האיגרת אל-העברים 12 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

האיגרת אל-העברים 12:1-29

1מאחר שאנו מוקפים בקהל עצום כזה של אנשי אמונה שמעידים על אמת אלוהים, הבה נסיר מעלינו כל דבר שמכביד עלינו, ובמיוחד את החטאים שדבקים בנו ומכשילים אותנו, ונרוץ בסבלנות את המרוץ שהעמיד אלוהים לפנינו. 2הבה נישא את עינינו אל ישוע, מורנו ויסוד אמונתנו, אשר היה מוכן למות מוות מביש על הצלב, כי ידע ששמורה לו שמחה לאחר מכן. עתה הוא יושב במקום הכבוד לימין האלוהים. 3אם רצונכם להימנע מעייפות וליאות רוחנית, חישבו לרגע על סבלנותו של המשיח כשסבל בושה וחרפה מיד האנשים החוטאים. 4אחרי הכול, מעולם לא נאבקתם נגד החטא עד מוות.

5האם שכחתם את תוכחת ה׳ שפונה אליכם כאל בניו?12‏.5 יב 5 משלי ג 11‏-12

”מוסר ה׳ בני אל תמאס

ואל תקץ בתוכחתו,

6כי את אשר יאהב ה׳

יוכיח וכאב את בן ירצה“.

7עליכם לקבל את תוכחת אלוהים, כי היא מיועדת לתועלת שלכם ולמען החינוך שלכם. אלוהים מתנהג אתכם כאב עם בניו, ואיזה אב אינו מוכיח ומחנך את בנו? 8אם אלוהים אינו מעניש אתכם כשאתם ראויים לכך, כשם שאבות אחרים מענישים את בניהם, פירוש הדבר שאינכם בני אלוהים ואינכם שייכים באמת למשפחתו. 9ואם אנו מכבדים את אבינו האנושי גם כשהוא מעניש אותנו, האם לא ניכנע בשמחה רבה יותר לפני האלוהים, אבינו הרוחני, כדי שנלמד כיצד לחיות?

10אבותינו האנושיים חינכו אותנו במשך שנים ספורות לפי ראות עיניהם, בעוד שאלוהים מחנך אותנו לתועלת שלנו, כדי שנשתתף בקדושתו.

11אין ספק שקבלת עונש היא חוויה מכאיבה ובלתי־נעימה, אך אלה שלמדו לקח מגלים כעבור זמן־מה שהעונש היה לברכה בחייהם.

12על כן חזקו את ידיכם החלשות ועמדו איתן על רגליכם הכושלות. 13הובילו את רגליכם בדרך ישרה, כדי שההולכים בעקבותיכם, גם אם יהיו חלשים וצולעים, לא יפלו ולא יכשלו, אלא יתחזקו.

14התרחקו מכל מריבה ונהלו חיי טוהר וקדושה, כי ללא קדושה לא תראו את האדון. 15השגיחו איש על רעהו שמא יתכחש אחד מכם לחסדו של אלוהים, כי באדם כזה יכולה להתפתח מרירות שעלולה להרעיל חיי רבים. 16השגיחו שאיש מכם לא ייגרר לזנות או לכל טומאה אחרת, כמו מעשי עשו שמכר את בכורתו תמורת נזיד עדשים. 17אתם יודעים שכאשר התחרט עשו ורצה להשיב לעצמו את זכות הבכורה, היה מאוחר מדי. הוא לא יכול היה לתקן את המעוות גם כאשר שפך דמעות רבות.

18זכרו היכן אתם עומדים: לא לפני להבת אש, ענן, ערפל או סערה נוראה, כפי שעמדו בני־ישראל לרגלי הר־סיני, 19ואף לא לפני תרועת שופר נוראה, וקול ה׳ שדיבר אל בני־ישראל דברים נוראים עד שהתחננו לפניו שיפסיק לדבר, 20כי לא יכלו לשאת את צו ה׳: שכל הנוגע בהר – כולל הבהמות – ייסקל באבנים וימות. 21המעמד היה נורא כל־כך עד שאפילו משה עצמו אמר: ”יגורתי וחרדתי!“

22אתם עומדים לפני הר־ציון האמיתי ולפני עיר אלוהים חיים, הלא היא ירושלים אשר בשמים. אתם עומדים גם לפני מקהלת רבבות מלאכים, 23לפני קהילת המשיח שמורכבת מאלה שכתובים בשמים, לפני האלוהים ששופט את הכול, לפני נשמות הצדיקים בשמים, אשר אלוהים השלים בהם את מלאכתו, 24ולפני ישוע המשיח עצמו אשר הביא לנו את הברית החדשה והנפלאה הזאת, ואשר דמו מכפר על חטאינו במקום שיזעק לנקמה כדמו של ‎ הֶבֶל.

25לכן אל תעזו לסרב להקשיב לקול של המדבר אליכם. שכן אם בני־ישראל לא נמלטו מעונש כשסירבו להקשיב למדבר כאן על־פני האדמה, על אחת כמה וכמה לא נימלט אנחנו מעונש, אם נסרב להקשיב לקולו של המדבר מן השמים. 26כשדיבר אלוהים מהר־סיני זעזע קולו את הארץ, אך הוא הבטיח שבפעם הבאה יזעזע לא רק את הארץ אלא גם את השמים!12‏.26 יב 26 ראה חגי ב 6 27מדבריו משתמע שהוא יבדוק ויברר את כל מה שעומד על יסודות רעועים, כדי שרק החזק והיציב יישאר.

28מאחר שקיבלנו מלכות שאינה יכולה להיהרס, הבה נבוא לפני אלוהים אסירי תודה, ונשרתהו כרצונו בצניעות וביראה, 29כי אלוהינו אש אוכלה הוא.

Hausa Contemporary Bible

Ibraniyawa 12:1-29

1Saboda haka, da yake muna kewaye da irin wannan taron shaidu mai girma, sai mu yar da duk abin da yake hana mu da kuma zunubin da yake saurin daure mu, mu kuma yi tseren da aka sa a gabanmu da nacewa. 2Bari mu kafa idanunmu a kan Yesu, tushe da kuma kammalar bangaskiyarmu, wanda ya jure kunyar gicciye da aka yi masa, domin ya san cewa daga baya zai yi farin ciki ya yi haka. Yanzu kuma yana zaune a hannun dama na kursiyin Allah. 3Ku lura da wannan wanda ya jure da irin hamayyan nan daga masu zunubi, don kada ku gaji, har ku fid da zuciya.

Allah yakan hori ’ya’yansa

4Cikin famanku da zunubi, ba ku yi tsayayya har ga zub da jininku ba tukuna. 5Kun kuma manta da kalmar ƙarfafawan nan da tana ce da ku ’ya’ya,

“Ɗana kada ka rena horon Ubangiji,

kada kuma ka fid da zuciya sa’ad da ya kwaɓe ka,

6domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna,

yakan kuma hori duk wanda yakan karɓa a matsayin ɗa.”12.5,6 K Mag 3.11,12

7Ku jimre shan wahala a matsayin horo; Allah yana yi da ku kamar ’ya’ya. Gama wane ɗa ne mahaifinsa ba ya horonsa? 8In ba a hore ku ba (kowa kuwa yakan sami horo), to, ku shegu ne ba ’ya’yan gida ba. 9Ban da haka ma, dukanmu mun kasance da ubannin jiki waɗanda suka hore mu muka kuma yi musu ladabi. Ashe, bai kamata mu yi wa Uban ruhohinmu biyayya mu kuwa rayu ba! 10Ubanninmu sun hore mu na ɗan lokaci yadda suka ga ya fi kyau; amma Allah yakan hore mu don amfaninmu, domin mu sami rabo cikin tsarkinsa. 11Babu horon da yake da daɗi a lokacin da ake yinsa, sai dai zafi. Amma daga baya waɗanda suka horu ta haka sukan sami kwanciyar rai wadda aikin adalci yake bayarwa.

12Saboda haka, sai ku ƙarfafa raunanan hannuwanku da gwiwoyinku marasa ƙarfi! 13“Ku shirya hanyoyi marasa gargaɗa saboda ƙafafunku,”12.13 K Mag 4.26 don kada guragu su daɗa gurguntawa, sai dai su warke.

Gargaɗi game da ƙin Allah

14Ku yi iyakacin ƙoƙari ku yi zaman lafiya da kowa, ku kuma zama masu tsarki; gama in ban da tsarki ba babu wanda zai ga Ubangiji. 15Ku lura fa kada wani yă kāsa samun alherin Allah, kada kuma wani tushen ɗacin rai yă tsira har yă kawo rikici, yă kuma ƙazantar da mutane da yawa. 16Ku lura kada wani yă zama mai fasikanci, ko marar tsoron Allah kamar Isuwa, wanda saboda ƙwaryar abinci ɗaya tak ya sayar da gādonsa na ɗan fari. 17Daga baya, kamar yadda kuka sani, sa’ad da ya nemi yă gāji wannan albarka, aka ƙi shi. Bai sami zarafin tuba ba, ko da yake ya nemi albarkan nan da hawaye.

Dutsen tsoro da kuma dutsen farin ciki

18Ba ku zo ga Dutsen Sinai12.18 Dutsen Sinai. Wato, inda Allah ya ba wa annabi Musa dokoki domin Isra’ilawa wanda ana iya taɓawa ba, ko ga wuta mai ci sosai, ko ga duhu baƙi ƙirin, ko 19ko busar ƙaho, ko ga irin wata murya mai magana da kalmomin da masu jinta suka yi roƙo kada su ƙara ji, 20domin ba su iya jimrewa da abin da aka umarta cewa, “Ko da ma dabba ce ta taɓa dutsen, dole a jajjefe ta da duwatsu.”12.20 Fit 19.12,13 21Ganin wannan abu da matuƙar bantsoro yake, har Musa ya ce, “Ina rawar jiki don tsoro.”12.21 Dubi M Sh 9.19.

22Sai dai kun zo ne ga Dutsen Sihiyona, ga Urushalima ta sama, birnin Allah mai rai. Kun zo ga dubu dubban mala’ikun da suke cikin taron farin ciki, 23kun zo ga ikkilisiyar ɗan fari, waɗanda sunayensu suna a rubuce a sama. Kun zo ga Allah, alƙalin dukan mutane, kun kuma zo ga ruhohin mutane masu adalci da aka mai da su cikakku. 24Kun zo ga Yesu, mai yin sulhu na sabon alkawari, da kuma ga jinin da aka yayyafa wanda yake magana mafi kyau fiye da jinin Habila.

25Ku lura fa kada ku ƙi wanda yake magana. Gama in su ba su tsira sa’ad da suka ƙi wanda ya gargaɗe su a wannan duniya ba, to, ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi jin wannan da yake yi mana gargaɗi daga Sama? 26A lokacin nan muryarsa ta jijjiga duniya, amma yanzu ya yi alkawari cewa, “Har wa yau sau ɗaya tak zan ƙara jijjiga ba duniya kaɗai ba, amma har ma da sammai.”12.26 Hag 2.6 27Wannan magana “sau ɗayan nan” sun nuna, kawar da abin da za a iya jijjigawa, wato, ƙirƙiro abubuwa, saboda abubuwan da ba a iya jijjigawa, su kasance.

28Saboda haka, da yake muna karɓar mulkin da ba ya jijjiguwa, sai mu yi godiya, ta haka kuwa mu yi wa Allah sujada yadda ya kamata, tare da bangirma da kuma tsoro, 29gama “Allahnmu wuta ne mai cinyewa.”12.29 M Sh 4.24