Mattiyu 4 – HCB & CARSA

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 4:1-25

Gwajin Yesu

(Markus 1.12,13; Luka 4.1-13)

1Sa’an nan Ruhu ya kai Yesu cikin hamada don Iblis yă gwada shi. 2Bayan ya yi azumi yini arba’in da kuma dare arba’in, sai ya ji yunwa. 3Sai mai gwajin ya zo wurinsa ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka ce wa duwatsun nan su zama burodi.”

4Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, sai dai da kowace kalmar da take fitowa daga bakin Allah.’4.4 M Sh 8.3

5Sai Iblis ya kai shi birni mai tsarki, ya kai shi can wuri mafi tsayi duka na haikali. 6Ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, yi tsalle ka sauka ƙasa. Gama a rubuce yake,

“ ‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai,

za su tallafe ka da hannuwansu,

don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’4.6 Zab 91.11,12

7Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake kuma cewa, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’4.7 M Sh 6.16

8Har wa yau, Iblis ya kai shi bisa wani dutse mai tsawo sosai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu. 9Ya ce, “Zan ba ka dukan wannan, in za ka durƙusa ka yi mini sujada.”

10Sai Yesu ya ce masa, “Rabu da ni, Shaiɗan! Gama a rubuce yake, ‘Yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai kuma za ka bauta wa.’4.10 M Sh 6.13

11Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.

Yesu ya fara wa’azi

(Markus 1.14,15; Luka 4.14,15)

12Da Yesu ya ji labari cewa an kulle Yohanna a kurkuku, sai ya koma zuwa Galili. 13Ya bar Nazaret, ya je ya zauna a Kafarnahum, wadda take a bakin tafki wajen Zebulun da Naftali 14don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,

15“Ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali,

da kuke a hanyar zuwa tekun Galili, a ƙetaren Urdun,

wannan yankin Galili ta Al’ummai,

16mutanen da suke zama cikin duhu

sun ga babban haske;

haske kuma ya haskaka

a kan waɗanda suke zama a inuwar mutuwa.”4.16 Ish 9.1,2f

17Tun daga wannan lokaci, Yesu ya fara wa’azi yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”

Kiran almajirai na farko

(Markus 1.16-20; Luka 5.1-11)

18Da Yesu yana kan tafiya a bakin Tekun Galili, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Siman wanda ake kira Bitrus da ɗan’uwansa Andarawus. Suna jefa abin kamun kifi a tafki, gama su masunta ne. 19Sai Yesu ya ce, “Zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masu jan mutane zuwa wurina.” 20Nan da nan suka bar abin kamun kifinsu suka bi shi.

21Da ya ci gaba daga nan, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna. Suna cikin jirgin ruwa tare da mahaifinsu Zebedi, suna shirya abin kamun kifinsu. Yesu ya kira su, 22nan take suka bar jirgin ruwan da mahaifinsu suka kuwa bi Yesu.

Yesu ya warkar da marasa lafiya

(Luka 6.17-19)

23Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane. 24Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su. 25Taron mutane mai yawa daga Galili, Dekafolis,4.25 Wato, Birane Goma Urushalima, Yahudiya da kuma yankin hayin Urdun suka bi shi.

Священное Писание (Восточный перевод), версия с «Аллахом»

Матай 4:1-25

Искушение в пустыне

(Мк. 1:12-13; Лк. 4:1-13)

1Затем Дух повёл Ису в пустыню для того, чтобы Ему пройти искушение от Иблиса. 2После сорока дней и сорока ночей, проведённых в посте, Иса почувствовал сильный голод. 3Тогда искуситель подошёл и сказал Ему:

– Если Ты Сын Всевышнего (Царственный Спаситель), то прикажи этим камням стать хлебом.

4Но Иса ответил:

– Написано: «Не одним хлебом живёт человек, но и каждым словом, исходящим из уст Аллаха»4:4 Втор. 8:3..

5Затем Иблис привёл Ису в святой город и поставил Его на самый верх Иерусалимского храма.

6– Если Ты Сын Всевышнего, – сказал он Ему, – то бросься вниз. Ведь написано же:

«Своим ангелам повелит о Тебе,

и они понесут Тебя на руках,

чтобы ноги Твои не ударились о камень»4:6 Заб. 90:11-12..

7Иса сказал ему:

– Написано также: «Не испытывай Вечного, Бога твоего»4:7 Втор. 6:16..

8Тогда Иблис взял Его на очень высокую гору и показал Ему все царства мира во всём их блеске.

9И он сказал Ему:

– Всё это я передам Тебе, если Ты падёшь и поклонишься мне!

10Тогда Иса сказал ему:

– Прочь от Меня, Шайтан! Ведь написано: «Поклоняйся Вечному, Богу твоему, и служи Ему одному»4:10 Втор. 6:13..

11Тогда Иблис оставил Его, а к Исе приступили ангелы и служили Ему.

Иса аль-Масих начинает Своё служение

(Мк. 1:14-15; Лк. 4:14-15)

12Когда Иса услышал о том, что Яхия заключён в темницу, Он возвратился в Галилею. 13Покинув Назарет, Он поселился в Капернауме, который расположен на берегу озера, в земле, принадлежавшей родам Завулона и Неффалима. 14Так исполнилось пророчество Исаии:

15«Земля Завулона и земля Неффалима,

где приморский путь, ведущий за Иордан,

Галилея языческая!

16Народ, живущий во тьме,

увидел великий свет.

У живущих в стране, объятой тенью смерти,

свет воссиял»4:15-16 Ис. 9:1-2..

17С этого времени Иса начал возвещать:

– Покайтесь, потому что Аллах уже устанавливает Своё Царство!

Четыре рыбака следуют за Исой аль-Масихом

(Мк. 1:16-20; Лк. 5:2-11)

18Однажды, проходя вдоль Галилейского озера, Иса увидел двух братьев: Шимона, прозванного Петиром, и его брата Андера. Они забрасывали в озеро сети, так как были рыбаками.

19– Идите за Мной, – сказал Он им, – и Я сделаю вас ловцами людей.

20Братья сразу же оставили сети и пошли за Ним. 21Пройдя дальше, Иса увидел двух других братьев: Якуба и Иохана, сыновей Завдая. Они были в лодке со своим отцом и чинили сети. Иса позвал и их. 22Они сразу же, оставив лодку и отца, пошли за Ним.

Иса аль-Масих возвещает Радостную Весть в Галилее

(Мк. 3:7-12; Лк. 6:17-19)

23Иса ходил по всей Галилее, уча в молитвенных домах, возвещая Радостную Весть о Царстве и исцеляя людей от всех болезней и недугов. 24Слух о Нём распространился по всей Сирии, и к Нему приносили страдающих от самых различных болезней, испытывающих сильные боли, одержимых демонами, больных эпилепсией, парализованных, и Он их исцелял. 25За Ним следовали большие толпы людей из Галилеи, области Десяти городов, Иерусалима, Иудеи и из-за реки Иордан.