Asalin Yesu Kiristi
(Luka 3.23-38)
1Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
2Ibrahim ya haifi Ishaku,
Ishaku ya haifi Yaƙub,
Yaƙub ya haifi Yahuda da ’yan’uwansa,
3Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu;
Ferez ya haifi Hezron,
Hezron ya haifi Ram,
4Ram ya haifi Amminadab,
Amminadab ya haifi Nashon,
Nashon ya haifi Salmon,
5Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa,
Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa,
Obed ya haifi Yesse,
6Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda.
Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
7Solomon ya haifi Rehobowam,
Rehobowam ya haifi Abiya,
Abiya ya haifi Asa,
8Asa ya haifi Yehoshafat,
Yehoshafat ya haifi Yehoram,
Yehoram ya haifi Azariya,
9Azariya ya haifi Yotam,
Yotam ya haifi Ahaz,
Ahaz ya haifi Hezekiya,
10Hezekiya ya haifi Manasse,
Manasse ya haifi Amon,
Amon ya haifi Yosiya,
11Yosiya kuma ya haifi Yekoniya1.11 Wato, Jehohiyachin; haka ma a aya 12 da ’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
12Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon.
Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel,
Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
13Zerubbabel ya haifi Abiyud,
Abiyud ya haifi Eliyakim,
Eliyakim ya haifi Azor,
14Azor ya haifi Zadok,
Zadok ya haifi Akim,
Akim kuma ya haifi Eliyud,
15Eliyud ya haifi Eleyazar,
Eleyazar ya haifi Mattan,
Mattan ya haifi Yaƙub,
16Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
17Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.1.17 Ko kuwa Kiristi. Kiristi (Da Girik) Almasihu (Da Ibraniyanci) duk suna nufin “Shafaffe.”
Haihuwar Yesu Kiristi
(Luka 2.1-7)
18Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 19Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
20Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne. 21Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu,1.21 Yesu da Girik shi ne Yoshuwa da Ibraniyanci, wanda yake nufin Ubangiji yana ceto. gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
22Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa, 23“Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel”1.23 Ish 7.14 (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
24Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa. 25Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.
Ježíšův rodokmen
1Ježíšův rodokmen sahá přes Davida až k Abrahamovi.
2Abraham – Izák
Izák – Jákob
3Jákob – Juda (a bratři)
Juda – Peres a Zerach (matka Támar)
Peres – Chesrón
Chesrón – Rám
4Rám – Amínadab
Amínadab – Nachšón
Nachšón – Salmón
5Salmón – Bóaz (matka: Rachab)
Bóaz – Obéd (matka: Rút)
Obéd – Jišaj
6Jišaj – David (král)
David – Šalomoun (matka: Batšeba).
7Šalomoun – Rechabeám
Rechabeám – Abijám
Abijám – Ása
8Ása – Jóšafat
Jóšafat – Jóram
Jóram – Uzijáš
9Uzijáš – Jótam
Jótam – Achaz
Achaz – Chizkijáš
10Chizkijáš – Menaše
Menaše – Ámon
Ámon – Jóšijáš
11Jóšijáš – Jechoniáš
12Jekonjáš a jeho bratři.
Babylónské zajetí –
Jekonjáš – Šealtíel
Šealtíel – Zerubábel
13Zerubábel – Abiud
Abiud – Eljakim
Eljakim – Azór
14Azór – Sádok
Sádok – Achim
Achim – Eliud
15Eliud – Eleazar
Eleazar – Mattan
Mattan – Jákob
16Jákob – Josef
Josef (muž Marie)
JEŽÍŠ KRISTUS (narozen z Marie).
Rodokmen uzavírá Josef, manžel Marie, které se narodil Ježíš – Boží Syn.
17Od praotce Abrahama k Davidovi je to čtrnáct generací, dále čtrnáct generací od Davida po babylónské zajetí a od zajetí v Babylóně až ke Kristu také čtrnáct.
Anděl se zjevuje Josefovi
18S narozením Ježíše Krista to bylo takto: Ježíšova matka Marie byla zasnoubena s Josefem. Dříve, než se vzali, se však ukázalo, že bude matkou. 19Josef byl ohleduplný muž a nechtěl Marii vystavit veřejné hanbě, proto se rozhodl, že se s ní rozejde. 20Když o tom uvažoval, ukázal se mu ve snu Boží posel a řekl: „Josefe, Davidův synu, neboj se vzít si Marii. Co v ní bylo počato, je z Ducha svatého. 21Porodí syna a dáš mu jméno Ježíš. On vysvobodí svůj lid z moci zla. 22Těmito událostmi se splní předpověď proroka Izajáše: 23‚Slyšte! Panna bude těhotná a porodí syna. Budete mu říkat Immanuel, to znamená: Bůh je s námi.‘ “
24Když se Josef probudil, udělal vše tak, jak mu přikázal Boží posel, a oženil se s Marií. 25Ale nežil s ní manželsky až do doby, kdy se jí narodil syn, kterému dal jméno Ježíš.