Yaƙub 3 – HCB & BPH

Hausa Contemporary Bible

Yaƙub 3:1-18

Ƙamewa harshe

1Kada yawancinku su so ɗaukan kansu a matsayin malamai, ’yan’uwana, domin kun san cewa mu da muke koyarwa za a yi mana shari’a mafi tsanani. 2Dukanmu mukan yi tuntuɓe a hanyoyi dabam-dabam. In wani bai taɓa yin kuskure a cikin maganarsa ba, shi cikakke ne, yana kuma iya ƙame dukan jikinsa.

3Sa’ad da muka sa linzamai a bakunan dawakai don mu sa su yi mana biyayya, mukan iya bin da dabbar gaba ɗaya. 4Ko kuwa misali, mu dubi jiragen ruwa, mana. Ko da yake suna da girma ƙwarai kuma iska mai ƙarfi ce take tura su, ana tuƙa su da ɗan ƙaramin sandan ƙarfe ne zuwa duk inda mai tuƙin jirgin yake so. 5Haka ma harshe yake, ga shi ɗan ƙanƙanin gaɓar jiki ne, amma sai manyan fariya. Ku dubi yadda ɗan ƙaramin ƙyastu yake ƙuna wa babban jeji wuta mana. 6Harshe ma wuta ne! A cikin duk gaɓoɓinmu, harshe shi ne tushen kowace irin mugunta, mai ɓata mutum gaba ɗaya, mai zuga zuciyar mutum ta tafasa, shi kuwa jahannama ce take zuga shi.

7Kowace irin dabba, tsuntsu, masu ja da ciki da kuma halittun da suke cikin teku an sarrafa su kuma mutum ne ya sarrafa, 8amma ba mutumin da zai iya ya sarrafa harshe. Mugu ne marar hutu, cike da dafi mai kisa.

9Da harshe mukan yabi Ubangijinmu da kuma Ubanmu, da shi kuma muke la’antar mutane, waɗanda aka halitta a kamannin Allah. 10Daga wannan baki guda yabo da la’ana suke fitowa. ’Yan’uwana, wannan bai kamata yă zama haka ba. 11Ruwa mai kyau da kuma ruwan gishiri zai iya fito daga maɓulɓula ɗaya? 12’Yan’uwana, itacen ɓaure yana iya haifar ’ya’yan zaitun, ko kuma itacen inabi yă haifi ’ya’yan ɓaure? Haka ma, maɓulɓular ruwan gishiri ba zai iya ba da ruwa mai kyau ba.

Hikima iri biyu

13Wane ne mai hikima da fahimta a cikinku? Bari yă nuna ta ta wurin rayuwarsa mai kyau, ta wurin ayyukan da aka yi cikin tawali’un da suke fitowa daga hikima. 14Amma in kuna cike da mugun kishi da kuma sonkai a cikin zukatanku, kada ku yi taƙama game da wannan, ko ku danne gaskiya. 15Irin wannan “hikima” ba daga sama ta sauko ba, ta duniya ce, ta rashin ruhaniya, ta Iblis kuma. 16Gama inda akwai kishi da sonkai, a can za a tarar da hargitsi da kowane irin mugun aiki.

17Amma hikimar da ta zo daga sama da fari tana da tsabta gaba ɗaya; sa’an nan mai ƙaunar salama ce, mai sanin ya kamata, mai biyayya, cike da jinƙai da aiki mai kyau, marar nuna bambanci, sahihiya kuma. 18Masu salama da suke shuki cikin salama sukan girbe adalci.

Bibelen på hverdagsdansk

Jakobs Brev 3:1-18

Om at passe på, hvad man siger

1Kære venner, kun ganske få af jer bør søge at blive lærere i menigheden. Vi, der har ansvar for den rette lære, kan nemlig forvente en strengere dom. 2Vi begår jo alle sammen fejl på mange forskellige måder. Den, der ikke siger noget forkert, har nået en høj grad af modenhed og vil også have kontrol over alle sine handlinger. 3Når vi lægger bidsel i munden på en hest, må den adlyde os, og så har vi hele hesten under kontrol. 4Eller tænk på skibene: De kan være nok så store, og kraftige vinde kan drive dem, men styrmanden kan med et ganske lille ror dreje sit skib, hvorhen han vil.

5-6På samme måde er tungen kun en lille del af vores krop, men den kan sætte en lavine af begivenheder i gang. Som en lille gnist kan sætte en stor skov i brand, kan tungen med ondskabsfulde ord ødelægge hele vores liv, selvom den kun er en lille del af kroppen. Er vores tunge først sat i brand af ilden fra Helvede, så kan den ødelægge hele vores tilværelse. 7Både vilde dyr og fugle, krybdyr og havdyr kan tæmmes og er blevet tæmmet, 8men tungen er det nærmest umuligt at tæmme. Det er svært at holde dens ondskab i skak, og den udspyr let en dødbringende gift. 9Tungen kan bruges til at lovprise Gud, men den samme tunge kan også bruges til at forbande mennesker, der jo er skabt i Guds billede. 10Hvis den samme mund både lovpriser og forbander, må der være noget galt, venner! 11Kan den samme kilde give både ferskvand og saltvand? 12Kan der vokse oliven på et figentræ eller figner på en vinstok? Nej vel? Det er umuligt at hente ferskvand op fra en saltholdig kilde.

Visdommens kendetegn

13Er der nogen iblandt jer, der mener, at de er vise og forstandige? Så lad dem gå foran med et godt eksempel og demonstrere deres visdom gennem ydmyghed og gode gerninger. 14Men hvis nogen er præget af bitter misundelse eller selviskhed, så kan de i alt fald ikke prale af at have Guds visdom. 15Den slags „visdom” kommer ikke fra Gud. Tværtimod, det er en jordisk, menneskelig tankegang, der stammer fra de onde ånder. 16Misundelse og selviskhed forvolder kaos og al slags ondskab. 17Men den visdom, der kommer fra Gud, er først og fremmest uskyldsren, dernæst fredselskende og imødekommende. Den tager hensyn til andre og er kendetegnet ved barmhjertighed og gode gerninger. Den er upartisk og oprigtig. 18Fredselskende mennesker planter fred, og de høster frugterne deraf.