Romawa 3 – HCB & LCB

Hausa Contemporary Bible

Romawa 3:1-31

Amincin Allah

1To, mece ce ribar zama mutumin Yahuda, ko kuwa mene ne amfanin kaciya? 2Akwai riba ƙwarai ta kowace hanya! Da farko dai, su ne aka danƙa wa kalmomin nan na Allah.

3Amma a ce waɗansu ba su da bangaskiya fa? Rashin bangaskiyarsu nan zai shafe amincin Allah? 4Ko kaɗan! Bari Allah yă zama mai gaskiya, kowane mutum kuma yă zama maƙaryaci. Kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Gama a tabbatar kana da gaskiya, sa’ad da ka yi magana,

ka kuma yi nasara sa’ad da ka yi shari’a.”3.4 Zab 51.4

5Amma in rashin adalcinmu ya bayyana adalcin Allah a fili, me za mu ce ke nan? Za mu ce Allah ya yi rashin adalci ke nan da ya saukar da fushinsa a kanmu? (Ina magana kamar yadda mutum zai yi ne.) 6Sam, ko kusa! Da a ce haka ne, ta yaya Allah zai shari’anta duniya? 7Wani zai iya ce, “In a dalilin ƙaryata, gaskiyar Allah ta ƙara bayyana, har aka ƙara ɗaukaka shi, to, ta yaya zan zama mai zunubi, in ƙaryata tana kawo ɗaukaka ga Allah?” 8In haka ne, “Ba sai mu yi ta yin mugunta don yă zama hanyar samun nagarta ba”? Kamar yadda masu baƙar magana game da mu suna cewa wai haka muke faɗa. Tabbatacce za a hukunta irin waɗannan da hukuncin da ya dace da su.

Babu mai adalci

9To, me za mu ce ke nan? Mun fi su ke nan? Ina, ko kaɗan! Mun riga mun zartar cewa da Yahudawa da Al’ummai duk suna a ƙarƙarshin zunubi. 10Kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Babu wani mai adalci, babu ko ɗaya;

11babu wani mai fahimta,

babu wani mai neman Allah.

12Duk sun kauce gaba ɗaya,

sun zama marasa amfani;

babu wani mai aikata nagarta,

babu ko ɗaya.”3.12 Zab 14.1-3; Zab 53.1-3; M Had 7.20

13“Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗun kaburbura ne,

harsunansu suna yin ƙarya.”3.13 Zab 5.9

“Dafin mugun maciji yana a leɓunansu.”3.13 Zab 140.3

14“Bakunansu sun cike da la’ana da ɗacin rai.”3.14 Zab 10.7

15“Ƙafafunsu suna saurin kai su zuwa ga zub da jini;

16hallaka da baƙin ciki suna ko’ina a hanyoyinsu,

17ba su kuma san hanyar salama ba.”3.17 Ish 59.7,8

18“Babu tsoron Allah a idanunsu.”3.18 Zab 36.1

19Yanzu mun san cewa dukan abin da doka ta ce, tana magana ne ga waɗanda suke ƙarƙarshin doka, saboda a rufe kowane baki; dukan duniya kuma ta ba da lissafin kanta a gaban Allah. 20Saboda haka babu wanda Allah zai ce da shi mai adalci ta wurin kiyaye doka kawai; a maimako, ta wurin doka ne muke sane da zunubi.

Adalci ta wurin bangaskiya

21Amma yanzu an bayyana wani adalci daga Allah, wannan adalcin bai danganta ga doka ba, Doka da Annabawa suna ba da shaida game da wannan adalci. 22Wannan adalcin Allah yana zuwa ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi ga dukan waɗanda suka ba da gaskiya ne. Ba bambanci, 23gama duka sun yi zunubi suka kuma kāsa ga ɗaukakar Allah, 24an kuma kuɓutar da su kyauta ta wurin alherinsa bisa ga aikin fansar da ya zo ta wurin Yesu Kiristi. 25Allah ya miƙa Yesu Kiristi a matsayin hadayar kafara, ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya yi haka domin yă nuna adalcinsa, domin a cikin haƙurinsa bai hukunta zunuban da aka aikata a dā ba 26ya yi haka domin yă nuna adalcinsa a wannan lokaci, saboda yă zama mai adalci da mai kuɓutar da waɗanda suke ba da gaskiya a cikin Yesu.

27To, me za mu yi taƙama a kai? Babu wani abin da zamu yi taƙama a kai. A kan wace ƙa’ida ce za mu yi taƙama? Ta hanyar bin doka ne? A’a, sai dai ta wurin bangaskiya. 28Gama mun tsaya a kan cewa ta wurin bangaskiya ne ake kuɓutar da mutum, ba ta wurin kiyaye doka ba. 29Allah ɗin, Allahn Yahudawa ne kaɗai? Shi ba Allahn Al’ummai ba ne? I, shi Allahn Al’ummai ne ma, 30da yake Allah ɗaya ne kaɗai, shi kuma zai kuɓutar da masu kaciya bisa ga bangaskiya da kuma marasa kaciya ta wurin wannan bangaskiya ɗin. 31To, za mu soke dokar saboda wannan bangaskiyar ne? Ko kaɗan! A maimako, sai ma tabbatar da ita muke yi.

Luganda Contemporary Bible

Abaruumi 3:1-31

Obwesigwa bwa Katonda

1Kaakano olwo Omuyudaaya alina nkizo ki? Oba okukomolebwa kugasa ki? 23:2 Ma 4:8; Zab 147:19Kugasa nnyo mu ngeri nnyingi. Okusookera ddala, Abayudaaya be baateresebwa ebigambo bya Katonda.

33:3 a Beb 4:2 b 2Ti 2:13Kituufu nti abamu ku bo tebakkiriza bigambo ebyo. Obutakkiriza bwabwe buliggyawo obwesigwa bwa Katonda, olw’okuba nga bo tebaalina kukkiriza? 43:4 a Yk 3:33 b Zab 116:11 c Zab 51:4Tekisoboka. Katonda ye wa mazima, newaakubadde nga buli muntu yenna mulimba. Ebyawandiikibwa bigamba nti,

“Olyoke otuukirire mu bigambo byo,

era osinge bw’osala omusango.”

53:5 Bar 6:19; Bag 3:15Naye obanga obutali butuukirivu bwaffe bulagira ddala obutuukirivu bwa Katonda, tunaayogera ki? Kikyamu Katonda okutunyiigira era n’atubonereza? Mu kino njogera ng’omuntu. 63:6 Lub 18:25Nedda, sikikyamu. Katonda alisalira atya ensi omusango? 73:7 nny 4Naye obanga obulimba bwammwe bweyongera okugulumiza Katonda, nga kiraga Katonda bw’ali ow’amazima, oyinza okwebuuza lwaki okyasalirwa omusango ng’omwonoonyi? 83:8 Bar 6:1Era okyayinza okwongerako na kino nti tukolenga ebibi mulyoke muveemu ebirungi, ng’abamu bwe batuwaayiriza nti, bwe tugamba. Kyokka Katonda mwenkanya, era alibasalira nga bwe kibagwanira.

Tewali mutuukirivu n’omu

93:9 nny 19, 23; Bag 3:22Bino byonna bitegeeza ki? Kitegeeza nti ffe Abayudaaya tuli bulungi nnyo okusinga abantu abalala bonna? Nedda, n’akatono. Ffenna tufugibwa kibi, ne bwe baba Abayudaaya oba Abaamawanga. 10Ng’ebyawandiikibwa bwe bigamba nti:

“Tewali mutuukirivu n’omu.

11Tewali ategeera

wadde anoonya Katonda.

123:12 Zab 14:1-3Bonna baakyama,

bonna awamu baafuuka kitagasa;

tewali n’omu akola obulungi,

tewali n’omu.”

133:13 a Zab 5:9 b Zab 140:3“Emimiro gyabwe giringa entaana ezaasaamiridde,

n’emimwa gyabwe gijjudde obulimba.”

“Buli kigambo ekibavaamu kiri ng’obusagwa bw’omusota.”

143:14 Zab 10:7“Emimwa gyabwe gijjudde okukolima n’obukyayi.”

15“Ebigere byabwe byanguwa okuyiwa omusaayi,

16buli gye balaga baleka abantu baayo mu kuzikirira na mu nnaku njereere.

17Tebamanyi kkubo lya mirembe.”

183:18 Zab 36:1“N’okutya tebatya Katonda.”

193:19 a Yk 10:34 b Bar 2:12Tumanyi nga buli kyawandiikibwa mu mateeka, kyawandiikibwa ku lw’abo abafugibwa amateeka. Amateeka malambulukufu ku nsonga ezo, omuntu yenna aleme okwekwasa ensonga yonna, ate era ne Katonda okwongera okulaga ng’ensi yonna bwe yasobya. 203:20 a Bik 13:39; Bag 2:16 b Bar 7:7Kubanga tewali n’omu aliweebwa obutuukirivu mu maaso ga Katonda olw’ebikolwa by’amateeka. Mu mateeka mwe tutegeerera ddala ekibi.

Obutuukirivu buva mu Kukkiriza

213:21 a Bar 1:17; 9:30 b Bik 10:43Kale kaakano tutegeere ng’obutuukirivu bwa Katonda tebutuweebwa lwa kugondera Mateeka. Ekyo kikakasibwa Amateeka ne bannabbi. 223:22 a Bar 9:30 b Bar 10:12; Bag 3:28; Bak 3:11Obutuukirivu bwa Katonda butuweebwa olw’okukkiriza Yesu Kristo. Katonda tasosola. 23Ffenna twayonoona era tetusaanira kitiibwa kya Katonda. 243:24 a Bar 4:16; Bef 2:8 b Bef 1:7, 14; Bak 1:14; Beb 9:12Kyokka twaweebwa obutuukirivu bwa buwa olw’ekisa kye ekiri mu kununulibwa okuli mu Yesu Kristo; 253:25 a 1Yk 4:10 b Beb 9:12, 14 c Bik 17:30Katonda yaweereza Kristo okuba omutango, bwe tukkiriza Kristo olw’omusaayi gwe yayiwa. Alaga obutuukirivu bwe mu kugumiikiriza ebibi ebyakolebwa edda, be bantu abaayonoona mu biseera biri eby’edda. 26Kino kiraga Katonda bw’alaga okwaniriza kw’alina eri abantu mu biro bino, bwe baba n’okukkiriza mu Yesu.

273:27 Bar 2:17, 23; 4:2; 1Ko 1:29-31; Bef 2:9Kale lwaki twenyumiriza? Tewali nsonga etwenyumirizisa. Lwa kuba nga twagoberera amateeka? Nedda, lwa kukkiriza. 283:28 nny 20, 21; Bik 13:39; Bef 2:9Noolwekyo omuntu aweebwa obutuukirivu lwa kukkiriza so si lwa kugoberera mateeka. 293:29 Bar 9:24Oba Katonda wa Bayudaaya bokka? Si ye Katonda w’amawanga amalala gonna? Weewaawo nabo Katonda waabwe. 303:30 Bag 3:8Kubanga ye Katonda omu awa obutuukirivu abaakomolebwa, n’abo abataakomolebwa olw’okukkiriza kwabwe. 31Kale amateeka tugaggyewo olw’okukkiriza? Kikafuuwe. Tunyweza manyweze.