Romawa 15 – HCB & CARSA

Hausa Contemporary Bible

Romawa 15:1-33

1Mu da muke da ƙarfi ya kamata mu yi haƙuri da kāsawar marasa ƙarfi ba kawai mu gamshi kanmu ba. 2Ya kamata kowannenmu yă faranta wa maƙwabcinsa rai don kyautata zamansa domin kuma yă gina shi. 3Gama ko Kiristi ma bai gamshi kansa ba, amma kamar yadda yake a rubuce cewa, “Zage-zagen da waɗansu suka yi maka, duk sun fāɗo a kaina.”15.3 Zab 69.9 4Gama duk abin da aka rubuta a dā an rubuta ne domin yă koya mana, don ta wurin jimrewa da kuma ƙarfafawar Nassosi mu kasance da bege.

5Bari Allah mai ba da haƙuri da kuma ƙarfafawa yă ba ku ruhun haɗinkai da juna yayinda kuke bin Kiristi Yesu, 6don da zuciya ɗaya da kuma baki ɗaya kuke ɗaukaka Allah da kuma Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi.

7Ta haka sai ku karɓi juna kamar yadda Kiristi ya karɓe ku, don a yabi Allah. 8Ina dai gaya muku cewa Kiristi ya zama bawan Yahudawa a madadin gaskiyar Allah, don yă tabbatar da alkawaran da aka yi wa kakannin kakanninmu 9domin Al’ummai su ɗaukaka Allah saboda jinƙansa, kamar yadda yake a rubuce,

“Saboda haka zan yabe ka a cikin Al’ummai;

zan rera waƙoƙi ga sunanka.”15.9 2Sam 22.50; Zab 18.49

10Ya kuma ce,

“Ku yi farin ciki, ya Al’ummai, tare da mutanensa.”15.10 M Sh 32.43

11Da kuma,

“Ku yabi Ubangiji, dukanku Al’ummai,

ku kuma rera masa yabo, dukanku mutanen duniya.”15.11 Zab 117.1

12Kuma Ishaya ya ce,

“Tushen Yesse zai tsiro,

wanda zai taso yă yi mulkin al’ummai;

al’ummai za su sa bege a gare shi.”15.12 Ish 11.10

13Bari Allah na bege yă cika ku da matuƙar farin ciki da salama yayinda kuke dogara gare shi, domin ku yalwata cikin bege ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki.

Bulus mai hidima ga al’ummai

14Ni kaina na tabbata, ’yan’uwana, cewa ku kanku kuna cike da kirki, cikakku cikin sani da kuma ƙwararru don yin wa juna gargaɗi. 15Na rubuta muku gabagadi a kan waɗansu batuttuwa, don in sāke tuna muku su, saboda alherin da Allah ya ba ni 16in zama mai hidimar Kiristi Yesu ga Al’ummai da aikin firist na yin shelar bisharar Allah, don Al’ummai su zama hadaya mai karɓuwa ga Allah, tsattsarka ta wurin Ruhu Mai Tsarki.

17Saboda haka ina taƙama cikin Kiristi Yesu a cikin hidimata ga Allah. 18Ba zan yi karambani in faɗi kome ba sai dai abin da Kiristi ya aikata ta wurina a jagorantar da Al’ummai su yi biyayya ga Allah ta wurin abin da na faɗa da kuma aikata 19ta wurin ikon alamu da ayyukan banmamaki, da kuma ikon Ruhun Allah. Ta haka daga Urushalima har yă zuwa kewayen Illirikum, na yi wa’azin bisharar Kiristi. 20Labudda, burina shi ne in yi wa’azin bishara inda ba a san Kiristi ba, don kada yă zama ina gini ne a kan tushen da wani ya kafa. 21Sai dai kamar yadda yake a rubuce,

“Waɗanda ba a faɗa musu labarinsa ba za su gani,

waɗanda kuma ba su ji ba za su fahimta.”15.21 Ish 52.15

22Wannan ne ya sa sau da yawa aka hana ni zuwa wurinku.

Shirin Bulus yă ziyarci Roma

23Amma yanzu da babu sauran wurin da ya rage mini in yi aiki a waɗannan yankuna, da yake kuma shekaru masu yawa ina da marmari in gan ku, 24ina shirin yin haka in na tafi Sifen. Ina fata in ziyarce ku yayinda nake wucewa don ku raka ni can, bayan na ji daɗin zama tare da ku na ɗan lokaci. 25Yanzu kam, ina hanyata zuwa Urushalima don in kai gudummawa ga tsarkaka a can. 26Gama Makidoniya da Akayya sun ji daɗin yin gudummawa domin matalautan da suke cikin tsarkakan da suke a Urushalima. 27Sun kuwa ji daɗin yin haka, gama ya zama kamar bashi ne a gare su. Da yake Al’ummai sun sami rabo cikin albarkun ruhaniyar Yahudawa, ya zama musu kamar bashi su ma su taimaki Yahudawa da albarkunsu na kayan duniya. 28Saboda haka in na kammala wannan aiki na kuma tabbata cewa sun karɓi wannan amfani, zan tafi Sifen in kuma ziyarce ku a hanyata. 29Na san cewa sa’ad da na zo wurinku, zan zo ne cikin yalwar albarkar Kiristi.

30Ina roƙonku ’yan’uwa, saboda Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma saboda ƙaunar Ruhu, ku haɗa kai tare da ni cikin famata ta wurin yin addu’a ga Allah saboda ni. 31Ku yi addu’a don in kuɓuta daga hannun marasa bi a Yahudiya don kuma gudummawar da nake kaiwa Urushalima ta zama abar karɓa ga tsarkaka a can, 32don da yardar Allah, in iso wurinku da farin ciki in kuma wartsake tare da ku. 33Allah na salama yă kasance tare da ku duka. Amin.

Священное Писание (Восточный перевод), версия с «Аллахом»

Римлянам 15:1-33

1Мы, сильные в вере, должны быть снисходительны к ошибкам слабых и не искать своей личной выгоды. 2Каждый из нас должен угождать своему ближнему, заботясь о том, что служит к его благу и духовному росту. 3Аль-Масих тоже не Самому Себе угождал, но, как написано: «Оскорбления тех, кто злословит Тебя, пали на Меня»15:3 Заб. 68:10.. 4Ведь всё Писание было дано с целью научить нас, чтобы благодаря терпению и ободрению, получаемому из Писания, мы имели надежду.

5Пусть же Аллах, Который даёт терпение и ободрение, даст вам жить в согласии друг с другом, как и подобает последователям Исы аль-Масиха, 6чтобы вы единодушно и едиными устами прославляли Бога и Отца нашего Повелителя Исы аль-Масиха.

Иса пришёл и для иудеев, и для других народов

7Ради прославления Аллаха принимайте друг друга, как и аль-Масих принял вас. 8Я говорю вам, что аль-Масих стал слугой обрезанных, чтобы явить верность Аллаха, подтвердив те обещания, которые Аллах дал праотцам, 9а также для того, чтобы и другие народы могли прославить Аллаха за Его милость, как написано:

«За это я буду славить Тебя среди других народов,

имени Твоему воспою я хвалу»15:9 Заб. 17:50; 2 Цар. 22:50..

10И ещё написано:

«Радуйтесь, язычники, вместе с Его народом!»15:10 Втор. 32:43.

11И ещё:

«Славьте Вечного, все язычники!

Хвалите Его, все народы!»15:11 Заб. 116:1.

12Исаия также говорит:

«Придёт Корень15:12 Или: «Росток». Есея

и поднимется, чтобы править народами,

и язычники будут надеяться на Него»15:12 Ис. 11:10..

13Пусть же Аллах, источник всякой надежды, через вашу веру наполнит вас радостью и миром, чтобы вам в силе Святого Духа изобиловать надеждой.

Паул – служитель Исы аль-Масиха для язычников

14Братья мои, я убеждён в том, что вы полны добра, исполнены знаний и можете учить друг друга. 15Тем не менее в этом послании я смело напоминаю вам о некоторых вещах, потому что Аллах по Своей благодати поручил мне 16быть служителем Исы аль-Масиха для язычников. И я тружусь как священнослужитель, возвещая Радостную Весть Аллаха, чтобы принести Ему обращённых из язычников, словно освящённую Святым Духом жертву, которая приятна Аллаху.

17Итак, я могу хвалиться своим служением Аллаху через Ису аль-Масиха. 18Я смею говорить только о том, что аль-Масих совершил через меня, чтобы привести язычников к повиновению Аллаху. Он совершил это словом и делом, 19силой знамений и чудес, силой Духа Аллаха, так что я исполнил это служение: возвещать Радостную Весть об аль-Масихе от Иерусалима и вплоть до Иллирика15:19 Иллирик – область, располагавшаяся на восточном побережье Адриатического моря.. 20Моим стремлением всегда было возвещать Радостную Весть там, где ещё не знают об аль-Масихе, чтобы мне не строить на чужом фундаменте, 21но исполнить написанное:

«Те, кому не было сказано о Нём, увидят,

и те, кто не слышал, поймут»15:21 Ис. 52:15..

22И это моё служение было причиной того, что я, хотя и собирался много раз, не смог прийти к вам.

Планы Паула посетить Рим

23Теперь же я закончил свой труд в этих краях, и так как я уже много лет хотел прийти к вам, 24то намерен сделать это, когда отправлюсь в Испанию. Я надеюсь, что навещу вас по дороге туда и что вы поможете мне продолжить мой путь, как только я хоть немного наслажусь вашим обществом. 25Сейчас же я отправляюсь в Иерусалим для служения живущим там братьям, 26потому что общины Македонии и Ахаии15:26 Македония и Ахаия – Греция в целом. решили провести сбор пожертвований для бедных из числа верующих, живущих в Иерусалиме. 27Они сами решили это сделать, ведь они и правда в долгу перед ними. Как иудеи, верующие в Ису, поделились с ними своими духовными благословениями, так и они, в свою очередь, должны поделиться с иудеями своими материальными благами. 28После того как я выполню это поручение и передам им собранное, я намерен отправиться в Испанию и по пути навестить вас. 29Я уверен, что, когда приду к вам, аль-Масих благословит вас в полной мере.

30Умоляю вас, братья, ради Повелителя нашего Исы аль-Масиха и ради любви Духа, присоединиться к моей усердной молитве к Аллаху обо мне. 31Молитесь о том, чтобы в Иудее неверующие не причинили мне вреда и чтобы братья в Иерусалиме приняли моё служение. 32Тогда я смогу прийти к вам с радостью, и мы сможем вместе отдохнуть, если на то будет воля Аллаха15:32 Если на то будет воля Аллаха – см. сноску на 1:10.. 33Пусть Аллах, дающий нам мир, будет со всеми вами, аминь.