אגרת פולוס הראשונה אל-הקורנתים 4 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

אגרת פולוס הראשונה אל-הקורנתים 4:1-21

1הייתי רוצה שתתייחסו אל אפולוס ואלי כאל משרתי המשיח שהופקדו בידם סודות ה׳. 2ומשרת נאמן ניכר בנכונותו לבצע את כל דברי אדוניו. 3לא אכפת לי אם אתם חושבים אותי למשרת טוב או לא; בנושא זה איני סומך אפילו על כושר השיפוט של עצמי. 4מצפוני אמנם נקי ושקט, אך עובדה זאת אינה הוכחה מספקת. רק אלוהים יכול לבחון אותי ולשפוט.

5לכן אל תמהרו להסיק מסקנות אם אדם זה או אחר הוא משרת טוב או לא; חכו לשובו של אדוננו. בבואו של האדון ישוע הוא יחשוף את האופי האמיתי של כל אחד מאתנו, וכולם ידעו מה הניע אותנו לשרת את האדון. באותו מעמד יעניק אלוהים שבחים לכל אחד לפי עבודתו.

6נתתי לכם כדוגמה את אפולוס ואותי, מפני שרציתי להדגיש את כוונתי: אל תפלו בין המאמינים! אל תתנשאו אחד על השני בשם שליח מסוים. 7מדוע אתם מתגאים כל־כך? האם יש בידכם דבר־מה שלא ניתן לכם על־ידי אלוהים? ואם כל מה שיש לכם בא מאלוהים, מדוע אתם מתנהגים כאנשים חשובים, כאילו כל מה שיש לכם הוא הישג פרטי ובלעדי שלכם?

8אתם חושבים שכבר קיבלתם את כל המזון הרוחני הדרוש לכם. אתם מרוצים ממצבכם הרוחני; הכתרתם את עצמכם למלכים בשעה שהיינו רחוקים מכם. הלוואי שבאמת הייתם מלכים בעיני ה׳, כי אז יכולנו למלוך יחד. 9לעתים קרובות אני חושב שאלוהים העמיד אותנו, השליחים, בסוף השורה; אנו מוצגים לראווה לפני העולם ולפני המלאכים כאסירים שנידונו למוות.

10אתם טוענים כי האמונה עשתה אותנו לטיפשים, ואילו אתם חכמים גדולים! אנחנו חלשים ואילו אתם חזקים מאוד! אנחנו נקלים ואתם מכובדים. 11דעו לכם שעד לרגע זה אנו רעבים, צמאים, ללא בגדים חמים, ללא בית משלנו ונזרקים ממקום למקום. 12הרווחנו את לחמנו בעמל־כפיים, ברכנו את מי שקילל אותנו, התייחסנו בסבלנות לאלה שפגעו בנו, 13דיברנו בשקט כשחרפו אותנו והעלילו עלינו עלילות. למרות הכול, עד לרגע זה מתייחסים אלינו כולם כאל טינופת ואשפה.

14איני כותב זאת כדי לבייש אתכם, אלא כדי להזהירכם ולייעץ לכם כילדים אהובים. 15אנשים רבים מסוגלים ללמד אתכם את דבר אלוהים, אך זכרו שאני לבדי דואג לכם כאב, שהרי אני הדרכתי אתכם אל המשיח בספרי לכם את הבשורה. 16משום כך אני מבקש מכם, אנא, קחו דוגמה ממני.

17אני שולח אליכם את טימותיוס כדי שיעזור לכם לעשות זאת. גם אותו הדרכתי אל האדון; הוא בני האהוב והנאמן באמונה, והוא יזכיר לכם מה שאני מלמד בכל הקהילות בהן אני מבקר.

18אני יודע כי יש ביניכם כאלה החושבים בטעות שאני פוחד לבוא ולדבר אתכם פנים אל פנים, ומחשבה זאת מכניסה בהם גאווה. 19אבל אל תדאגו; אם ירצה ה׳ אבוא אליכם בקרוב, ואז איווכח לדעת אם הגאוותנים האלה הם סתם דברנים גדולים, או אם הם באמת מלאים בכוח אלוהים. 20מלכות אלוהים אינה מבוססת על דיבורים, כי אם על מעשים בגבורת אלוהים. 21ומה אתם מעדיפים, שאבוא אליכם עם שוט או באהבה וביד רכה?

Hausa Contemporary Bible

1 Korintiyawa 4:1-21

Manzannin Kiristi

1Saboda haka, ya kamata mutane su ɗauke mu a matsayin bayin Kiristi, da kuma a matsayin waɗanda aka ba su amanar asirin abubuwan Allah. 2Yanzu fa, ana bukatar waɗanda aka ba su riƙon amana, dole su zama masu aminci. 3Ƙaramin abu ne a gare ni a ce ku ne za ku gwada ni, ko kuwa a gwada ni a wata kotun mutane, ai, ko ni kaina ba na yanka wa kaina hukunci. 4Lamirina bai ba ni laifi ba, sai dai wannan bai mai da ni marar laifi ba. Ubangiji ne mai hukunta ni. 5Saboda haka, kada ku shari’anta kome tun lokaci bai yi ba. Ku jira sai Ubangiji ya zo. Zai bayyana abin da yake a ɓoye a cikin duhu a sarari, zai kuma tone nufin zukatan mutane. A lokacin ne fa kowa zai karɓi yabo daga wurin Allah daidai gwargwado.

6To, fa ’yan’uwa, ga zancen waɗannan abubuwa, na misalta su ne ga kaina, da kuma Afollos saboda ku, don ku yi koyi da mu a kan abin da ake nufi da cewa, “Kada ku zarce abin da yake a rubuce.” Ta haka, ba za ku yi taƙama da wani mutum fiye da wani ba. 7Wa ya ce ka fi sauran mutane? Me kuma kake da shi, wanda ba karɓa ka yi ba? In kuma karɓa ka yi, me ya sa kake taƙama kamar ba karɓa ba ne ka yi?

8Kun riga kun sami duk abin da kuke nema! Kun riga kun yi arziki! Kun zama sarakuna, kun kuma zama haka ɗin ba tare da mu ba! Da a ce kun riga kun zama sarakuna mana da sai mu zama sarakuna tare da ku! 9Gama a ganina fa, Allah ya baje mu manzanni a ƙarshen jerin gwanon, a matsayin mutanen da aka hukunta ga mutuwa a filin wasanni. Mun zama abin kallo ga dukan duniya, ga mala’iku da kuma mutane. 10Mun zama masu wauta saboda Kiristi, ku kuwa kuna da hikima sosai a cikin Kiristi! Ba mu da ƙarfi, amma ku kuna da ƙarfi! Ana girmama ku, mu kuwa ana ƙasƙantar da mu! 11Har yă zuwa wannan sa’a, yunwa da ƙishirwa muke ciki, muna sanye da tsummoki, ana wulaƙanta mu, ba mu kuma da gida. 12Muna aiki da gaske da hannuwanmu. In aka la’anta mu, mukan sa albarka. In aka tsananta mana, mukan jimre; 13in aka ɓata mana suna, mukan mayar da alheri. Har yă zuwa wannan lokaci, mu ne kamar jujin duniya, abin ƙyamar kowa.

14Ba don in kunyata ku ba ne na rubuta wannan, sai dai don in gargaɗe ku a kan cewa ku ’ya’yana ne, ƙaunatattu. 15Ko da kuna da iyayen riƙo dubu goma cikin Kiristi, ba ku da ubanni da yawa, gama a cikin Kiristi Yesu, na zama mahaifi a gare ku, ta wurin bishara. 16Saboda haka, ina roƙonku ku yi koyi da ni. 17Saboda wannan dalili ina aika muku Timoti, ɗana, wanda nake ƙauna, mai aminci kuma a cikin Ubangiji. Zai tunashe ku game da yadda za ku bi Kiristi Yesu da kuma yadda ya yi daidai da yadda nake koyarwa a ko’ina, a kowace ikkilisiya.

18Waɗansunku suna tsammani ba zan zo wurinku ba har suna ɗagankai. 19Amma in Ubangiji ya yarda zan zo wurinku ba da daɗewa ba. Sa’an nan zan bincike ko masu wannan yawan ɗagan kan nan suna da wani iko. 20Gama mulkin Allah ba cika baki ba ne, sai dai ga iko. 21Wanne kuka fi so in na zo? Kuna so in tsananta muku ko in zama mai hankali da kuma sauƙinkai?