Yaƙub 5 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

Yaƙub 5:1-20

Gargaɗi ga masu arziki masu danniya

1Yanzu fa sai ku saurara, ku masu arziki, ku yi kuka da ihu, saboda azabar da take zuwa a kanku. 2Arzikinku ya ruɓa, asu kuma sun cinye tufafinku. 3Zinariyarku da azurfarku sun yi tsatsa. Tsatsarsu kuwa za tă zama shaida a kanku, ta kuma ci namar jikinku kamar wuta. Kun ɓoye dukiya a kwanakin ƙarshe. 4Ga shi! Zaluncin da kuka yi na hakkin ma’aikatan gonakinku yana ta ƙara. Kukan masu girbi ya kai kunnuwan Ubangiji Maɗaukaki. 5Kun yi rayuwar jin daɗi a duniya kuna ci kuna sha na ganin dama. Kun ciyar da kanku kun yi ƙiba don ranar yanka. 6Kun hukunta kun kuma kashe mutane marasa laifi, waɗanda ba su yi gāba da ku ba.

Haƙuri cikin wahala

7Saboda haka ’yan’uwa, sai ku yi haƙuri har dawowar Ubangiji. Ku dubi yadda manomi yakan jira gona ta ba da amfaninta mai kyau, da kuma yadda yake haƙurin jiran ruwan sama na damina da na kaka. 8Haka ku ma, ku yi haƙuri, ku tsaya da ƙarfi, gama dawowar Ubangiji ya yi kusa. 9’Yan’uwa, kada ku yi gunaguni da juna, don kada a hukunta ku. Alƙalin yana tsaye a bakin ƙofa!

10’Yan’uwa, ku ɗauki annabawa da suka yi magana a cikin sunan Ubangiji, a matsayin gurbi na haƙuri a cikin shan wahala. 11Kamar yadda kuka sani, mukan ce da waɗanda suka jure, masu albarka ne. Kun ji daurewar Ayuba, kuka kuma ga abin da Ubangiji ya yi a ƙarshe. Ubangiji yana cike da tausayi da jinƙai.

12’Yan’uwana, fiye da kome, kada ku yi rantsuwa ko da sama, ko da ƙasa ko da wani abu dabam. Bari “I” naku yă zama “I”. “A’a” naku kuma yă zama “A’a”, don kada a hukunta ku.

Addu’ar bangaskiya

13Akwai waninku da yake shan wahala? Ya kamata yă yi addu’a. Akwai wani mai murna? Sai yă rera waƙoƙin yabo. 14Akwai waninku da yake ciwo? Ya kamata yă kira dattawan ikkilisiya su yi masa addu’a, su kuma shafa masa mai cikin sunan Ubangiji. 15Addu’ar da aka yi cikin bangaskiya, za tă warkar da marar lafiya, Ubangiji zai tashe shi. In ya yi zunubi kuwa za a gafarta masa. 16Saboda haka, ku furta wa juna zunubanku, ku yi addu’a saboda juna, domin ku sami warkarwa. Addu’ar mai adalci tana da iko da kuma amfani.

17Iliya mutum ne kamar mu. Ya yi addu’a da gaske don kada a yi ruwan sama, ba a kuma yi ruwan sama a ƙasar ba har shekaru uku da rabi. 18Ya sāke yin addu’a, sai sammai suka ba da ruwan sama, ƙasa kuma ta ba da amfaninta.

19’Yan’uwana, in waninku ya kauce daga gaskiya, wani kuma ya komo da shi, 20sai yă tuna da wannan. Duk wanda ya komo da mai zunubi daga kaucewarsa, zai cece shi daga mutuwa, yă kuma rufe zunubai masu ɗumbun yawa.

New International Reader’s Version

James 5:1-20

A Warning to Rich People

1You rich people, listen to me. Cry and weep, because you will soon be suffering. 2Your riches have rotted. Moths have eaten your clothes. 3Your gold and silver have lost their brightness. Their dullness will be a witness against you. Your wanting more and more will eat your body like fire. You have stored up riches in these last days. 4You have even failed to pay the workers who mowed your fields. Their pay is crying out against you. The cries of those who gathered the harvest have reached the ears of the Lord. He rules over all. 5You have lived an easy life on earth. You have given yourselves everything you wanted. You have made yourselves fat like cattle that will soon be butchered. 6You have judged and murdered people who aren’t guilty. And they weren’t even opposing you.

Be Patient When You Suffer

7Brothers and sisters, be patient until the Lord comes. See how the farmer waits for the land to produce its rich crop. See how patient the farmer is for the fall and spring rains. 8You too must be patient. You must remain strong. The Lord will soon come back. 9Brothers and sisters, don’t find fault with one another. If you do, you will be judged. And the Judge is standing at the door!

10Brothers and sisters, think about the prophets who spoke in the name of the Lord. They are an example of how to be patient when you suffer. 11As you know, we think that people who don’t give up are blessed. You have heard that Job was patient. And you have seen what the Lord finally did for him. The Lord is full of tender mercy and loving concern.

12My brothers and sisters, here is what is most important. Don’t make a promise by giving your word. Don’t promise by heaven or earth. And don’t promise by anything else to back up what you say. All you need to say is a simple “Yes” or “No.” If you do more than this, you will be judged.

The Prayer of Faith

13Is anyone among you in trouble? Then that person should pray. Is anyone among you happy? Then that person should sing songs of praise. 14Is anyone among you sick? Then that person should send for the elders of the church to pray over them. They should ask the elders to anoint them with olive oil in the name of the Lord. 15The prayer offered by those who have faith will make the sick person well. The Lord will heal them. If they have sinned, they will be forgiven. 16So confess your sins to one another. Pray for one another so that you might be healed. The prayer of a godly person is powerful. Things happen because of it.

17Elijah was a human being, just as we are. He prayed hard that it wouldn’t rain. And it didn’t rain on the land for three and a half years. 18Then he prayed again. That time it rained. And the earth produced its crops.

19My brothers and sisters, suppose one of you wanders away from the truth. And suppose someone brings that person back. 20Then here is what I want you to remember. Anyone who keeps a sinner from going astray will save them from death. God will erase many sins by forgiving them.