המעשים האלה, והם מוכיחים שהוא שלח אותי. 37האב עצמו מעיד עלי, למרות שמעולם לא שמעתם את קולו, ואת מראהו לא ראיתם. 38אולם דברו אינו שוכן בכם כלל, כי אתם מסרבים להאמין שאני שליחו.

39”אתם דורשים בכתובים מתוך תקווה למצוא בהם חיי נצח, אך הכתובים מצביעים עלי! 40למרות זאת אינכם רוצים לבוא אלי כדי שאעניק לכם חיי נצח.

41”איני לוקח כבוד ושבחים מבני־אדם ואיני דואג לדעתכם עלי, 42אבל אני רוצה לומר לכם שאינכם אוהבים את אלוהים. 43אני באתי בשם אבי ולא קיבלתם אותי; אך אם יבוא מישהו אחר בשם עצמו, כן תקבלו אותו. 44אין פלא שאינכם מאמינים, שכן אתם מבקשים כבוד איש מרעהו, וכלל אינכם דואגים לכבוד שחולק אלוהים.

45”אל תחשבו שאטען עליכם לפני אבי. משה רבנו – שבו אתם מאמינים – הוא הטוען עליכם! 46אילו האמנתם למשה הייתם מאמינים גם לי, שהרי הוא כתב עלי. 47ואם אינכם מאמינים למה שכתב משה, איני מתפלא שאינכם מאמינים לדברי.“

Hausa Contemporary Bible

Yohanna 5:1-47

Warkarwa a tafki

1Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa. 2To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda5.2 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da Betzata; waɗansu kuma suna da Betsaida ne a nan. an kuma kewaye shi da shirayi biyar. 3A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.5.3 Waɗansu rubuce-rubucen hannu marar muhimmanci sosai suna da shanyayyu, kuma suka jira a motsa ruwaye. 4 Lokaci-lokaci mala’ikan Ubangiji yakan sauko ya motsa ruwaye. Mutum na farko da ya shiga tafkin bayan motsawa zai warke daga kowace cutar da yake da ita. 5Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas. 6Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”

7Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”

8Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.” 9Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya.

A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce, 10saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”

11Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’ ”

12Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”

13Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.

14Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.” 15Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.

Rai ta wurin Ɗan

16To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa. 17Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.” 18Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.

19Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi. 20Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma. 21Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama. 22Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan, 23don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.

24“Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. 25Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu. 26Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa. 27Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.

28“Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa 29su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci. 30Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.

Shaidu game da Yesu

31“In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce. 32Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.

33“Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya. 34Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto. 35Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.

36“Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni. 37Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba, 38maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba. 39Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, 40duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.

41“Ni ba na neman yabon mutane, 42na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku. 43Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi. 44Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?

45“Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi. 46Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni. 47Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”