אגרת פולוס השליח אל-הקולוסים 4 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

אגרת פולוס השליח אל-הקולוסים 4:1-18

1אדונים, אל תקפחו את פועליכם! תנו להם את המגיע להם, ואל תשכחו שגם לכם יש אדון בשמים.

2התמידו בתפילה; צפו לתשובתו של אלוהים, וכאשר זו תגיע, אל תשכחו להודות לו.

3התפללו גם בעדנו, שאלוהים ייתן לנו הזדמנויות רבות לבשר את הבשורה על המשיח, מעשה שהביא למאסרי הנוכחי. 4התפללו שיהיה בי האומץ לספר את הבשורה בחופשיות, בשלמות ובפשטות, כפי שמוטל עלי.

5התנהגו בחכמה עם הלא־מאמינים, ונצלו היטב כל הזדמנות להעיד על המשיח. 6דברו אך ורק דברים נעימים ודברי טעם, כדי שתוכלו להשיב לספקות של כל אחד.

7באשר אלי, טוכיקוס אחינו האהוב יספר לכם מה נשמע אצלי. טוכיקוס הוא עובד חרוץ שמשרת את האדון יחד איתי. 8שלחתי אותו אליכם כדי שיברר מה שלומכם, וכדי שבאותה הזדמנות יעודד וישמח אתכם. 9אוניסימוס, אחינו הנאמן והאהוב שהוא גם בן־עירכם, יצטרף לטוכיקוס, והשניים יספרו לכם את כל החדשות האחרונות.

10אריסטרכוס, האסור איתי כאן בכלא, מוסר לכם דרישת שלום, וכן מרקוס, בן אחותו של בר־נבא. אם מרקוס יבוא אליכם, קבלוהו בסבר־פנים יפות, כפי שכבר ביקשתי מכם. 11גם ישוע יוסטוס מוסר לכם דרישת שלום. אלה הם היהודים המשיחיים היחידים שעובדים איתי כאן, ועלי לומר שהיו לי לעידוד רב ולשמחה. 12אפפרס, בן־עירכם ומשרתו של ישוע המשיח, שולח לכם דרישת שלום חמה. הוא תמיד מתפלל בעדכם מכל לבו כדי שתתחזקו, שתתבגרו באמונתכם וכדי שתדעו את רצון האלוהים בכל מעשיכם. 13אני עד לכך שהוא מתפלל רבות למענכם מתוך דאגה אמיתית. ולא רק למענכם, אלא גם למען המאמינים בלודקיא והירפוליס.

14לוקס – הרופא היקר, ודימס מוסרים לכם דרישת שלום.

15מסרו דרישת שלום למאמינים בלודקיא, לנומפס ולכל המאמינים שנפגשים בביתה.

16דרך־אגב, לאחר שתקראו את המכתב הזה, אנא, תנו גם לקהילה בלודקיא לקרוא אותו, ובקשו מהם שיניחו לכם לקרוא את מכתבי אליהם. 17אמרו לארכיפוס בשמי: ”דאג לבצע בשלמות את המשימה שהטיל עליך האדון!“

18אני, פולוס, דורש בשלומכם בכתב ידי. אנא, זכרו אותי כאן בכלא. יברך אלוהים את כולכם. – אמן.

Hausa Contemporary Bible

Kolossiyawa 4:1-18

1Masu bayi, ku riƙe bayinku da kyau da kuma daidai, domin kun san cewa ku ma kuna da Ubangiji a sama.

Ƙarin umarnai

2Ku nace da yin addu’a, kuna zaman tsaro da kuma godiya. 3Ku kuma yi mana addu’a, mu ma, don Allah yă buɗe ƙofa saboda saƙonmu, don mu iya yin shelar asirin Kiristi, wanda saboda shi nake cikin sarƙoƙi. 4Ku yi addu’a yadda zan yi shelarsa, yadda ya kamata. 5Ku zama masu hikima a yadda kuke ma’amala da waɗanda suke ba masu bi ba; ku kuma yi amfani da kowane zarafi. 6Bari maganarku kullum ta zama da ladabi da kuma daɗin ji, domin ku san amsar da ta dace ku ba wa kowa.

Gaisuwa ta ƙarshe

7Tikikus shi ne ƙaunataccen ɗan’uwan nan, wanda ya yi aiki da aminci a hidimar Ubangiji tare da mu, zai kuwa faɗa muku dukan labari game da ni. 8Ina aikansa shi a gare ku musamman domin ku san yadda muke, yă kuma ƙarfafa muku zuciya. 9Yana zuwa tare da Onesimus, ƙaunatacce da kuma amintaccen mai bin nan, wanda yake ɗaya daga cikinku. Za su gaya muku dukan abin da yake faruwa a nan.

10Aristarkus yana a kurkuku tare da ni. Yana gaishe ku, haka ma Markus, wanda kakansa ɗaya ne da Barnabas. (Shi ne na riga na yi magana a kansa, na ce muku in ya zo, ku karɓe shi hannu biyu-biyu.)

11Yesu, wannan da muke kira Yustus, shi ma yana gaisuwa. Waɗannan ne kaɗai Yahudawa masu bi a cikin abokan aikina saboda mulkin Allah. Sun kuma zama da taimako a gare ni.

12Efafaras naku, mai hidimar Kiristi Yesu, yana gaisuwa. Kullum yana addu’a dominku sosai, don ku san cikakken abin da Allah yake so ku yi don kuma ku yi shi cikakke. 13Na tabbatar muku, cewa yana aiki ƙwarai dominku da kuma domin waɗanda suke a Lawodiseya da Hiyerafolis.

14Luka ƙaunataccen likitan nan, da kuma Demas suna gaishe ku.

15Ku miƙa gaisuwata ga ’yan’uwan da suke a Lawodiseya, musamman ga Nimfa da kuma ikkilisiyar da take taru a gidanta.

16Bayan an karanta muku wannan wasiƙa, ku tabbata an karanta ta kuma a ikkilisiyar Lawodiseyawa; ku ma ku karanta wasiƙar da ta zo daga Lawodiseya.

17Ku faɗa wa Arkiffus yă tabbata ya ƙarasa aikin da ya karɓa cikin Ubangiji.

18Ni Bulus ne nake rubuta muku wannan gaisuwa da hannuna. Ku tuna da sarƙoƙina. Alherin Allah yă kasance tare da ku.