אגרת פולוס השנייה אל-הקורנתים 10 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

אגרת פולוס השנייה אל-הקורנתים 10:1-18

1אני, פולוס, מתחנן לפניכם בענווה, כפי שהמשיח היה מתחנן לפניכם. אחדים מכם טוענים: ”מכתביו של פולוס נועזים כל עוד הוא רחוק מאתנו, אך בבואו הנה יפחד להרים את קולו!“

2אני מתחנן לפניכם שלא תאלצוני לנהוג בכם ביד קשה בבואי אליכם, כי אני בטוח שאוכל לנהוג בחומרה באלה שטוענים שמעשי ומניעי הינם של אדם רגיל. 3אני אמנם אדם רגיל וחלש, אך איני נלחם את מלחמותיי בדרך אנושית רגילה. 4איני נלחם בכלי מלחמה רגילים, אלא בכלי המלחמה של אלוהים, ובעזרתם אני הורס את מבצרי השטן. 5אכן, כלי מלחמה אלה יכולים למוטט תחבולות וכל דבר שמתנשא נגד דעת אלוהים. בעזרתם אני מכניע את אלה לציות למשיח. 6אני מוכן להעניש כל הפרת משמעת עד שתושלם המשמעת שלכם במשיח.

7הבעיה אתכם היא, שאתם מסתכלים רק בקנקן ולא במה שיש בו. אם מישהו בטוח בעצמו שהוא שייך למשיח, שלא ישכח שאני שייך למשיח בדיוק כמוהו! 8גם אם נראה שאני מתגאה מדי על הסמכות שנתן לי האדון, לבנותכם ולא לפגוע בכם, איני מתבייש. 9אני אומר זאת כדי שלא תחשבו שאני מאיים עליכם סתם במכתבי.

10”אל תשימו לב למכתביו של פולוס“, אומרים אחדים מכם. ”הוא אמנם נשמע מרשים ותקיף, אך בבואו אלינו אישית תראו שהוא חלש ודיבורו אינו משכנע.“ 11הפעם ביקורי האישי יהיה מרשים ותקיף כמכתבי.

12כמובן שאיני מעיז לכלול את עצמי עם אלה שמשבחים את עצמם, ואף לא להשוות את עצמי אליהם. מה טיפשים הם! הם משווים את עצמם לעצמם, ושופטים את עצמם על־פי קנה המידה שקבעו בעצמם.

13אנחנו לעומתם איננו מתפארים יתר על המידה; אנו מתפארים רק בתחום העבודה שהקצה לנו אלוהים, ואתם נכללים בתחום זה.

14איננו מפריזים בסמכותנו עליכם, שכן אנו הבאנו לכם ראשונים את בשורת המשיח.

15איננו מתפארים בדברים מעבר לתחומנו, ואף לא בעמלם של אחרים. אנו רק מקווים שאמונתכם תגדל ושעבודתנו ביניכם תגדל גם היא, אך רק בתחום שהוקצה לנו.

16לאחר מכן נוכל לבשר את הבשורה לערים הרחוקות מכם, היכן שאיש אינו מבשר את הבשורה, וכך לא נפלוש לתחומם של אחרים. 17הכתובים אומרים:10‏.17 י 17 ירמיהו ט 23 ”המתהלל יתהלל בה׳!“ 18כי הלא אין ערך רב להתפארותו של אדם בעצמו, אך כאשר אלוהים משבח אדם יש לשבח ערך רב!

Hausa Contemporary Bible

2 Korintiyawa 10:1-18

Bulus ya kāre aikinsa

1Ni Bulus da kaina, ina roƙonku albarkacin tawali’u da sanyin hali na Kiristi, ni da ake yi wa kirari “marar tsanani” a cikinku, amma “mai matsawa” sa’ad da nake rabe da ku! 2Ina roƙonku cewa sa’ad da na zo kada ku tilasta ni in matsa muku, gama na tabbata zan iya tsaya wa waɗanda suka ce abin da muke yi sha’anin duniya ne. 3Ko da yake muna cikin duniya, ba ma yaƙi kamar yadda duniya take yi. 4Makaman da muke yaƙi da su, ba makamai na duniya ba ne. Sai dai na ikon Allah ne, masu rushe wuraren mafaka masu ƙarfi. 5Muna ka da masu gardama da kowane tunanin ɗaga kai da yake kafa kansa gāba da sanin Allah, muna kuma jan hankalin kowa ga bautar Kiristi. 6A shirye muke mu hori kowane rashin biyayya, sa’ad da biyayyarku ta cika.

7Kuna duban abubuwa bisa-bisa ne kawai. In wani ya ganin cewa shi na Kiristi ne, ya kamata yă sāke lura cewa kamar yadda yake na Kiristi, haka mu ma muke. 8Ko da zan yi gadara fiye da kima a game da izinin nan namu, wanda Ubangiji ya bayar saboda inganta ku, ba don rushe ku ba, ba ni da abin jin kunya a ciki. 9Ba na so yă zama kamar ina ƙoƙari in tsorata ku ne da wasiƙuna. 10Gama waɗansu suna cewa, “Wasiƙunsa suna da nauyi da kuma ƙarfi, amma kuwa in ka gan shi, ba shi da wani kwarjini, maganarsa kuma ba kome ba ce.” 11Ya kamata irin waɗannan mutane su gane cewa abin da muke faɗa a cikin wasiƙunmu sa’ad da ba ma nan tare da ku, shi muke aikatawa sa’ad da muke nan.

12Ba za mu yi ƙarfin halin lissafta kanmu, ko mu kwatanta kanmu da waɗansu masu yabon kansu ba. Sa’ad da suke gwada kansu da kansu, da kuma kwatanta kansu da kansu, ba su da hikima. 13Amma mu kam, ba za mu yi taƙama mu zarce iyakarmu ba, sai dai za mu yi taƙama cikin filin da Allah ya ƙayyade mana, filin kuwa ya kai har zuwa wurinku. 14Ba mu wuce gona da iri a taƙamarmu ba, kamar yadda zai zama, da a ce ba mu zo wurinku ba, gama mun kai har wurinku da bisharar Kiristi. 15Fahariyarmu ba fiye da yadda ya kamata take ba, ba tă kuma shafi aikin waɗansu ba. Sai dai muna sa zuciya bangaskiyarku ta riƙa ƙaruwa, ta haka kuma fagen aikinmu a cikinku yă riƙa ƙaruwa ƙwarai da gaske. 16Saboda mu iya yin wa’azin bishara a yankunan da suke gaba da ku. Gama ba ma so mu yi taƙama game da aikin da aka riga aka yi a sashen wani. 17Amma, “Duk mai yin taƙama, sai ya yi taƙama da Ubangiji.” 18Ai, ba mai yabon kansa ake amincewa da shi ba, sai dai wanda Ubangiji ya yaba wa.